Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci Sake Tura Sojoji Cikin Gaggawa Zuwa Borno Da Yobe
Published: 13th, May 2025 GMT
Majalisar dattawa a ranar Talata ta yi kira ga rundunar sojin Nijeriya da ta gaggauta tura jami’anta da sabbin kayan yaki na zamani zuwa jihohin Borno da Yobe sakamakon sabon hare-haren da mayakan Boko Haram suka kai a yankin. An yi wannan kiran ne biyo bayan sabbin hare-haren ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, ciki har da kashe sojoji sama da 10 a garin Marte da ke karamar hukumar Monguno ta jihar Borno, a ranar Litinin, 12 ga watan Mayu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
Sojoji sun kashe ’yan ta’addan Boko Haram 9 tare da kwato kudi fansa kimanin Naira miliyan 5 a yankunan Magumeri da Gajiram a jihar Borno.
Kakakin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK), Laftanar Kanar Sani Uba , ya ce sojojin da suke sintiri a yankunan ne suka hallakan mayakan bayan sahihan bayanan sirri kan zirga-zirgar ’yan ta’addan a kusa da Goni Dunari a Karamar Hukumar Magumeri.
Sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, 11 ga Oktoba, 2025 ta ce, “Dakarun mu sun yi gaggawar daukar matakin dakile barazanar bayan da suka ga yadda ’yan ta’addan suka kona gidaje tare da tsoratar da mutanen yankin.”
Ya bayyana cewa sojoji sun yi artabu da ’yan ta’addan ne bayan sun shafe sa’o’i hudu suna bibiyar su, inda suka kashe mayaka biyar tare da tilasta wa sauran tserewa.
Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoniKayayyakin da aka kwato sun haxa da bindiga kirar AK-47, alburusai, wuqa, da wayar hannu.
Uba ya qara da cewa “Babu asarar rayuka ko asarar kayan aiki da sojojin mu suka yi.”
A wani samamen kuma a hanyar Gajiram Bolori – Mile 40 – Gajiganna, sojoji sun yi arangama da mayakan Boko Haram a kusa da kauyen Zundur, inda suka kashe ’yan ta’adda hudu tare da kubutar da wasu mutane biyu da aka yi garkuwa da su daga Guzamala.
Kayayyakin da aka kwato sun hada da wata mota, sabbin wayoyin hannu guda biyu, man fetur lita 30, da tsabar kudi da suka kai Naira miliyan 4.35.
Binciken farko ya nuna cewa ’yan ta’addan sun bukaci naira miliyan 2 da wayoyi biyu a matsayin kudin fansa ga dan uwan wadanda suka kama kafin sojojin su kai dauki.
Laftanar Kanar Uba ya tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka matsin lamba kan ’yan ta’addan tare da hana su sakat.