Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai
Published: 30th, January 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewar akwai wasu shafaffu da mai da ake biya maƙudan kuɗaɗe domin kare Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.
Ya bayyana haka ne, yayin mayar wa Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Siyasar, Daniel Bwala, martani kan sukar da ya masa game da APC.
An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a Sweden Mahaifi ya harbe ’yarsa har lahira saboda wallafa bidiyo a TiktokEl-Rufai ya yi wannan magana ne a wani taro da aka shirya kan ƙarfafa dimokuraɗiyya a Najeriya.
Tsohon gwamnan ya soki jam’iyyar APC saboda rashin kwatanta dimokuraɗiyya, inda ya ce bai gane inda jam’iyyar ta dosa a yanzu ba.
A yayin martaninsa ga El-Rufai, Bwala ya tambayi ko El-Rufai zai ci gaba da yin irin waɗannan kalamai idan yana cikin gwamnati.
Bwala ya ce: “Ɗan uwana, idan kana cikinagwamnati da majalisar zartarwa, shin za ka riƙa irin waɗannan kalamai? Tarihi yana cike da misalai.
“Gwamnatin da ka taka rawa aka kafa, yanzu ita kake son saukewa. Haba Mallam, a ji tsoron Allah mana.”
El-Rufai ya mayar da martani, inda ya ce: “Na yi minista shekaru 22 da suka wuce kuma Asiwaju ya fahimci cewa bana sha’awar kowane muƙami a cikin gwamnatinsa.”
Ya ƙara da cewa, “Idan na zauna a cikin gwamnatin Tinubu, zan ci gaba yin abin da nake ganin ba daidai ba ne.”
El-Rufai ya kuma soki wasu daga cikin mutanen da ya ke ganin ’yan siyasa ne da ake biya don kare gwamnatin Tinubu.
Ya ce, “Wannan wasa ne na siyasa da ake biyan wasu kuɗaɗe masu yawa don suke shiga shafukan sada zumunta don kare duk abin da gwamnatin Asiwaju.”
Ya kammala da cewa, “Ka more muƙamin mai bayar da shawara na musamman, ɗan uwana, amma ka tuna cewa biyayya ga Allah da ƙasa yana da muhimmanci sama da kowane mutum ko hukuma.”
Majalisar Dattawa ga ƙi amincewa El-Rufai ya zama minista a 2023, saboda ƙarar da wasu abokan hamayyarsa suka shigar a kansa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Bwala gwamnatin tinubu Siyasa tsohon gwamna El Rufai ya
এছাড়াও পড়ুন:
Kungiyar Amnesty International Ta Kafa Hujja Kan Ta’asar’Yan Sahayoniyya A Gaza
Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta bayyana cewa: Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila’ tana aiwatar da kisan kiyashi kan Falasdinawa ana gani kai tsaye a tauraron dan Adam
Kungiyar kare hakkin bil adama ta Amnesty International a yau Talata ta yi Allah wadai da shirun da duniya ta yi game da yadda gwamnatin yahudawan sahayoniyya ‘yan mamaya take aiwatar da kisan kiyashi a zirin Gaza, kai tsaye duniya na gani ta hanyar tauraron dan Adama.
A yayin gabatar da rahoton shekara-shekara na kungiyar ta Amnesty kan kare hakkin bil’adama a duniya Agnes Callamard, sakatariyar kungiyar kare hakkin bil’adama ta Amnesty International, ta ce tun ranar 7 ga watan Oktoban shekara ta 2023, duniya ke kallon yadda ake aiwatar da kisan kare dangi kai tsaye a tauraron dan Adam a Zirin Gaza.
Ta kara da cewa, “Sun ga kasashe kamar babu abin da zasu iya saboda da rauni” tare da nuna cewa “gwamnatin mamayar Isra’ila na kashe dubban Falasdinawa maza da mata, ta hanyar kisan kiyashi kan dukkanin iyalai da suka hada da kananan yara, da lalata gidaje, rusa cibiyoyin tsare rayuka, rusa asibitoci da cibiyoyin ilimi.