Shugaban kasar Amurka Donal Trump ya bayyana cewa zai dagewa kasar Siriya dukkan takunkuman tattalin arzikin da ta dora mata, kuma zai gana da shugaban gwamnatin riko na kasar Ahmad Sharaa wanda aka fi sani da Julani.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto shugaban yana fadar haka a wata tattaunawa da jami’an gwamnatin kasar Saudiya a birnin Riyad na kasar Saudiya, inda ya fara ziyarar aiki a can tun jiya Talata.

Shugaban ya kara da cewa: A yanzu lokaci yayi da mutanen kasar Siriya zasu huta, don zamu dauke dukkan takunkuman da muka dorawa kasar Siriya. Saboda zata samar da huldar Jakadanci da HKI kuma babu wata cuta da zata sami kasar daga Siriya.

Wannan yana zuwa ne bayan da shugaban HKS kuma shugaban gwamnatin riko na kasar ta Siriya bayan kifar da gwamnatin Bashar Al-Asad ya fito fili ya bayyana cewa gwamnatinsa zata samar da huldar Jakadanci da HKI.

Abu Muhammad Al-jula ne, ya kuma gabatar da wani shiri na gina Hasumiyyar Trump a birnin Damascus babban birnin Kasar Siriya don yabawa shugaban.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Siriya

এছাড়াও পড়ুন:

Shugaban Amurka Na Kan Hanyarsa Ta Zuwa Kasar Saudiya

Shugaban kasar Amurka Donal Trump yana kan hanyarsa ta zuwa kasar Saudia a wani tafiya ta musamman don samar da kuded da kuma harkokin kasuwa ga Amurka a yankin Gabas ta tsakiya.

Trump  zai ziyarci wasu kasashen larabawa a yankin, wadanda suka hada da Qatar da HDL da kuma Turkiya inda ake saran zai tattauna dangane da yakin da ke faruwa a Ukraine tare da shugaban  kasar Turkiyya Rajab Tayyid Urdugan.

Shugaban yana zuwa yankin ne a dai-dali lokacinda HKI ta ci gaba da kissan kiayashi ga Falasdinawa a Gaza da kuma hana abinci shiga Gaza.

Shugaban ya sami labarin saken wani ba’amerike mai suna Edan Alezander wanda yake tsare a hannun kungiyar Hamas tun shekara ta 2023. Kungiyar Hamas ta sake shi ne don ganin HKI ta bude kofar Rafah don a shigo da kayakin abinci ga falasdinawa wadanda suke fama da yunwa. Tun kimani watanni biyu da suka gabata.

Shugaban yace yana saran kulla yarjeniyoyi na zuba jari a Amurka da kuma harkokin kasuwanci a wannan tafiyar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Isa Birnin Jakarta Na Kasar Indonesiya
  • Amurka ta kulla yarjejeniyar sayen makamai ta dala biliyan 142 da Saudiyya
  • Gwamnatin Netanyahu Tana Yi Wa Gwamnatin Trump Leken Asiri
  • Shugaban Kungiyar Hizbulla Ya Ce Cewa Kungiyarsa Ba Zata Taba Mika Kai Ga Bukatun HKI Ba
  • Shugaban Amurka Na Kan Hanyarsa Ta Zuwa Kasar Saudiya
  • Sabuwar Gwamnatin Siriya Zata Kulla Kyakkyawar Alaka Da Haramtacciyar Kasar Isra’ila
  • An Zabi Birnin Esfahan Na Kasar Iran A Matrsayin Cibiyar Yawon Bude Ido A Asia Na Shekara Ta 2025
  • Trump Ya Bukaci Ukraine Ta Amince Da Tayin Putin Na Bude Tattaunawa A Birnin Istambul