Shugaban kungiyar Hizbullah ta kasar Lebanon Sheikh Na’im Kasin ya bayyana cewa kungiyarsa ba zata mika kai don takurawa da kuma matsin lambar da takewa gwamnatin kasar Lebanon don kawo karshen kungiyar ba.

Tashar talabijin ta Almanar ta nakalto Sheikh Qasim yana fadar haka a jiya litinin, a wanijawabinda ya yi ta tashar talabijin ta AL-Amnar na kungiyar don tunawa da babban kwamandar kungiyar Sayyed Mustafa Badreddin wanda yayi shahada shekaru 9 da suka gabata.

Sheikh Kasim ya kara da cewa kungiyar tana kan al-kawalinda na tsagaita budewa juna wuta duk tare da cewa HKI ta keta wannan yarjeniyar har sau 3000.

HKI dai ta amince da tsagaita budewa juna wuta bayan fafatawa da kungiyar Hizbullah na tsawon watanni 14, a ranar 27 ga watan Nuwamban shekarar da ta gabata a kudancin kasar Lebanon.

Sannan bayan ta rasa daruruwan sojojinta a kan iyakar kasar Lebanon wadanda suka dauki kimani watannin 2 suna kokarin shiga kasar ta Lebanon daga kudancin kasar tare da tankunan yakin Mirkava,  amma suka kasa yin hakan.

Sheikh Kasin ya bayyana cewa dukkan kokarin HKI da Amurka na shafe al-ummar Falasdinawa a Gaza ko a yankin yamma da kogin Jordan ba zai kai ga nasara ba. Duk da cewa manufarsu ta shafe kasar Falasdinu daga doron kasa ne fiye da shekaru 75 da suka gabata.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Lebanon

এছাড়াও পড়ুন:

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

 

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun yi wa ’yan bindiga luguden wuta a Neja
  • Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
  • Ziyarar Manzon Allah (SAW) A Madinah (3)
  • Amince Wa Al’umma Mallakar Makamai Zai Ƙara Tsananta Rashin Tsaro — IGP
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr
  • Nazarin CGTN: Neman Kashe Kaso 5 Na GDP Kan Tsaro Ya Nuna Rashin Dabara Na NATO
  • Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba
  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu