Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Published: 10th, May 2025 GMT
12.Malaman makaranta suna nuna yadda muhimmnci ilimi yake.
Malaman makaranta suna zama abin yin koyi musamman ma saboda lamarin ilimin da al’umma suke karuwa da shi daga gare su.Yada suka maida hankalinsu kan koyon darussan da za su koyar, hakan ya sa daliban abin ya basu sha’awa har abin ya burge su suka fara gane karfi da darajar ilimi, a rayuwa ta yau da kullum.
13.Malaman makaranta suna karkakawa kan yadda al’umma za su bada gudunmawar ci gaban wuraren da suke
Malaman makaranta suna bada muhimmiyar gudunmawa wajen koyar da yadda su dalibai za su gane cewa suma fa akwai ayyukan da za su yiwa al’ummar domin ci gabansu.In kana koya muhimmancin yi wa al’umma ayyuka, halaye masu kyau, yadda za su kasance cikin kowane aiki na al’umma. Malaman makaranta sune wadanda za su iya daukar nauyin aiwatar da hakan ga ‘yan kasa wadanda suke da sha’awar yin hakan.
Yadda Malamin makaranta zai cimma wannan burin:
Koya darussan da suka shafi gida, kasa, da kuma duniya gaba daya.
Ka ba dalibai kwarin gwiwa na kasancewa cikin ayyukan da suka shafi al’umma, da kuma Kamfen da ya shafe su.
Koya masu muhimmacin jefa kuri’a,aikin sa kai,da kuma da kuma sauran ayyuka masu inganta rayuwar al’umma.
14.Malaman makaranta suna samar da suka kamata ga ci gaban karuwar basira abubuwan ci gaba na al’umma
Malaman makaranta suna samar da wani yanayi inda dalibai za su samu damar koyon sabbin dabaru, su yi tunanin da zai samar da wani sabon abu,dauki wani matakin da ana iya samun matsala da kwakwalwa amma idan aka samu nasara akwai karuwa.Irin wannan bada kwarin gwiwa yana bunkasa kowane dalibi ta yadda kirkirar wani abu da sauki,tare da samar da tunanin da zai bunkasa ci gaban al’umma.
Hanyoyin da Malaman makaranta za su bunkasa iya kirkirar abubuwa:
Samar da wasu ayyuka wadanda za su ba dalibai samun damar yadda za su bayyana abubuwan ta hanyar bada shawarwari.
Ba dalibai kwarin gwiwa inda za su musayar ra’ayi, yin gwaji,da kuma gabatar da shawarwarinsu.
Bada dama yadda za a shigar da yadda za ayi maganin wata matsala da ke nasaba da kirkira a kowane darussan koyarwa na kowace rana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Matashi ya yi wa maraya ɗan shekara 10 kisan gilla a Zariya
Ana zargin wani ɗan shekaru 18 da kashe wani maraya ɗan shekara 10 a yankin Ƙaramar Hukumar Zariya ta Jihar Kaduna.
’Yan sanda sun kama matashin ne kan zargin sa da yi wa ɗan yaron, wanda ɗan baffansa ne, ɗaurin goro tare da azabtar da shi saboda yaron ya ƙi amincewa ya yi lalata da shi.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis da ta gabata a unguwar Iyan Juma da ke Karamar Hukumar Zariya.
Mahaifiyar marigayin mai suna Asama’u Mohammed ta shaida wa Aminiya cewa, “Na dawo wajen aikatau kamar yadda na saba yi don na samo abin da zan ba su su ci tare da ’yan uwansa, sai ga yayansa ya shigo a guje ya ce ga Idris can a kwance cikin jini kuma fuskarsa a kumbure, wai sun yi faɗa da wani duk an ji mishi ciwo, nan da nan na yafa hijabi ni da ɗan uwar gidana muka tafi inda yake.”
Mahaifiyar Babban Editan jaridar Daily Trust ta rasu Koriya ta Arewa za ta taimaka da gyara tashoshin nukiliyan Iran —MasaniAminiya ta garzaya Babban Ofishin ’yan sanda da ke Ƙofar Fada cikin birnin Zariya domin ji daga bakin babban jima’i, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin kuma ya shaida wa wakilinmu, cewa sun tattara bayanai yadda lamarin ya kasance kuma sun tura zuwa babban ofishinsu da ke Kaduna
Kakakin rundunar ’yan sandan jihar Kaduna DSP Mansur Hassan ya tabbatar wa wakilin namu da faruwar lamarin, da kama wanda da ake zargi.
Ya ƙara da cewa bayan sun kammala bincike za su tora zuwa kuto.