HausaTv:
2025-08-11@14:20:28 GMT

Shugaban Kasar Iran Ya Bayyana Matsayin Kasarsa Na Tattaunawa Da Amurka

Published: 12th, May 2025 GMT

Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Tattaunawar Iran da Amurka ba zata shafi matakin jan layi da Iran ta gindaya ba

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa da gaske kasarsa tana tattaunawa da Amurka, kuma tana neman cimma matsaya, amma batun neman yin watsi da cibiyoyin nukiliyarta wani zabi ne da ba za a taba amincewa da shi ba.

A cikin rashin tabbas da ke tattare da ci gaba da aiwatar da tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, biyo bayan cin karo da maganganun da jami’an fadar mulkin Amurka ta White House suka yi, da kuma karuwar bukatar Amurka kan Iran; Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta kawo karshen matsin lambar da ake yi mata; Yayin da shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya jaddada cewa: Kasarsa da gaske take yi kan tattaunawar, kuma tana neman cimma matsaya, amma neman yin watsi da cibiyoyin nukiliya da fasahar nukiliyar, wani zabi ne da ba zata taba a amincewa da shi ba. Pezeshkian ya jaddada cewa Iran ba ta taba nema ba kuma ba za ta taba neman mallakar makamin nukiliya ba.

Shugaba Pezeshkian ya ce, “Za su iya tabbatar da cewa Jamhuriyar Musulunci ta Iran ba ta neman mallakar makaman kare dangi, kuma ba zata taba amincewa da batun yin watsi da dukkan cibiyoyin nukiliya da binciken ilimi da take yi kafin fara tattaunawar ba, kuma tabbas manufarta ta tattaunawan ita ce neman cimma yarjejeniya.”

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: Pezeshkian ya

এছাড়াও পড়ুন:

Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa

Garima wanda har ila yau shi ne, and Jakadan Gwandu ya yi nuni da cewa, cibiyoyin na CNG da gwamnatin taraya ta samar a jihohin Kano da Kaduna, za su taimaka wajen samar da Iskar Gas ɗin a Arewa ta tsakiya da kuma Arewa ta Gabas.

Kazalika ya ce, samar da cibiyar a jihar Sokoto wadda take kusa da Jamhuriyyar Nijar, hakan zai ƙara bunƙasa tattalin arzikin jihar

Garima ya sanar da cewa, Iskar Gas ɗin ta CNG tsafatattaciya ce kuma bata da wani tsada, inda kuma ta rage gurɓatar muhalli.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • UNICEF Da Gavi Sun Bada Na’urorin Samar Da Wutar Lantarki Ta Hasken Rana Ga Jihar Kano
  • Iran: Babu wani abu da aka yanke game da tattaunawa da Washington
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • Jami’in Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12
  • Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
  • Tehran Times: Mai Yiwuwa Iran da Amurka su koma Tattaunawa
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Iran: Amurka Ta Sha Kaye Daga ‘Yan Gwagwarmayar Kasar Yemen
  • Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza