HausaTv:
2025-08-08@08:51:29 GMT

Amurka da Iran zasuyi tattaunawa ta hudu a ranar Lahadi

Published: 9th, May 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka ranar Lahadi.

Araghchi ya bayyana a yau Juma’a cewa Oman ce, zata kasance mai shiga tsakani, kuma ita ce ke tantance lokaci da wurin da za a yi tattaunawar.

Ya kara da cewa bisa ga dukkan alamu kasar Oman ta tattauna da bangaren waccen bangaren.

Babban mai shiga tsakani na Iran ya jaddada cewa tattaunawar Tehran da Washington tana ci gaba.

Iran da AMurka dai sun yi jerin tattaunawa har guda uku a Oman, sannan a Italiya sai kuma a Oman.

Dukkan bangarorin dai sun bayyana tattaunar da mai kyakyawan fata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano

Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana alhini kan rasuwar Sadiq Gentle, wani hadiminsa kan harkokin yada labarai a Ma’aikatar Tarihi da Al’adu ta jihar, wanda wasu da ake zargi ’yan daba suka kai masa harin da ya yi sanadiyyar mutuwarsa.

Wata sanarwa da Kakakin Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya wallafa a Facebook, ta bayyana Sadiq a matsayin jarumi, ƙwararre, kuma mai kishin kasa a fannin kafafen sada zumunta.

NAHCON ta ƙayyade N8.5m kafin alƙalami na kujerar Hajjin 2026 An kashe mutum huɗu da tayar da ƙauyuka 17 a Sakkwato

Gwamna Abba ya ce mutuwar Sadiq Gentle ta girgiza shi sosai, inda ya bayyana mamacin a matsayin mutum mai kamun kai, haƙuri, da sadaukarwa ga ci gaban Jihar Kano.

Gwamnan ya bayyana kisan da aka yi masa a matsayin keta haddin bil’adama da ba za a lamunta ba, lamarin da bayyana a matsayin ƙoƙarin da wasu bata-gari ke yi domin kawo cikas a zaman lafiya a jihar.

Ya umarci hukumomin tsaro da su gudanar da cikakken bincike, tare da tabbatar da cewa wadanda suka aikata wannan aika-aikar sun fuskanci hukunci kamar yadda doka ta tanada.

Ya kuma jaddada cewa gwamnatin jihar ba za ta lamunci irin wannan ta’asa ba, yana mai bayyana bukatar tsauraran matakan tsaro domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

Kazalika, Gwamnan ya mika ta’aziyya ga iyalan marigayin, abokan aikinsa, da daukacin jami’an Ma’aikatan Tarihi da Al’adu, yana mai tabbatar musu da cewa Gwamnatin Kano na tare da su a wannan lokaci na jimami da baƙin ciki.

Aminiya ta ruwaito cewa, a bayan nan ne wasu da ake zargi ’yan daba ne suka sassari hadimin gwamnan yayin wani farmaki da suka kai masa har gida da adduna.

Daga bisani an garzaya da Sadiq Gentle Asibitin Murtala da ke birnin Kano inda a nan ajali ya katse masa hanzari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Abba ya yi alhinin hadiminsa da ’yan daba suka kashe a Kano
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Kasar Masar Tana Ta Zama Mai Shiga Tsakanin Iran Da IAEA Da Kuma Amurka
  • Matasan Kauru Sun zargin Dan Majalisar Dokoki Barnabas Danmaigona da Rashin tabuka komai
  • Araqchi: Ba a kayyade wani lokacin shiga wata sabuwar tattaunawa da Amurka ba
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Taraba
  • An shafe wata 8 ana mulki babu mataimakin gwamna a Tataba
  • Kasar Sin Ta Bayyana Adawa Da Ziyarar Boris Johnson A Taiwan
  • IRGC: Bayan yakin Kwanaki 12 Yanayi Ya Sauya Zuwa Ga Amfani Ga Iran
  • Iran: Yakin Kwanaki 12 Ya Bayyana Inganci Da Karfin Yakin Yanar Gizo Na Kasar