‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban APC A Ondo, Sun Nemi N100m
Published: 13th, May 2025 GMT
Kwamandan rundunar Amotekun a Jihar Ondo, Adetunji Adeleye, ya tabbatar da faruwar lamarin, kuma ya ce ana ƙoƙarin ceto Adepoyigi.
Kakakin rundunar ‘yansandan Jihar Ondo, Olushola Ayanlade, shi ma ya tabbatar da sace shugaban na APC, inda ya ce an sace shi a gonarsa da ke hanyar Ifon-Owo.
Ya ƙara da cewa DPO na Ifon tare da mafarauta, ‘yan sa-kai da sojoji sun fara bincike domin gano inda aka kai shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Hari Sacewa Yan bindiga
এছাড়াও পড়ুন:
Hajjin 2025: Rukunin Farko Na Alhazan Jihar Kwara Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
Rukunin farko na maniyyata dari biyar da sittin (560) daga jihar Kwara tare da jami’an hukumar aikin hajji ta kasa NAHCON su biyu, sun tashi daga Filin Jirgin Sama na na Babatunde Idiagbon da ke Ilori zuwa Saudiyya domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2025.
Yayin da yake jawabi ga maniyyatan kafin tafiyarsu, Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya bukace su da su kasance masu kamun kai da kuma wakiltar jihar da kasa Najeriya.
Gwamna AbdulRazaq, wanda mai ba shi shawara ta musamman, Alhaji Saadu Salaudeen, ya wakilta, ya yi kira ga dukkan maniyyata 2,174 daga jihar da su yi addu’a domin zaman lafiya da hadin kai a jihar da kuma kasa baki daya.
Gwamnan ya kuma gargadi maniyyatan da su nisanci duk wani hali da zai iya bata suna ko kimar jihar da kasar nan, tare da jaddada bukatar zaman lafiya da fahimta a tsakanin maniyyatan.
A jawabansu, Shugaban Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kwara, Farfesa Mashood Mahmood Jimba, da Amirul-Hajj na bana, Olupo na Ajase-Ipo, Oba Ismail Yahaya Alebiosu, sun shawarci maniyyatan da su kasance masu hali na gari a tsawon lokacin aikin hajji.
Shi ma a jawabinsa, Shugaban Hukumar Jin Dadin Maniyyatan Musulmi ta Jihar Kwara, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam, ya bayyana cewa za a yi sahu 4 wajen jigilar jimillar maniyyata dubu biyu da dari daya da saba’in da hudu (2,174) a matsayin wani bangare na shirye-shiryen aikin hajjin bana.
Maniyyatan sun tashi ne a jirgin Max Airline da karfe goma sha biyu da minti arba’in (12:40) na rana, zuwa kasa mai tsarki.
Ali Muhammad Rabi’u