Aminiya:
2025-06-25@05:18:02 GMT

Matsalar Tsaro: Zulum ya haramta sayar da man fetur a Bama

Published: 10th, May 2025 GMT

Gwamnan Borno, Babagana Umara Zulum ya haramta sayar da man fetur a Ƙaramar Hukumar Bama ta jihar, ciki har da garin Banki.

Gwamnan ya ce haramcin ya zo ne bayan tattaunawa da hukumomin tsaro a jihar, kuma an yi haka ne domin shawo kan matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

Gidauniya ta yi wa masu cutar gwaiwa dubu 12 tiyata kyauta a Katsina Za a faɗaɗa Gasar Kofin Duniya ta Mata zuwa ƙasashe 48 — FIFA

Wata sanarwa da mai taimaka wa gwamnan kan harkokin yaɗa labarai Dauda Iliya ya fitar, ya ce matakin wani ɓangare ne na tsare-tsaren da gwamnatin jihar ke yi na daƙile ayyukan ’yan ta-da ƙayar baya.

“Na bayar da umarnin haramta sayar da da man fetur a garuruwan Bama da Banki da kuma wasu sassa na karamar hukumar Bama nan take,” in ji gwamna Zulum.

Ya yi gargaɗin cewa duk wanda aka samu yana saɓa umarnin zai fuskanci hukunci mai tsanani.

“Babu wanda doka za ta ƙyale, sannan babu shafaffe da mai – za mu hukunta ko waye.

Gwamnan ya bai wa hukumomin tsaro damar kama duk wani gidan mai ko kuma mutum da ya take wannan umarnin.

Ya ƙara nanata zimmar da gwamnatinsa ke yi na dawo da zaman lafiya ma ɗorewa a jihar, inda ya yi kira ga al’ummar jihar da su ba da haɗin-kai a yaƙi da ƴan ta-da ƙayar baya da ake ci gaba da yi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Babagana Umara Zulum jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran

Trump ya ce hare-haren da Amurka ta kai kan cibiyoyin nukiliyar Iran guda uku, lallai zai kara rura wutar rikici a ci gaba da yakin da ake yi tsakanin Iran da Isra’ila.

 

Sai dai ministan harkokin wajen Iran Seyed Abbas Araghchi ya yi Allah wadai da harin da Amurka ta kai da cewa “abin takaici ne” sannan ya ce Iran ta tanadi “dukkan zabin kare ‘yancinta”, yana mai jaddada cewa Amurka za ta fuskanci “tsauraran sakamako”.

 

Araghchi ya kara da cewa, Amurka ta keta kundin tsarin mulkin Majalisar Dinkin Duniya a matsayinta na mamba a kwamitin sulhu na Majalisar Dinkin Duniya.

 

Bugu da kari, wani dan Majalisar kasar Iran, ya kara da cewa, “babu wani mummunan lahani a wuraren, kuma dama tun kafin harin, an riga an kwashe duk wasu abubuwa masu muhimmanci na tashoshin nukiliyar”.

 

Tun da farko, Tehran ta yi gargadin cewa za ta kai hari kan muradun Amurka a yankin Gabas ta Tsakiya domin daukar fansa kan duk wani hari da Amurka ta kai, kuma ya zuwa yanzu ta harba makamai masu linzami kan Isra’ila, inda aka ji karar fashewar wasu abubuwa a birnin Kudus.

 

A halin da ake ciki, kawunan ‘yan majalisar dokokin Amurka ya rabu dangane da shigar kasar, inda ‘yan jam’iyyar Republican suka yabawa Trump, yayin da ‘yan jam’iyyar Democrat suka yi gargadin cewa an jefa Amurka cikin wani yakin da ba nata ba.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sayar Da Makamai: Goyon Baya Ko Cin Riba?
  • Gwamnatin Nijeriya ta yi wa Amurka martani kan barazanar tsaro a Abuja
  • Sarkin Musulmi ya ba da umarnin fara duban watan Muharram
  • Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja Duk da Gargaɗin Da Ofishin Jakadancin Amurka Ya Yi
  • Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
  • Iran: Amurka ta ɗebo ruwan dafa kanta
  • Yakin Iran Da Isra’ila Ya Haifar Da Tashin Farashin Litar Man Fetur A Nijeriya
  • NAJERIYA A YAU: Matakan daƙile kisan matafiya a hanyoyin Najeriya
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Harin Amurka A Wurare 3 Na Nukiliyar Iran: Babu Wani Lahani A Harin Bama-baman – Iran