HausaTv:
2025-09-24@11:15:59 GMT

Amurka da Iran zasuyi tattaunawa ta hudu a ranar Lahadi

Published: 9th, May 2025 GMT

Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce za a gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa tsakanin Iran da Amurka ranar Lahadi.

Araghchi ya bayyana a yau Juma’a cewa Oman ce, zata kasance mai shiga tsakani, kuma ita ce ke tantance lokaci da wurin da za a yi tattaunawar.

Ya kara da cewa bisa ga dukkan alamu kasar Oman ta tattauna da bangaren waccen bangaren.

Babban mai shiga tsakani na Iran ya jaddada cewa tattaunawar Tehran da Washington tana ci gaba.

Iran da AMurka dai sun yi jerin tattaunawa har guda uku a Oman, sannan a Italiya sai kuma a Oman.

Dukkan bangarorin dai sun bayyana tattaunar da mai kyakyawan fata.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya

 

Haddadiyar Kungiyoyin Makiyaya na kasashen Africa (CORET) ta bayyana cewa an samu karin yawan ɗalibai a makarantun makiyaya cikin watanni goma da aka fara shirin ciyar da ɗalibai.

 

Babban Sakataren CORET, Muhammed Bello Tukur, ya bayyana haka a taron kwana ɗaya da aka gudanar a Kaduna domin ƙara wa ma’aikata da abokan hulɗarsu ƙwarewa kan harkar ciyar da ɗalibai.

 

Taron ya mayar da hankali ne wajen duba nasarorin da aka samu cikin watanni goma tun lokacin da aka fara shirin a Ladduga, Karamar Hukumar Kachia ta Jihar Kaduna, da kuma Maigatari a Jihar Jigawa.

 

Babban Sakataren CORET, Muhammed Bello Tukur, ya bayyana cewa shirin ya shafi makarantun makiyaya kawai a jihohin Jigawa da Kaduna.

 

Ya ce ciyarwa na daga cikin manyan matsalolin da ke sa yara barin makarantu, don haka shirin ya ƙunshi amfani da al’ummomin yankuna wajen samar da abincin ɗalibai.

 

Ya ƙara da cewa an sayi kayan abinci daga cikin al’umma tare da haɗa su wajen tabbatar da ingancin abincin da ɗalibai ke ci. Bugu da ƙari, CORET ta samar da rijiyoyin burtsatse domin tabbatar da samun ruwa na sha da na yau da kullum.

 

Muhammed Bello Tukur ya yaba da irin goyon bayan da abokan hulɗa musamman ECOWAS, da kuma Gwamnatin Tarayya da Jihohi ke bayarwa wajen tabbatar da nasarar shirin.

 

A nasa jawabin, Ko’odinatan Shirin, Dakta Abdu Umar Ardo, ya bayyana cewa shirin ya zama nasara daga komai zuwa abu mai amfani tun da jihohin suka rungumi karatun ’ya’yan makiyaya.

 

Haka kuma, a kasidarsa, Bashir Abbo ya bayyana cewa bincike ya nuna akwai bukatar ƙwararrun malamai, farfaɗo da kwamitocin gudanar da makarantu da ƙarfafa ƙungiyoyin mata domin su riƙa taka rawar da ta dace.

 

Ya ce ɗaukar ƙarin malamai ƙwararru zai samar da sakamako mai kyau nan gaba.

 

Mahalarta taron sun fito ne daga Ladduga, yayin da wasu daga cikin mahalarta daga Karamar Hukumar Maigatari ta Jihar Jigawa suka halarci taron ta yanar gizo.

COV: Adamu Yusuf

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Araqchi; Tattaunawa Tsakanin Iran Da Norway Kan Kyakkyawar Alakar Da Ke Tsakaninsu
  • Kuri’ar Jin Ra’ayoyi Ta CGTN: Guguwar Amincewa Da Kasar Falasdinu Ta Nuna Yadda Amurka Da Isra’ila Suka Zama Saniyar Waren Da Ba A Taba Gani Ba
  • An yi wa sojoji ɗaurin rai da rai kan sayar wa ’yan ta’adda makamai a Borno
  • Lebanon: A yau Ne Aka Yi Jana’izar Shahidan Bitij Bail Wadanda HKI Ta Kai Ga Shahada A Ranar Lahadi
  • An ƙona al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • An ƙone al’aurar ’yar shekara 5 saboda fitsarin kwance a Bauchi
  • CORET Ta Yaba Da Nasarar Shirin Ciyarda Daliban Makarantun Makiyaya
  • Mata 400 sun amfana da kayan haihuwa a Gombe
  • Ministan Harkokin Wajen Sin Ya Bayyana Ra’ayin Kasar Kan Rikicin Falasdinu Da Isra’ila
  • Arakci Ya Kore Cewa Ya Zanta Da Steven Witkoff Na Amurka