HausaTv:
2025-11-08@17:21:48 GMT

Amurka da Iran zasuyi tattaunawa ta hudu a ranar Lahadi

Published: 9th, May 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka ranar Lahadi.

Araghchi ya bayyana a yau Juma’a cewa Oman ce, zata kasance mai shiga tsakani, kuma ita ce ke tantance lokaci da wurin da za a yi tattaunawar.

Ya kara da cewa bisa ga dukkan alamu kasar Oman ta tattauna da bangaren waccen bangaren.

Babban mai shiga tsakani na Iran ya jaddada cewa tattaunawar Tehran da Washington tana ci gaba.

Iran da AMurka dai sun yi jerin tattaunawa har guda uku a Oman, sannan a Italiya sai kuma a Oman.

Dukkan bangarorin dai sun bayyana tattaunar da mai kyakyawan fata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya

Dakarun Sojin Amurka sun kammala shirye-shiryen kai hare-hare a Najeriya bayan umarnin da Shugaba Donald Trump, ya bai wa Ma’aikatar Tsaron ƙasar kan ɗaukar mataki game da zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi.

Jaridar The New York Times ta ruwaito cewa rundunar sojin Amurka da ke nahiyar Afirka (AFRICOM), ta gabatar da yadda hare-haren za su kasance.

An kama mutum 2 kan sukar shugaban karamar hukuma a Kano Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa

Daga cikin shirin akwai kai wa ’yan ta’adda hare-hare da jiragen yaƙi da amfani da jirage marasa matuƙa.

Sannan kuma akwai tsarin haɗin gwiwa da sojojin Najeriya ta hanyar musayar bayanan leƙen asiri da tallafin kayan aiki.

Sai dai jami’an Ma’aikatar Tsaron Amurka sun yi gargaɗin cewa irin waɗannan hare-haren ba lallai su magance matsalolin tsaro a Najeriya ba.

Sun ce dole sai an gudanar da yaƙi mai faɗi  kamar yadda aka yi a Iraƙi ko Afghanistan, sai dai sun ce hakan zai sa Amurka ta kashe maƙudan kuɗaɗe.

Trump, ya zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da tin sakaci wajen “kisan Kiristoci,” kuma ya bayar da umarnin dakatar da sayar wa Najeriya makamai.

Gwamnatin Najeriya ta ƙaryata zargin, inda ta danganta matsalar tsaro da wasu abubuwa kuma tana shafar kowane ɓangare na addini.

Mai bai wa Shugaba Tinubu shawara, Daniel Bwala, ya bayyana cewa Najeriya ba ta buƙatar sojojin Amurka su shiga ƙasarta, sai dai taimako a fannin leƙen asiri da kayan aiki, tare da buƙatar Amurka ta mutunta Najeriya.

Ƙasar China ta goyi bayan Najeriya, tare da gargaɗin Trump kan tsoma baki cikin harkokin da suka shafi ƙasa mai ’yanci.

Masana da tsofaffin Hafsoshin sojin Amurka sun yi gargaɗin cewa irin wannan farmaki zai iya ƙara ta’azzara matsalar tsaro.

Sun kuma bayyana cewa matsalar tsaro a Najeriya ta samo asali ne daga ’yan fashi, rikicin filaye, da ta’addanci da ke shafar Musulmai da Kiristoci baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Barau ya nemi Trump ya janye kalamansa, ya nemi afuwar Najeriya
  • Jamhuriyar Musulunci Ta Iran Ta Tabbatar Da Hannun Amurka Wajen Kaddamar Da Yaki Kanta
  • Kasar Sin Ta Musanta Zargin Da Wakilin Amurka Ya Yi Game Da Batun Sauyin Yanayi
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Mun fara tattaunawa da Amurka kan barazanar Trump – Gwamnatin Tarayya
  • Araqchi Ya Ce: Harin Amurka Kan Kasar Venezuela Ya Bayyana Karara Duniya Tana Gani
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Araghchi : Yakin kwanaki 12 ya bamu babban darasi
  • Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho
  • Ɓarayi Sun Shiga Ofishin Shugaban Karama Hukuma A Kano, Sun Tafka Sata