Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Na Tattaunawa Da Amurka
Published: 12th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Tattaunawar Iran da Amurka ba zata shafi matakin jan layi da Iran ta gindaya ba
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa da gaske kasarsa tana tattaunawa da Amurka, kuma tana neman cimma matsaya, amma batun neman yin watsi da cibiyoyin nukiliyarta wani zabi ne da ba za a taba amincewa da shi ba.
A cikin rashin tabbas da ke tattare da ci gaba da aiwatar da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, biyo bayan cin karo da maganganun da jami’an fadar mulkin Amurka ta White House suka yi, da kuma karuwar bukatar Amurka kan Iran; Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kawo karshen matsin lambar da ake yi mata; Yayin da shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Kasarsa da gaske take yi kan tattaunawar, kuma tana neman cimma matsaya, amma neman yin watsi da cibiyoyin nukiliya da fasahar nukiliyar, wani zabi ne da ba zata taba a amincewa da shi ba. Pezeshkian ya jaddada cewa Iran ba ta taba nema ba kuma ba za ta taba neman mallakar makamin nukiliya ba.
Shugaba Pezeshkian ya ce, “Za su iya tabbatar da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta neman mallakar makaman kare dangi, kuma ba zata taba amincewa da batun yin watsi da dukkan cibiyoyin nukiliya da binciken ilimi da take yi kafin fara tattaunawar ba, kuma tabbas manufarta ta tattaunawan ita ce neman cimma yarjejeniya.”
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Pezeshkian ya
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
Gwamnatin Nijeriya ta ce babu wata barazanar tsaro a babban birnin ƙasar, Abuja, inda ta yi kira ga mazauna birnin su ci gaba da gudanar da harkokinsu na yau da kullum cikin lumana.
Nijeriya ta musanta batun yiwuwar kai hari kan ’yan Amurka da suke zaune a kasar, sakamakon rikicin da ke faruwa a yankin Gabas ta Tsakiya.
Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha Trump ya soki Iran da Isra’ila kan saɓa wa yarjejeniyar tsagaita wutaGwamnatin ta bayyana haka ne a matsayin martani dangane da gargaɗin tsaro da Amurka ta aika zuwa ga ’yan ƙasarta da ke birnin Abuja.
A sanarwar da Ministan Watsa Labarai na Nijeriya, Mohammed Idris ya fitar, ya ce, “Gwamnatin Nijeriya ta samu labarin gargaɗin da Amurka ta aika wa ma’aikatan ofishin jakadancinta da ma ’yan ƙasarta da ke Abuja game da tsaro.
“Duk da Gwamnatin Nijeriya na girmama haƙƙin da ofisoshin jakadanci — ciki har da na Amurka — ke da shi na ba ’yan ƙasarta shawara ko gargaɗi game da matsalolin tsaro, yana da muhimmanci mu tabbatar da cewa babu wata barazanar tsaro da Nijeriya ke fuskanta, sannan mazauna birnin da masu ziyara babu wata barazana da suke fuskanta.”
Sanarwar ta ƙara da cewa babu dalilin wannan gargaɗi saboda akwai cikakken tsaro a Abuja, “domin jami’an tsaro suna aiki ba dare ba rana domin tabbatar da daƙile dukkan wata barazanar tsaro.”