HausaTv:
2025-06-26@20:50:02 GMT

Putin  Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro

Published: 11th, May 2025 GMT

Shugaban kasar Rasha Vladmir Putin ya karbi bakuncin shugabannin kasashen Afirka da su ka hada na Zimbabwe da na Burkina Fasa, inda su ka tattaunawa hanyoyin karfafa alaka a tsakanin kasashen nasu.

Shugaban kasar Zimbabwe Emmerson Mnangagwa da na Burkina Faso Ibrahim Taraore sun isa birnin Moscow domin halartar bikin cika shekaru 80 da samun nasara akan ‘yan Nazi na Jamus a lokacin yakin duniya na 2.

Bugu da kari shugaban kasar ta Rasha ya kuma gana da shugaban gwamnatin kwarya-karyar Falasdinawa Mahmmud Abbas Abu Mazin,inda su ka yi musayar ra’ayi akan yadda za a kawo karshen kisan kiyashin da HKI take yi wa al’ummar Falasdinu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Yi

Ya ce: “Duk da cewa Gwamnatin Tarayya ta amince da haƙƙin ofisoshin jakadanci na ƙasashen waje, ciki har da na Amurka, na fitar da gargaɗin tafiye-tafiye ga ‘yan ƙasar su, yana da muhimmanci a faɗa a fili cewa Abuja tana da tsaro ga ‘yan ƙasa da mazauna da kuma baƙi baki ɗaya.”

 

Ya bayyana cewa hukumomin tsaro a Nijeriya suna aiki tuƙuru dare da rana don tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin jama’a, ya ƙara da cewa tsarin tsaro a Abuja yana aiki yadda ya kamata tare da nasarori masu yawa wajen gano duk wata barazana da kuma daƙile ta kafin ta faru.

 

Ministan ya ƙara da cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ba ya nuni da wata barazana kai-tsaye ga Abuja, illa ya dogara ne da al’amuran tsaro na duniya gaba ɗaya.

 

Ya ce: “Mun fahimci cewa gargaɗin da Amurka ta fitar ya ta’allaƙa ne da wasu abubuwan da ke faruwa a duniya gaba ɗaya, ba wai yana nuna wata barazana kai-tsaye ko ta gaggawa a cikin Babban Birnin Tarayya ba.

 

“Sai dai muna sake jaddadawa ga dukkan ofisoshin jakadanci, da masu zuba jari da abokan cigaba, da jama’a gaba ɗaya cewa babu wani dalilin fargaba.”

 

Ya kuma bayyana ƙudirin gwamnati wajen tabbatar da zaman lafiya da tsaro a birnin tarayya, yana mai cewa: “Gwamnatin Tarayya tana son sake jaddada ƙudirin ta na kare lafiyar duk mazauna ƙasar nan tare da ci gaba da tabbatar da martabar Abuja a matsayin ɗaya daga cikin manyan biranen da suka fi tsaro a duniya.”

 

Daga ƙarshe, ya buƙaci jama’a da su ci gaba da gudanar da harkokin su cikin kwanciyar hankali ba tare da tsoro ba, tare da yin taka-tsantsan da kuma bayar da rahoto kan duk wani abu da suka ga ya ɗaure masu kai ga jami’an tsaro mafi kusa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Afirka CDC Ta Yaba Da Hadin Gwiwa Kan Kiwon Lafiya Da Kasar Sin
  • Wannan Imanin Ne Ya Kai Likitocin Sin Nahiyar Afirka…
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • 2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau
  • DHQ Za Ta Tura Dakaru Na Musamman 800 Yankunan Da Ke Fama Da Rashin Tsaro – CDS
  • Yuan (RENMINBI) Na Ci Gaba Da Samun Farin Jini A Kasashen Afirka 
  • Mali ta ƙulla yarjejeniyar nukiliya da Rasha
  • Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
  • Shugaban CMG Ya Zanta Da Manyan Jami’an IOC
  • Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Yi