Ko yanzu aka yi zaɓe Tinubu ne zai yi nasara — Oshiomhole
Published: 14th, May 2025 GMT
Tsohon Shugaban APC na ƙasa, Sanata Adams Oshiomhole ya bayyana cewa ko yau aka yi zaɓe, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne zai yi nasara.
Oshiomhole wanda shi ne mai wakiltar shiyyar Edo ta Arewa a Majalisar Dattawan Nijeriya ya bayyana hakan ne a wata hirarsa da gidan talabijin na Channels a safiyar wannan Larabar.
Tsohon gwamnan na Jihar Edo ya faɗi hakan a lokacin da yake tsokaci kan sauya sheƙar da Sanatocin Kebbi uku suka yi daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Ya ce, Tinubu ya ɗauki ƙwararan matakai domin daidaita Nijeriya, yana mai cewa kafin gwamnatinsa manoma a wasu sassan ƙasar ba sa iya shiga gonakinsu amma yanzu lamarin ya sauya.
Da yake tsokaci kan guguwar sauyin sheƙa da ake gani a halin yanzu, Oshiomhole ya ce babu wani ɗan siyasa a Nijeriya mafi shahara da sauye-sauyen sheƙa a tsakanin jam’iyyu kamar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar.
“A yanzu babu wani ɗan siyasa a Nijeriya mafi dacewar rubuta littafi kan sauya sheƙa daga wannan jam’iyya zuwa wannan kamar Atiku,” in ji Oshiomhole.
Ya yi bayanin cewa Atiku ya fi kowane ɗan siyasa shahara idan an taɓo batun sauya sheƙa domin a cewarsa shi ne ya fara ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa ACN wadda ta rikiɗe zuwa APC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
‘Duk da hauhawar farashi tattalin arzikin Nijeriya ya haɓaka’
Bankin Duniya ya sanar da cewa duk da ƙalubalen hauhawar farashin da Nijeriya take fuskanta, tattalin arzikin ƙasar ya ƙaru a shekarar da ta gabata.
Babban bankin ya ce tattalin arzikin Nijeriyar ya samu haɓaka a kusan shekaru goma a 2024, inda a watanni uku na karshen 2024 aka samu haɓaka sosai.
HOTUNA: Trump na ziyara a Saudiyya Majalisa ta yi watsi da kudurin dokar mulkin karba-karbaHakan na ƙunshe cikin wani rahoto da babban jami’in tattalin arzaki na Bankin Duniya a Nijeriya, Alex Sienaert, ya fitar ranar Litinin a Abuja.
Sienaert ya bayyana cewa tattalin arzikin ya ƙaru da kashi 4.6 a watanni uku na ƙarshen 2024, inda ya kuma yi nuni da cewa zai ci gaba da haɓaka a farkon 2025.
Sai dai ya yi gargaɗin cewa hauhawar farashi na ci gaba da zama ƙalubale amma ana sa ran tattalin arzikin Nijeriyar zai haɓaka a wannan shekarar da kashi 3.6.
Nijeriya na ci gaba da fama da hauhawar farashi, inda Sieneart ya yi gargaɗin cewa dole ne a ɗauki matakan tsuke bakin aljihu da tasarrufin kuɗaɗe bisa doka da oda.
Sienaert ya ce harajin gwamnati ya ƙaru da kashi 4.5 sama da na shekarar da ta gabata, wanda “muhimmiyar nasara” ce, da janye tallafi ga kuɗaɗen ƙasashen waje, da kyautata tsarin karɓar haraji da yawan saka kuɗaɗe a asusun gwamnati suka kawo.
Kuɗaɗen shiga masu yawa da aka samu sun taimaka wajen cike giɓin Kasafin Kuɗi da aka yi hasashen ya kai kusan kashi uku a 2024, daga kashi 5.4 da aka samu a 2023.
Manyan matakan da shugaban ƙasar Bola Tinubu ke ɗauka, ciki har da kawo ƙarshen tallafin mai, da janye tallafi kan wutar lantarki da karya darajar naira har sau biyu, sun ƙara matsa lamba ga farashin kayayyaki.