Dalilan Da Ke Nuna Malaman Makaranta Na Da Muhimmaci (5)
Published: 10th, May 2025 GMT
12.Malaman makaranta suna nuna yadda muhimmnci ilimi yake.
Malaman makaranta suna zama abin yin koyi musamman ma saboda lamarin ilimin da al’umma suke karuwa da shi daga gare su.Yada suka maida hankalinsu kan koyon darussan da za su koyar, hakan ya sa daliban abin ya basu sha’awa har abin ya burge su suka fara gane karfi da darajar ilimi, a rayuwa ta yau da kullum.
13.Malaman makaranta suna karkakawa kan yadda al’umma za su bada gudunmawar ci gaban wuraren da suke
Malaman makaranta suna bada muhimmiyar gudunmawa wajen koyar da yadda su dalibai za su gane cewa suma fa akwai ayyukan da za su yiwa al’ummar domin ci gabansu.In kana koya muhimmancin yi wa al’umma ayyuka, halaye masu kyau, yadda za su kasance cikin kowane aiki na al’umma. Malaman makaranta sune wadanda za su iya daukar nauyin aiwatar da hakan ga ‘yan kasa wadanda suke da sha’awar yin hakan.
Yadda Malamin makaranta zai cimma wannan burin:
Koya darussan da suka shafi gida, kasa, da kuma duniya gaba daya.
Ka ba dalibai kwarin gwiwa na kasancewa cikin ayyukan da suka shafi al’umma, da kuma Kamfen da ya shafe su.
Koya masu muhimmacin jefa kuri’a,aikin sa kai,da kuma da kuma sauran ayyuka masu inganta rayuwar al’umma.
14.Malaman makaranta suna samar da suka kamata ga ci gaban karuwar basira abubuwan ci gaba na al’umma
Malaman makaranta suna samar da wani yanayi inda dalibai za su samu damar koyon sabbin dabaru, su yi tunanin da zai samar da wani sabon abu,dauki wani matakin da ana iya samun matsala da kwakwalwa amma idan aka samu nasara akwai karuwa.Irin wannan bada kwarin gwiwa yana bunkasa kowane dalibi ta yadda kirkirar wani abu da sauki,tare da samar da tunanin da zai bunkasa ci gaban al’umma.
Hanyoyin da Malaman makaranta za su bunkasa iya kirkirar abubuwa:
Samar da wasu ayyuka wadanda za su ba dalibai samun damar yadda za su bayyana abubuwan ta hanyar bada shawarwari.
Ba dalibai kwarin gwiwa inda za su musayar ra’ayi, yin gwaji,da kuma gabatar da shawarwarinsu.
Bada dama yadda za a shigar da yadda za ayi maganin wata matsala da ke nasaba da kirkira a kowane darussan koyarwa na kowace rana.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato
’Yan sanda sun gano harsasai guda 500 a wata maɓoyar masu aikata laifuka da ke kusa da hanyar Bauchi a Ƙaramar Hukumar Jos ta Arewa a Jihar Filato.
Kwamishinan ’yan sandan jihar, Emmanuel Adesina, ya ce an gano harsasan ne ta hanyar rahotannin sirri, inda ya bayyana hakan a matsayin babbar nasara a yaƙi da aikata laifuka a jihar.
Kwamishinan ya ci gaba da bayanin cewa an gano harsasan ne bayan wani kisan kai da ya faru a yankin, inda aka kashe wani da ba a gane ko wanene ba.
“Bayan samun rahoton faruwar lamarin, nan take muka fara gudanar da bincike domin gano yanayin da ya kai ga mutuwar wanda aka kashe.
An kwantar da kishiyoyi a asibiti bayan sun sha ‘Kayan Mata’ ’Yan sanda sun bankaɗo masana’antar man gyaɗa na bogi a Kaduna“A yayin gudanar da wannan binciken ne aka samu nasarar gano waɗannan harsasan. Ina so in ba ku tabbacin cewa muna ci gaba da ƙoƙarin ganowa tare da kama waɗanda suka aikata wannan laifin tare da ƙwato makamansu.”
Ya yi kira ga al’ummar jihar da su ba su duk wani bayani da zai iya taimakawa wajen kama su.