Leadership News Hausa:
2025-05-10@12:42:13 GMT

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Published: 10th, May 2025 GMT

Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet

Bugu da kari, wasu kwararru a fannin aikin noma, su ma tuni suka gargadi manoman kan kaucewa yin shuka da wuri, inda suka shawarce su da su tabbatar da sun kiyaye da hasashen na hukumar ta NiMet, domin kaucewa tabka asara da kuma yin da-na-sani.

Lokacin Da Ya Fi Dacewa Manona Su Yi Shuka:

Wata kungiya mai bayar da agajin gaggawa, (Christian Aids) tare da hadaka da wasu abokan hudda, sun samar da wata taswira da ke kunshe da lokacin da ya fi dacewa manoman da ke jihohin kasar 36 ciki har da babban birnin tarayayyar Abuja, su yi shuka.

Taswirar wadda ta kasance mai saukin amfanai, sun tsara matakan da suka kamata manoman su bi, na kiyaye lokacin yin shuka, mussamman domin manoman su kauce wa fadawa cikin matsalar irin yadda suka tsinci kansu a ciki a kakar noman shekarar 2024.

Idan za a iya tunawa, hukumar ta NiMet, a wasu bayanai da ta wallafa na farko da suka kuma karade shafukan sada zumunta na zamani a 2025, ta sanar da manoman kasar, ranakun da ya kamata su fara yin shuka da kuma Irin da ya kamata su shuka.

Kazalika, hukumar ta kuma shawarci manoman da su gujewa yin shuka da wuri, duba da bayanan sauyin yanayi da hukumar ta yi hasashen za a iya samu a kasar.

Idan za a iya tunawa, a kakar noma ta shekarar 2024, wasu manoman kasar da dama da suka yi shuka da wuri, sun tabka mummunar asara.

Wani malamain gona mai suna Jacob Auta, ya shawarci manoman kasar cewa; kada su yi saurin yin shuka, inda ya kara da cewa; duba da yadda Irin noma ya yi tsada, ya zama wajibi manoman su sanya ido kafin su fara yin shuka.

Ya yi nuni da cewa, wasu daga cikin Irin noman, ba sa iya jurewa yanayi kamar na zafi, idan an shuka su.

Jacob ya kara da cewa, idan har manoman sun yi shuka kuma ya kasance an kai sama da mako daya ba a samu ruwan sama ba, za su iya tafka asara.

“Haka nan, batun yake a kan sauran amfanin gona, sai dai kawai idan manomi, yana da kayan ban ruwan da zai iya rika yi wa gonarsa ban ruwa,”  in ji Jacob.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2
  • Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha
  • Hamas ta yi tir da Isra’ila kan rufe makarantun MDD  
  • JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025
  • Hukumar Raya Arewa Maso Yamma Ta Soke Shirin Tallafin Karatun Ƙasashen Waje
  • Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Gamsu da Gudanar da Aikin Tantance ‘Yan Fansho
  • Falasdinawa Sun Yi Shahada A Hare-Haren Da Sojojin Isra’il Suka Kai Gidan Cin Abinci Da Kasuwa A Gaza
  • Ma’aikatar Yaɗa Labarai Ta Fara Bitar Ayyuka Na Tsakiyar Wa’adi