Wani hari kan gidan yarin Al-Obeid yayi sanadiyyar mutuwa da jikkatan mutane da dama a kasar Sudan

Ministan al’adu da yada labarai, kuma kakakin gwamnatin Sudan, Khaled Al-Aiser, ya tabbatar da cewa: Mutane 20 ne suka mutu, yayin da wasu 50 na daban suka jikkata a wani harin da ‘yan ta’addar Daglo na  kungiyar Rapid Support Forces masu aikata laifuka suka kai hari kan gidan yarin Al-Obeid.

Al-Aiser ya bayyana cewa: Harin da aka kai ya hada da asibitin birnin, inda ya yi sanadin mutuwar mutane musamman majinyata masu yawa tare da raunata wasu kimanin 50, wadanda dukkansu fararen hula ne, yana mai cewa wannan yana daga cikin manyan laifukan yaki.

Ministan ya kara da cewa: “Abin da ya faru a gidan yarin Al Obeid, babban laifin yaki ne, wanda ya kara tabbatar da cewa: Dakarun Kkai daukin gaggawa na Rapid Support Forces da magoya bayansu ‘yan ta’adda ne da suke cin zarafin fararen hula a Sudan.”

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

IRGC Ya Kaddamar Da Sabon Sansanin Jiragen Yaki Na Karkashiun Kasa

Janar Hussain Salami babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci a nan Iran ya kaddamar da sabon sansanin jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa na karkashin kasa.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Janar Salami yana cewa, wadannan jiragen yakin da ake sarrafasu daga nesa, suna iya daukar hotunan jiragen yakin Amurka wadanda suka kasance sansanin jiragen saman yaki na kasar wadanda suke cikin tekuna, don amfani da hotunan saboda kai wa sansanin hare hare.

Salami yace gabatar da wannan sansanin gargadi ne ga mjakiya, sannan duk wata kasa a yankin wacce ta bar Amurka ta yi amfani da dandanin sojojinta da ke kasar don kaiwa kasar Iran hare0hare kasar ma ta zama filin daga.

Wannan kaddamarwan ta na zuwa ne bayan da kasashen Amurka da HKI suka yi barazanar farwa kasar don wargaza cibiyoyin Nukliyar kasar ta Iran. Sai daga bayan shugaba Trump yace ya fi son a cimma yarjeniya da Iran maimakon yaki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Boko Haram 5, Sun Kwato Makamai A Borno
  • An kama ɗan daba mai yin fashi a cikin shigar mata a Kano
  • Mahara sanye da kayan ’yan sanda sun kashe malami sun sace mata 3 a makaranta a Zamfara
  • Pakisatan Ta Kore Cewa Ta Keta Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki
  •   Iran Ta Yi Maraba Da Tsayar Da Wutar Yaki A Tsakanin Indiya Da Pakistan
  • Kaduna Ta Gano Ma’adanai 73, Yayin Da Take Neman Masu Zuba Jari
  • Jagora Ya Jaddada Wajabci Daukan Matakan Kalubalantar Zaluncin ‘Yan Sahayoniyya
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah Wadai Da Kai Hari Kan Ofishin Jakadancin Kasarsa A Kasar Sweden
  • IRGC Ya Kaddamar Da Sabon Sansanin Jiragen Yaki Na Karkashiun Kasa