Aminiya:
2025-06-14@14:51:19 GMT

Zaɓen 1993: IBB ya wallafa ba daidai ba a littafinsa — Sule Lamiɗo

Published: 14th, May 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Jigawa, Alhaji Sule Lamiɗo, ya musanta dalilin da tsohon shugaban mulkin sojin Nijeriya, Ibrahim Badamasi Babangida ya bayar a littafinsa dangane da soke zaɓen 1993.

Tsohon Ministan Harkokin Wajen Nijeriyar ya ce dalilin da IBB ya bayar cewa shi ne abin da ya sa ya rushe zaɓen 1993, “ba gaskiya” ba ne.

Janar Babangida a littafinsa mai suna “A Journey in Service” ya yi zargin cewa marigayi Janar Sani Abacha ne ke da alhakin rushe Zaɓen 12 ga watan Yunin 1993.

Trump ya janye takunkumin da Amurka ta ƙaƙaba wa Syria ‘Duk da hauhawar farashi tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka’

Alhaji Sule Lamido ya faɗi hakan ne a littafin tarihinsa da ya rubuta mai suna “Being True to Myself” wanda aka ƙaddamar ranar Talata a Abuja.

Littafin mai shafi kimanin 500 ya mayar da hankali ne kan rayuwar marubucin tun daga ƙuruciya har zuwa gwagwarmayar siyasarsa daga jamhuriya ta biyu kawo yanzu.

Abin da Sule Lamiɗo ya faɗi

A wani babi mai taken “Matsayata kan rushe zaɓen 12 ga watan Yuni”, Sule Lamiɗo ya musanta dalilin da Janar Ibrahim Badamasi Babangida ya bayar a littafinsa mai suna “A Journey in Service” a matsayin dalilin da ya sa ya rushe zaɓen watan Yunin 1993.

Bayan kammala ƙaddamar da littafi, marubucin ya yi wa BBC Hausa ƙarin bayani dangane da haƙiƙanin abin da yake nufi a babin kamar haka:

“A littafin Babangida ya ce Abiola shi ya ci zaɓe. A gaskiya shi ne ya ci zaɓen. Yanzu hujjar sokewa kuma wani abu ne daban.

“Amma ni abin da ya gaya min cewa shi ne dalilin da ya sa ya soke zaɓen shi ne saboda Abiola yana bin Najeriya bashin kuɗi naira miliyan 45,000 saboda haka idan ya ba shi wannan mulki to zai amfani da mulkin ya biya kansa kuma a lokacin nan ƙasar ba ta da wannan kuɗin da za ta biya shi, shi ya sa ya soke zaɓen.

“Kenan Abiola ya ci zaɓen amma an zalunce shi an hana shi sannan kuma ga kuɗi yana bi ba a biya shi ba.

“Idan ana so a yi adalci tunda mutumin nan ya mutu to kuɗin da yake bi naira miliyan 45,000 kamar yadda Babangida ya gaya min shi ya sa ya soke zaɓen nan to a ba wa iyalan Abiola, a biya su kuɗinsu. Shi kenan daga nan komai ya ƙare kenan.”

“Shi ya sa nake faɗa wa Tinubu cewa ya kamata maganar June 12 a ƙare ta. Saboda haka a biya wannan bashin na naira miliyan 45,000 ga iyalansa. Shi kenan magana ta ƙare.”

Abin da IBB ya faɗi a littafinsa

Janar Ibrahim Badamasi Babangida a littafin nasa mai suna “A Journey in Service” ya amince da cewa Cif Mashood Abiola ɗan takarar shugabancin ƙasa a jam’iyyar SDP, shi ne ya lashe zaɓen 1993 da ya rushe.

Duk da dai Janar ɗin ya ɗauki alhakin rushe zaɓen amma ya ɗora laifin a kan wasu manyan sojoji da ke aiki ƙarƙashin tsohon hafsan hafsoshin lokacin, Janar Sani Abacha cewa su ne suka rushe zaɓen ba tare da “izinina ba”.

To sai dai littafin na IBB ya janyo martani daga iyalai da ’yan uwan Janar Sani Abacha inda suka yi watsi da zargin.

“Yana da muhimmanci in bayyana cewa Janar Sani Abacha ba shi ba ne shugaban ƙasa ko kwamandan dakarun Nijeriya a lokacin da aka rushe zaɓen 12 ga Yuni ba.

“Kuma an yanke hukuncin soke zaɓen ne ƙarƙashin mulkin Janar Ibrahim Babangida wanda a lokacin shi ne shugaban mulkin soji kuma shi ke da ƙarfin iko a, hakazalika shi ke da alhakin dukkanin ayyukan da gwamnatinsa ta yi,” in ji wata sanarwa da iyalan Abacha suka fitar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Janar Sani Abacha Babangida ya rushe zaɓen soke zaɓen zaɓen 1993

এছাড়াও পড়ুন:

Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya

Ana zargin wata mata mai suna Khadija kan zargin kashe ’yarta mai shekaru 11, Fadila, saboda Naira 100 da ta samu a yawon Sallah a unguwar Tukur Tukur da ke Ƙaramar Hukumar Zariya a Jihar Kaduna.

Lamarin ya faru ne a ranar Asabar kafin sallar Magariba, inda lamarin ya janyo ce-ce-ku-ce a unguwar har maƙwabta suka ƙi yi wa gawar yarinyar sallah saboda tsoron abin da zai biyo baya.

Ranar Dimokuraɗiyya: Tinubu zai yi wa ’yan Najeriya jawabi Majalisar Dokokin Kuros Riba ta dakatar da shugabar ƙaramar hukuma na wata 3

Wasu maƙwabta sun bayyana cewa Khadija ta doke Fadila da taɓarya ne saboda ta zargi yarinyar da satar Naira 100.

Sun ce irin wannan ɗabi’a na duka da tsangwama ba sabon abu ba ne domin sau da dama idan ta tura Fadila talla aka samu matsala, sai ta lakaɗa mata dukan tsiya.

Wani mutum ya ce: “Dalilin da ya sa muka ƙi yi mata sallah shi ne, ba a ɗauki matakin da ya dace ba. An zubar da gaskiya. Saboda haka mu ma muka yanke shawarar ba za mu yi mata sallah ba.”

Amma mahaifiyar da ake zargi, wato Khadija, ta musanta zargin cewa ta yi wa ’yarta da duka da taɓarya.

Ta ce a lokacin da ta ke dukan yarinyar, ba kowa a gidan sai yara.

Mijin matar, Malam Mustapha Musa, ya shaida wa wakilinmu cewa lokacin da lamarin ya faru ba ya gida, don haka bai san yadda abin ya wakana ba.

Tuni mahaifin Fadila ya ɗauki gawar ’yarsa zuwa ƙauyensu da ke ji6har Kano domin yi mata sutura.

Ya ce: “Na bar komai da hannun Allah.”

Wani jami’in tsaron sa-kai wanda ya buƙaci a sakaya sunansa ya ce sun gayyaci Khadija da mijinta ofishinsu domin amsa tambayoyi, amma daga baya sai suka janye bayan sun ga ’yan sanda sun isa wajen.

Wakilinmu ya kai ziyara babban ofishin ’yan sanda da ke Ɗan Magaji, amma ya tarar babban jami’in ba ya nan.

Mataimakinsa ya ce ba su da masaniya game da lamarin.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna, DSP Mansur Hassan, ya ce: “Ka jira, zan tuntuɓi ofishin yankin don jin yadda lamarin yake.”

Har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto, ba a samu ƙarin bayani daga ’yan sandan ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sudan Ta Zargi Janar Haftar Na Libiya Da Goyon Bayan ‘Yan Tawayen Kasarta Na Rapid Support Forces
  • IRGC : Iran ta kai hare hare wurare a kalla 150 a Isra’ila
  • Kwamadan Sararin Samaniyar Iran Na Dakarun Kare Juyi Haji Zadeh Yana Cikin Wadanda Su Ka Yi Shahada
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya
  • Iran ta Yi Gargadin Cewa Zata Fice Daga Yarjeniyar NPT Idan Hukumar IAEA Ta Tir Da Ita
  • An kashe mutum 15 a sabbin hare-hare a Filato
  • Ana zargin uwa da kashe ’yarta kan Naira 100 a Zariya