HausaTv:
2025-05-12@03:48:58 GMT

Putin  Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro

Published: 11th, May 2025 GMT

Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya karbi bakuncin shugabannin kasashen Afirka da su ka hada na Zimbabwe da na Burkina Fasa, inda su ka tattaunawa hanyoyin karfafa alaka a tsakanin kasashen nasu.

Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da na Burkina Faso Ibrahim Taraore sun isa birnin Moscow domin halartar bikin cika shekaru 80 da samun nasara akan ‘yan Nazi na Jamus a lokacin yakin duniya na 2.

Bugu da kari shugaban kasar ta Rasha ya kuma gana da shugaban gwamnatin kwarya-karyar Falasdinawa Mahmmud Abbas Abu Mazin,inda su ka yi musayar ra’ayi akan yadda za a kawo karshen kisan kiyashin da HKI take yi wa al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Muna bayan Tinubu a Zaɓen 2027 — Patience Jonathan

Uwargidan tsohon Shugaban Najeriya Dame Patience Jonathan, ta bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu za ta marawa baya a Zaɓen 2027.

Patience ta nanata cewa ba ta da burin komawa fadar shugaban ƙasa, amma ta ce a shirye take ta taimakawa uwargidan shugaban ƙasa na yanzu, Sanata Oluremi Tinubu wajen yaƙin zaɓen 2027.

Muhawarar da ta ɓarke kan saya wa Sarkin Kano motocin naira miliyan 670 Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin

Aminiya ta ruwaito Patience na bayyana haka ne a lokacin da take kiran sunan manyan baƙi ciki har da ’yar shugaban ƙasar, Folashade Tinubu-Ojo a wajen taron da aka karrama ta a matsayin jagora ta gari, wanda kamfanin Accolade Dynamics Limited ya shirya ranar Asabar a Abuja.

Ta ce, “ita ya kamata in fara kira amma sai na bari zuwa ƙarshe wato ’yar shugaban ƙasarmu wanda muka aminta da shi wato Shugaba Bola Tinubu.

“Iyajola ina miki godiya bisa yadda kike ƙarfafa gwiwar mata. Muna tare da ke a wannan aikin kuma za mu mara miki baya.

“Ina da yawan magana, idan ba na son abu ana ganewa, amma idan ina tare da abu, zan iya mutuwa a kansa.

“Kowa da lokacinsa a mulki, kuma idan lokacin mutum ne, ina goya masa baya ne.”

Ta ƙara da cewa a lokacin da suke mulki, Uwargidan shugaban ƙasa Oluremi Tinubu ta goya mata baya.

“Ina da hankali, don haka dole ne in mayar da biki. Na faɗa mata cewa zan taya ta yaƙin zaɓe, ba zan juya mata baya ba. Ni ba na sha’awar komawa fadar shugaban.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Muna bayan Tinubu a Zaɓen 2027 — Patience Jonathan
  • Putin ya ba da shawarar tattaunawa kai tsaye da Ukraine a Istanbul
  • Abinda Ya Kamata Kusani Akan Wasan El Classico Na Yau
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Gana Da Tokwaransa Na Kasar Saudiya A Jiya Asabar
  • Shugaban Putin Ya Gana Da Sisi Don Karfafa Harkokin Kasuwanci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama
  • Xi Jinping Ya Gana Da Shugabannin Kasashe Daban-Daban A Moscow
  • Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow
  • Rasha Da China Sun Sha Alwashin Fuskantar Amurka