Zaɓen 1993: IBB ya wallafa ba daidai ba a littafinsa — Sule Lamiɗo
Published: 14th, May 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Jigawa, Alhaji Sule Lamiɗo, ya musanta dalilin da tsohon shugaban mulkin sojin Nijeriya, Ibrahim Badamasi Babangida ya bayar a littafinsa dangane da soke zaɓen 1993.
Tsohon Ministan Harkokin Wajen Nijeriyar ya ce dalilin da IBB ya bayar cewa shi ne abin da ya sa ya rushe zaɓen 1993, “ba gaskiya” ba ne.
Janar Babangida a littafinsa mai suna “A Journey in Service” ya yi zargin cewa marigayi Janar Sani Abacha ne ke da alhakin rushe Zaɓen 12 ga watan Yunin 1993.
Trump ya janye takunkumin da Amurka ta ƙaƙaba wa Syria ‘Duk da hauhawar farashi tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka’Alhaji Sule Lamido ya faɗi hakan ne a littafin tarihinsa da ya rubuta mai suna “Being True to Myself” wanda aka ƙaddamar ranar Talata a Abuja.
Littafin mai shafi kimanin 500 ya mayar da hankali ne kan rayuwar marubucin tun daga ƙuruciya har zuwa gwagwarmayar siyasarsa daga jamhuriya ta biyu kawo yanzu.
Abin da Sule Lamiɗo ya faɗi
A wani babi mai taken “Matsayata kan rushe zaɓen 12 ga watan Yuni”, Sule Lamiɗo ya musanta dalilin da Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya bayar a littafinsa mai suna “A Journey in Service” a matsayin dalilin da ya sa ya rushe zaɓen watan Yunin 1993.
Bayan kammala ƙaddamar da littafi, marubucin ya yi wa BBC Hausa ƙarin bayani dangane da haƙiƙanin abin da yake nufi a babin kamar haka:
“A littafin Babangida ya ce Abiola shi ya ci zaɓe. A gaskiya shi ne ya ci zaɓen. Yanzu hujjar sokewa kuma wani abu ne daban.
“Amma ni abin da ya gaya min cewa shi ne dalilin da ya sa ya soke zaɓen shi ne saboda Abiola yana bin Najeriya bashin kuɗi naira miliyan 45,000 saboda haka idan ya ba shi wannan mulki to zai amfani da mulkin ya biya kansa kuma a lokacin nan ƙasar ba ta da wannan kuɗin da za ta biya shi, shi ya sa ya soke zaɓen.
“Kenan Abiola ya ci zaɓen amma an zalunce shi an hana shi sannan kuma ga kuɗi yana bi ba a biya shi ba.
“Idan ana so a yi adalci tunda mutumin nan ya mutu to kuɗin da yake bi naira miliyan 45,000 kamar yadda Babangida ya gaya min shi ya sa ya soke zaɓen nan to a ba wa iyalan Abiola, a biya su kuɗinsu. Shi kenan daga nan komai ya ƙare kenan.”
“Shi ya sa nake faɗa wa Tinubu cewa ya kamata maganar June 12 a ƙare ta. Saboda haka a biya wannan bashin na naira miliyan 45,000 ga iyalansa. Shi kenan magana ta ƙare.”
Abin da IBB ya faɗi a littafinsa
Janar Ibrahim Badamasi Babangida a littafin nasa mai suna “A Journey in Service” ya amince da cewa Cif Mashood Abiola ɗan takarar shugabancin ƙasa a jam’iyyar SDP, shi ne ya lashe zaɓen 1993 da ya rushe.
Duk da dai Janar ɗin ya ɗauki alhakin rushe zaɓen amma ya ɗora laifin a kan wasu manyan sojoji da ke aiki ƙarƙashin tsohon hafsan hafsoshin lokacin, Janar Sani Abacha cewa su ne suka rushe zaɓen ba tare da “izinina ba”.
To sai dai littafin na IBB ya janyo martani daga iyalai da ’yan uwan Janar Sani Abacha inda suka yi watsi da zargin.
“Yana da muhimmanci in bayyana cewa Janar Sani Abacha ba shi ba ne shugaban ƙasa ko kwamandan dakarun Nijeriya a lokacin da aka rushe zaɓen 12 ga Yuni ba.
“Kuma an yanke hukuncin soke zaɓen ne ƙarƙashin mulkin Janar Ibrahim Babangida wanda a lokacin shi ne shugaban mulkin soji kuma shi ke da ƙarfin iko a, hakazalika shi ke da alhakin dukkanin ayyukan da gwamnatinsa ta yi,” in ji wata sanarwa da iyalan Abacha suka fitar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Janar Sani Abacha Babangida ya rushe zaɓen soke zaɓen zaɓen 1993
এছাড়াও পড়ুন:
EFCC ta tsare tsohon Gwamnan Sakkwato Tambuwal kan zargin N189bn
Hukumar Yaki da Masu Karya Tattalin Arziki (EFCC) ta tsare tsohon Gwamnan Jihar Sakkwato, Sanata Aminu Waziri Tambuwal kan zargin almundahana.
A ranar Litinin ce EFCC ta tsare Tambuwal bayan da ya masa gayyatar da ta yi masa zuwa Ofishinta domin amsa tambayoyin kan badaƙalar Naira biliyan 189.
Majiyoyi sun shaida wa wakilinmu cewa Hukumar EFCC ta tsare tsohon Shugaban Majalisar Wakilan ne kan zargin cirar Naira biliyan 189.
Wata majiya a EFCC ta bayyana cewa, “Ba kama shi aka yi ba, zuwa ya yi domin amsa tambayoyi kan yadda ya yi amfani da Naira biliyan 189. Amma da ya kasa bayani sai aka tsare shi. Ina ganin shi ya sa mutane ke cewa an kama shi.
“Zai ci gaba da kasancewa a hannun har zuwa lokacin da zai iya bayar da cikakken bayani game da yadda ya kashe Naira biliyan 189 a lokacin da yake gwamna.”
Ta ci gaba da cewa, “Ka san abin da Naira biliyan 189 zai iya yi a Jihar Sakkwato kuwa? Yadda aka cire kuɗaɗen ya saɓa wa Ɗokar Haramta Safarar Kuɗaɗen Haram. Saboda haka dole sai ya yi cikakken bayani.”
Aminiya ta samu labarin cewa EFCC ta gayyaci tsohon Gwamnan Jihar Imo, Emeka Ihedioha domin amsa tambayoyi a cikin wannan makon.
Idan ba a manta ba, Ihedioha shi ne Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai a lokacin da Tambuwal yake matsayin shugaban majalisar.
Daga makusantan TambuwalA martaninsa kan wannan damvarwa, wani makusancin Tambuwal ya ya yi zargin cewa wannan “abin siyasa ce 100%”.
Ya yi zargin cewa abin ya samo asali ne tun wata huɗu da suka gabata inda wasu muƙarraban gwamnati suka buƙaci Tambuwal ya shiga “tafyar siyasar Tinubu.”
“Da ya tuntuɓe mum sai muka cika da mamakin yadda za a yi, da hankalinmu, mu shiga tafiyar gwamnatin da ta jefa mutane cikin wannan talauci da rashin tsaro da ke addabar musamman yankin Arewa,”in ji shi.
A cewarsa bayan rashin jin wata ƙwaƙƙwarar magana daga Tambuwal ne kimanin makonni uku da suka gabata, sai EFCC ta aiko masa da takardar gayyatar neman bayanai kan zamanin mulkinsa a Jihar Sakkwato.
“Sai muka nemi Hukumar ta fayyace haƙikanin abin da take neman bayanai a kai, amma ba ta yi ba. Don haka ya buƙaci su tuntuɓi gwamnatin jihar ko akwai wani abu da ba ta gamsu da shi ba game da gwamnoninsa.
“Amma duk da cewa ba su yi cikakken bayani ba, muna zargin yana da alaƙa da batun yadda aka gudanar da Kuɗaɗen Bankin Duniya da aka bayar a zamanin mulkinsa. Ta banki aka tura kuɗaɗen kuma Tambuwal ya samu sahalewar Bankin Duniya,” a cewarsa, amma ya nemi kasa a bayyana sunansa.
Ya ce tsohon Gwamnan ya samu gayyatar EFCC, wadda ya amsa a ranar Litinin kuma ya samu labarin cewa hukumar ta amince cewa zainiya samun beli.
A cewarsa, makusantan Tambuwal sun riga sun cika sharuɗan belin tsohon gwamnan, amma hukumar ta zaɓi ta ci gaba da ajiye shi zuwa ranar Talatar nan.
Shi ma wani makusancin Tambuwal ya alaƙanta tsarewar da siyasa, yana mai bayyana cewa, “Gwamnan Sakkwato na yanzu shi ne mataimakin gwamnan a lokacin mulkin Tambuwal kafin daga baya su raba gari.
“Shi (Gwamna Aliyu Sokoto) yana cikin waɗanda aka ɗauki mataki kan abubuwa da dama a jihar a zamanin Tambuwal. Saboda haka idan za a yi adalci ya kamata shi ma Gwamna EFCC ta ambaci sunansa a binciken, duk da cewa a yanzu yana da rigar kariya.
“Duk da cewa EFCC ta gayyaci wasu jami’an gwamnatin Tambuwal domin amsa tambayoyi. Amma abin da muke buƙata shi ne a yi adalci ba ɗaukar fansa ba. A daina tozarta mutane saboda neman biyan buƙatun siyasa,” in ji shi.
EFCC ta gayyaci IhediohaWata majiya ta bayyana cewa an yi wa tsohon Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai a zamanin Tambuwal, Emeka Ihedioha tayin shiga tafiyar siyasar Tinubu kimanin wata shida da suka gabata. Shi ma Ihedioha, EFCC ta gayyace shi domin amsa tambayoyi a cikin wannan makon.
A wata wasika da hukumar ta hannun Daraktan Bincike Abdukarim Chukkol, a ranar 18nga watan Yuli, 2025, ta aike wa Sakataren Gwamnatin Jihar Iko ta buƙaci samun wasu bayanai daga wasu jami’an gwamnatin jihar.
Wasiƙar ta buƙaci jami’an su bayyana a ofishin hukumar EFCC a ranar Talata, 11 ga Agusta, 2025, domin amsa tambayoyi.
“Ana buƙatar su zo da takardun izinin duk kuɗaɗen da aka kashe daga ranar 29 ga watan Mayu, 2019 zuwa 14 ga watan Janairu, 2020.”
Majiyar da ta nuna wa wakilinmu takardar ta bayyana cewa Ihedioha ya dawo daga tafiyar da ya yi daga ƙasar waje domin amsa gayyatar EFCC.
Ihedioha wanda a yanzu ya koma jam’iyyar ADC ya kasance Gwamnan Jihar Imo daga ranar 29 ga watan Mayu, 2019 zuwa 14 ga watan January, 2020, lokacin da Kotun Ƙoli ta soke zaɓensa tare da ayyana Hope Uzodinma, a matsayin wanda ya yi nasara.
Alaƙar Tambuwal da Atiku da ADCSanata Tambuwal, wanda ɗan babbar Jam’iyyar adawa ta PDP ne ya bayyana goyon bayansa ga tafiyar haɗakar ’yan adawa ta sabuwar Jam’iyyar ADC.
An gan shi tare da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar da ɗan takarar shugaban ƙasa na Jam’iyyar LP a zaɓen 2023, Peter Obi da tsohon Gwamnan Jihar Kaduna Nasir El-Rufai a yayin taron da suka shiga ADC a ranar 2 ga watan Yuli 2025.
A taron ne suka amince da ADC a matsayin inuwar da za su yi amfani da ita domin ƙalubalantar Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu a zaɓen 2027 da ke tafe.
Kazalika Tambuwal ya kasance tare da Atiku a lokacin taron jana’izar tsohon Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a mahaifasrsa da ke Daura, Jihar Katsina.
Sai dai saɓanin Atiku da ya sauya sheka daga PDP zuwa ADC, har yanzu Tambuwal bai fice daga PDP ba. Haka kuma yana da alaƙa mai ƙarfi da Atiku, wanda ake ganin ta wuce siyasa zuwa ƙawancen adawa.
Alakarsu ta fara ɗaukar hankali ne a lokacin babban zaɓen ’yan takarar shugaban ƙasa na PDP a 2019, inda bayan Tambuwal ya faɗuwa, ya bayyana goyon bayansa ga Atiku, domin fafatawa da shugaban kasa mai ci a lokacin, Marigayi Muhammadu Buhari.
A 2022 kuma Tambuwal ya janye neman takararsa a zauren zaɓen dan takarar shugaban ƙasa na PDP, ya kuma buƙaci deleget su zaɓi Atiku a madadinsa.
Wannan ne ake ganin ya ba wa Atiku damar kayar da Nyesom Suke da sauran masu neman tikitin takarar PDP.
A baya-bayan kuma Tambuwal ya raka Atiku wajen wasu manyan tattaunawa da shugabannin adawa kamar tsohon Shugaban Ƙasa Marigayi Muhammadu Buhari, gabanin ƙulla haɗakar ’yan adawa domin shiga ADC da nufin tunkarar APC a zaɓen 2027.