Wike Ya Gargaɗi PDP Kan Bai Wa Ɗan Arewa A 2027
Published: 13th, May 2025 GMT
“Amma idan yanzu aka sake bai wa Arewa takara, wannan tsari tsakanin Arewa da Kudu zai ruguje.”
Wike, wanda tsohon gwamnan Jihar Ribas ne, yana daga cikin fitattun jiga-jigan PDP da ke goyon bayan daidaito da karɓa-karɓar mulki tsakanin Arewa da Kudu domin tabbatar da zaman lafiya da haɗin kan ƙasa.
A baya dai, rikici wajen tantance daga inda ɗan takarar PDP zai fito ya janyo rabuwar kai a cikin jam’iyyar, lamarin da ya taimaka wajen rage ƙarfinta a zaɓen 2023.
Masana siyasa na ganin wannan gargaɗi na Wike na iya sake haifar da muhawara a jam’iyyar, musamman yayin da ta ke shirin fuskantar babban zaɓen 2027.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
2027: Zan karɓi kowane irin muƙami da Tinubu zai ba ni — Sanata Barau
Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau Jibrin, ya ce zai karɓi kowane irin muƙami da Shugaba Bola Tinubu ya ba shi, amma ya ce a yanzu ba ya son a yi magana kan batun zama mataimakin shugaban ƙasa a zaɓen 2027.
Yayin wata ganawa da manema labarai kan shirin sauraron ra’ayoyin jama’a da za a yi kan sauya kundin tsarin mulki, Barau ya ce, “Duk abin da Shugaba ya ce na yi, zan yi shi da yaƙini na gaske.”
Ba zan yi Tinubu ba a 2027 matukar ya canza Kashim Shettima – Sheik Jingir NAJERIYA A YAU: Yadda ‘Yan Najeriya Za Su Kula Da Lafiyar Jikin SuWannan na zuwa ne bayan ya shawarci wani rukuni da ke goyon bayan ya zama mataimakin shugaban ƙasa da su mayar da hankali wajen tallafa wa ayyukan Tinubu maimakon batun siyasa.
Ya ce, “Yin wannan magana a yanzu bai dace ba. Ban san waɗannan mutane ba, amma na gode da yadda suka yarda da ni.
“Na faɗa musu su daina ɓata lokaci kan abin da lokacisa bai yi ba, su yi amfani da kuɗinsu da ƙarfinsu wajen tallafa wa Shugaban Ƙasa.”
“Idan lokacin siyasa ya yi, za mu shiga. Amma yanzu lokaci ne na aiki.”
Barau ya bayyana Shugaba Tinubu a matsayin jagoran siyasarsa, wanda ya ce yana yi wa biyayya.
Ya gode masa saboda taimakonsa wajen warware rikicin jam’iyya a Kano, dawowarsa majalisa a 2023, da kuma tallafa masa ya zama Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa.
“Ina son na sanar da ku, idan Shugaba ya ce yana buƙatar na yi aiki tare da shi, zan ce masa ‘na gode sosai,’ kuma zan yi. Duk abin da ya buƙaci na yi, zan yi shi. Zan yi masa biyayya. Shi ne uban ƙasa, kun sani.”
Barau, ya ce su dukkaninsu ’yan jam’iyyar APC ne, kuma suna da ra’ayoyi iri ɗaya.
“Mun fito daga gida ɗaya, mun sadaukar da kanmu ga ci gaba. Ina da ra’ayin ganin an samu ci gaba. Don haka zan yi wa Shugaban Ƙasa cikakkiyar biyayya. A 2027, duk abin da ya ce na yi, zan yi.”