Aminiya:
2025-11-03@14:02:19 GMT

Ana biyan wasu kuɗi don kare gwamnatin Tinubu — El-Rufai

Published: 30th, January 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewar akwai wasu shafaffu da mai da ake biya maƙudan kuɗaɗe domin kare Gwamnatin Shugaba Bola Tinubu.

Ya bayyana haka ne, yayin mayar wa Mai Bai Wa Shugaban Ƙasa kan Harkokin Siyasar, Daniel Bwala, martani kan sukar da ya masa game da APC.

An kashe mutumin da ya ƙone Al-Ƙur’ani a Sweden Mahaifi ya harbe ’yarsa har lahira saboda wallafa bidiyo a Tiktok

El-Rufai ya yi wannan magana ne a wani taro da aka shirya kan ƙarfafa dimokuraɗiyya a Najeriya.

Tsohon gwamnan ya soki jam’iyyar APC saboda rashin kwatanta dimokuraɗiyya, inda ya ce bai gane inda jam’iyyar ta dosa a yanzu ba.

A yayin martaninsa ga El-Rufai, Bwala ya tambayi ko El-Rufai zai ci gaba da yin irin waɗannan kalamai idan yana cikin gwamnati.

Bwala ya ce: “Ɗan uwana, idan kana cikinagwamnati da majalisar zartarwa, shin za ka riƙa irin waɗannan kalamai? Tarihi yana cike da misalai.

“Gwamnatin da ka taka rawa aka kafa, yanzu ita kake son saukewa. Haba Mallam, a ji tsoron Allah mana.”

El-Rufai ya mayar da martani, inda ya ce: “Na yi minista shekaru 22 da suka wuce kuma Asiwaju ya fahimci cewa bana sha’awar kowane muƙami a cikin gwamnatinsa.”

Ya ƙara da cewa, “Idan na zauna a cikin gwamnatin Tinubu, zan ci gaba yin abin da nake ganin ba daidai ba ne.”

El-Rufai ya kuma soki wasu daga cikin mutanen da ya ke ganin ’yan siyasa ne da ake biya don kare gwamnatin Tinubu.

Ya ce, “Wannan wasa ne na siyasa da ake biyan wasu kuɗaɗe masu yawa don suke shiga shafukan sada zumunta don kare duk abin da gwamnatin Asiwaju.”

Ya kammala da cewa, “Ka more muƙamin mai bayar da shawara na musamman, ɗan uwana, amma ka tuna cewa biyayya ga Allah da ƙasa yana da muhimmanci sama da kowane mutum ko hukuma.”

Majalisar Dattawa ga ƙi amincewa El-Rufai ya zama minista a 2023, saboda ƙarar da wasu abokan hamayyarsa suka shigar a kansa.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Bwala gwamnatin tinubu Siyasa tsohon gwamna El Rufai ya

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Ƴansanda Sun Kama  Wani Mai Wasa Da Bindiga AK-47 A Cikin Wani Bidiyo A Adamawa October 31, 2025 Manyan Labarai Kifewar Kwalekwale: Gwamnan Gombe Ya Jajanta Wa Al’ummar Nafada Kan Mutuwar Matasa Biyar October 31, 2025 Manyan Labarai NPA Da Ƙungiyar Injiniyoyi Ta Yi Haɗaka Don Bunƙasa Tashoshin Jiragen Ruwa October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • El-Zakzaki: Yakin Sudan Yana Kare Maslahar Kasashen Yamma ne Kawai
  • Ƙasashen Da Ba Su Yanke Hukuncin Kisa A Duniya Ba
  • Muna shirin kai farmaki a Nijeriya — Ma’aikatar Yaƙin Amurka
  • Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka
  • Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala
  • Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini ba — Tinubu
  • Zargin Kisan Kiristoci: Najeriya ba ta yadda da cin zarafin addini — Tinubu
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Zaben 2027 Zai Kasance Ne Tsakanin Mulkin Tinubu Da Zabin Ƴan Nijeriya —Atiku Abubakar
  • Gwamnatin Tarayya Da Stellar Steel, Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Habaka Karafan Cikin Gida