Putin Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro
Published: 11th, May 2025 GMT
Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya karbi bakuncin shugabannin kasashen Afirka da su ka hada na Zimbabwe da na Burkina Fasa, inda su ka tattaunawa hanyoyin karfafa alaka a tsakanin kasashen nasu.
Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da na Burkina Faso Ibrahim Taraore sun isa birnin Moscow domin halartar bikin cika shekaru 80 da samun nasara akan ‘yan Nazi na Jamus a lokacin yakin duniya na 2.
Bugu da kari shugaban kasar ta Rasha ya kuma gana da shugaban gwamnatin kwarya-karyar Falasdinawa Mahmmud Abbas Abu Mazin,inda su ka yi musayar ra’ayi akan yadda za a kawo karshen kisan kiyashin da HKI take yi wa al’ummar Falasdinu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ofishin Jakadancin Sin A Birtaniya Ya Soki Furucin Kasashen G7 Dangane Da Yankin HK
Kakakin ofishin jakadancin kasar Sin a kasar Birtaniya, ya soki kalaman da kasashen kungiyar G7 suka yi, dangane da ganin baiken ‘yan sandan yankin HK, bayan da a ranar 25 ga watan Yuli da ya shude, ‘yan sandan suka fitar da takardar sammacen cafke wasu mutane 19, masu yunkurin haifar da tashin-tashina a kasar Sin da suka tsere zuwa kasashen ketare.
A ranar Asabar ne ofishin jakadancin na kasar Sin a Birtaniya, ya yi tir da kalamai marasa ma’ana da kasashe membobin kungiyar G7, ciki har da Birtaniya suka furta kan batun, yana mai cewa, wasu kasashe tsiraru ciki har da Birtaniya, sun tsoma baki a batun dokar tabbatar da tsaro, wadda ‘yan sandan yankin musamman na HK ke aiwatarwa, wanda hakan katsalandan ne cikin harkokin cikin gidan kasar Sin, da ma dokokin yankin na HK. Don haka, kakakin ofishin ya ce, “Muna matukar bayyana adawa da hakan.”
Jami’in ya kara da cewa, “Muna matukar goyon bayan gwamnatin yankin musamman na HK, game da yadda take aiwatar da harkokin gwamnati bisa doka, kana muna goyon bayan ‘yan sandan yankin na HK, bisa rawar da suke takawa ta kare doka, bisa la’akari da tabbatattun dokoki.”
Ya ce, yadda hadakar wadannan kasashe suka tsoma baki cikin harkokin yankin HK, ya kara fayyace matsayarsu ta yin baki biyu, da munafurci a batutuwa masu nasaba da kare hakkin bil’adama da wanzar da doka. Kuma a cewar jami’in, ba abun da hakan zai haifar sai karfafa gwiwar gwamnatin HK, wajen jagorantar yankin bisa doka da hukunta masu laifi. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp