HausaTv:
2025-05-12@23:51:35 GMT

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Na Tattaunawa Da Amurka

Published: 12th, May 2025 GMT

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Tattaunawar Iran da Amurka ba zata shafi matakin jan layi da Iran ta gindaya ba

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa da gaske kasarsa tana tattaunawa da Amurka, kuma tana neman cimma matsaya, amma batun neman yin watsi da cibiyoyin nukiliyarta wani zabi ne da ba za a taba amincewa da shi ba.

A cikin rashin tabbas da ke tattare da ci gaba da aiwatar da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, biyo bayan cin karo da maganganun da jami’an fadar mulkin Amurka ta White House suka yi, da kuma karuwar bukatar Amurka kan Iran; Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kawo karshen matsin lambar da ake yi mata; Yayin da shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Kasarsa da gaske take yi kan tattaunawar, kuma tana neman cimma matsaya, amma neman yin watsi da cibiyoyin nukiliya da fasahar nukiliyar, wani zabi ne da ba zata taba a amincewa da shi ba. Pezeshkian ya jaddada cewa Iran ba ta taba nema ba kuma ba za ta taba neman mallakar makamin nukiliya ba.

Shugaba Pezeshkian ya ce, “Za su iya tabbatar da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta neman mallakar makaman kare dangi, kuma ba zata taba amincewa da batun yin watsi da dukkan cibiyoyin nukiliya da binciken ilimi da take yi kafin fara tattaunawar ba, kuma tabbas manufarta ta tattaunawan ita ce neman cimma yarjejeniya.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Pezeshkian ya

এছাড়াও পড়ুন:

Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari

Ya kara da cewa bukatar kasa da kasa game da karfin ma’adinai na Kaduna yana karuwa, tare da masu saka hannun jari da yawa wadanda suke bincike kan yadda za su yi amfani da wadannan albarkatun da ba a taba amfani da su ba.

“Baya ga wannan, muna da ma’adanan karfe. Kamfanin ‘African Mines’ ya riga ya zo Kaduna don hakar wannan albarkatun, wanda ya nuna a fili cewa Kaduna tana da ma’adanan karfe da za a iya gudanar da kasuwancinsu,” in ji shi.

Bello ya jaddada cewa tsarin kamfanin yana nuna jajircewa don kokarin killace iyakokin ma’adinai da kuma habaka su.

Ya ce tun lokacin da aka kafa kamfanin, hukumar gudanarwaar kamfanin ta ba da fifiko ga ayyukan da ke sanya alhakin muhalli da zamantakewar al’umma a gaba a ayyukanta.

Haka kuma manajan daraktan ya kuma yaba wa Gwamna Uba Sani saboda goyon bayan da yake bayarwa ga bangaren hakar ma’adanai, yana mai cewa a karkashin jagorancin gwamnan, kamfanin ba wai kawai a shirye yake ba har ma yana da cikakkiyar kayan aiki don samar da sakamako mai kyau.

“Ana sa ran wannan kokari zai samar da ci gaba a hakar ma’adanai tare da bude hanyoyin arziki a bangaren ma’adanai, samar da dubban ayyuka, da kuma habaka ci gaban tattalin arziki ba kawai a Kaduna ba har ma a duk fadin Nijeriya,” in ji shi.

Ya kuma tabbatar wa masu saka hannun jari na cikin gida da na waje samar da yanayi mai aminci wanda ke karfafa kirkire-kirkire da ci gaba na dogon lokaci.

Bello ya kuma sanar da cewa kamfanin bunkasa ma’adanai na Kaduna a shirye yake ya yi maraba da masu saka hannun jari da ke da sha’awar yin amfani da albarkatun kasa na jihar.

Ya bayyana tashar sarrafa lithium ta Kangimi, wacce ke aiki a karfin tan 5,000 a kowace rana, a matsayin babban ci gaba a tafiyar hakar ma’adinai ta jihar.

“Bisa jajircewar kamfanin wajen samar da aminci da ci gaba mai dorewa, Kaduna za ta kasance a matsayin babban wurin saka hannun jari,” in ji shi.

Ya nuna godiya ga Gwamna Uba Sani, yana mai cewa, “Godiya ga kokarin da Gwamna Uba Sani ya yi, muna shaida canji mai ban mamaki a bangaren hakar ma’adanai wanda ke bude hanya don kyakkyawar makoma mai kyau.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Matsayin Kasarsa Na Rashin Sallama Hakkinta Na Makamashin Nukiliya
  • Iran Da Amurka Sun Fahinci Juna Sosai A Zagaye Na 4 A Tattaunawa A Mascat
  • Trump Ya Bukaci Ukraine Ta Amince Da Tayin Putin Na Bude Tattaunawa A Birnin Istambul
  • Kungiyar Hamas Ta Amince Ta Saki Fursinan Yaki Wanda Yake Da Jinsiyar Amurka Da HKI
  • Iran ta ce tattaunawa ta hudu da Amurka tana da wahala amma tana da amfani  
  • Putin ya ba da shawarar tattaunawa kai tsaye da Ukraine a Istanbul
  • Iran Ta Bayyana Damuwarsa Da Makaman Nukliyar HKI A Sanda Ake Takura Mata
  • Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah Wadai Da Kai Hari Kan Ofishin Jakadancin Kasarsa A Kasar Sweden