Dukan matar maƙwabci ya kai magidanci gidan yari a Kano
Published: 13th, May 2025 GMT
An gurfanar da wani mutum a gaban kotun Musulunci kan zargin yi wa matar maƙwabcinsa dukan kawo wuƙa a Jihar Kano.
Mai gabatar da ƙara ya shaida wa kotun da ke zama a unguwar Kurna Asabe cewa wanda ake zargin ya kuma ji wa matar auren munanan raunuka.
Ya yi wa matar wannan aika-aika ne bayan wata taƙaddama, inda ya ji mata munanan raunuka a fuska da wasu sassan jikinta.
Alƙalin kotun, Khadi Alhaji Jibrin Ɗanzaki, ya ba da umarnin tsare mutumin a gidan yari sannan ya ɗage sauraron shari’ar zuwa ranar 20 ga watan nan na Mayu.
Ya kashe abokinsa saboda hula a Kano Matashi ya kashe saurayin ƙanwarsa a Kano NAJERIYA A YAU: Matsalar lantarki: ’Yan Najeriya sun yi tir da biyan diyya ga ’yan Band Aউৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: matar maƙwabci
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Musanta Zargin Kamfanin Dillancin Labaran Reuters Dangane Da Aikawa Rasha Makamai
Jakadan JMI a MDD ya musanta zargin kamfanin dillancin labaran reuters dangane da rotohonsa na cewa JMI tana aika makamai masu linzami zuwa kasar Rasah don taimakawa kasar Rasha yakin da take fafatwa da kasar Ukraine fiye da shekaru 3 da suka gabata.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto
Ofishin jakadancin JMI dake birnin NewYork ya kara da cewa, abin mamaki da kamfanin dilancin laraban reuters, shi ne ba wannan ne karo na farko yake yada labaran karya a duniya wanda wai yake samu daga wasu wadanda basa son a bayyana sunansu.
Kafin haka dai JMI ta sha nanata cewa bata bayan wani bangare daga cikin bangarori biyu da suke fafatawa a kasar Ukraine.
Don haka bata taba taimakawa kasar Rasha da makamai don yakar kasar Ukraine ba, kuma bata taba taimaka kasar Ukraine.
Ofishin jakadancin ya bayyana cewa ra’ayinta da so samu ne ta zama mai shiga tsakani don warware rikicin kasar ta Ukraine.
Amma reuters ya ci gaba da bada labaran karya wadanda suke cewa tana shirin aikawa kasar Rasha damdamalin cilla makamai masulinzami wadanda Iran ta aikawa kasar Rasa a Bara, kamar yadda Amurka take zargin hakan.