Za a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata zuwa ƙasashe 48 — FIFA
Published: 10th, May 2025 GMT
Hukumar Ƙwallon Kafa ta Duniya, FIFA, ta ce za ta faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata daga tawagogi 32 zuwa 48.
FIFA ta ce sabon tsarin zai fara aiki ne daga gasar 2031, wadda Amurka ce kawai ke neman ɗaukar nauyinta.
Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne — Kwankwaso HOTUNA: An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa SaudiyyaTuni dai FIFA ta faɗaɗa gasar cin Kofin Duniya ta Maza da za a yi nan gaba, zuwa wannan adadi.
FIFA ta ce ta ɗauki matakin ne saboda yadda gasar ke ci gaba da samun karɓuwa da farin jini tsakanin masoya ƙwallon ƙafa a duniya.
Masu suka sun zargi hukumar da fifita kuɗin da za ta samau fiye da la’akari da yawan wasanni da ’yan wasa za su fuskanta.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gasar Kofin Duniya ta Mata
এছাড়াও পড়ুন:
Yemen Ta Jaddada Cewa: Idan Amurka Ta Kai Mata Hari, Tabbas Yarjejeniyar Kawo Karshen Bude Wuta Tsakaninsu Zata Ruguje
Kasar Yemen ta jaddada cewa: Ba za su yi kasa a gwiwa ba wajen kai munanan hare-hare kan Amurka idan ta dawo da kai hari a kan kasarta
Sojojin Yemen sun sanar da aiwatar da hare-haren soji guda uku kan tashar jiragen sama na Ramon, wani muhimmin wuri ne na makiya yahudawan sahayoniyya, da a wurin akwai jirgin ruwan Amurka Truman mai dauke da dauke da jiragen saman yakin Amurka da kuma wasu kayayyakin yakinta.
Majiyar sojojin Yemen ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa, sojojin samanta sun gudanar da ayyukan soji guda biyu, na farko a kan filin jirgin saman “Ramon” na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke yankin Umm al-Rashrash a kudancin kasar Falasdinu da aka mamaye da jiragen sama masu saukar ungulu guda biyu, yayin da hari na biyun an kai harin ne kan wani muhimmin yanki a Jaffa da aka mamaye da wani jirgin sama maras matuki ciki, nau’in “Jaffa”, don tallafawa al’ummar Falastinu da ake zalunta.
A cikin wata sanarwa da kakakinta Birgediya Janar Yahya Sari’e ya fitar ya tabbatar da cewa: “A cikin yanayin tunkarar hare-haren da Amurka ke kaiwa kasar Yemen da kuma mayar da martani kan laifukan da suke yi kan al’ummar kasar, sojojin ruwa da na sama sun gudanar da wani farmaki na musamman na soji kan jirgin Amurka Truman da kuma wani adadi mai yawa na jiragen yakinta a tekun Bahar Maliya da wani makami mai linzami.”