Ko yanzu aka yi zaɓe Tinubu ne zai yi nasara — Oshiomhole
Published: 14th, May 2025 GMT
Tsohon Shugaban APC na ƙasa, Sanata Adams Oshiomhole ya bayyana cewa ko yau aka yi zaɓe, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne zai yi nasara.
Oshiomhole wanda shi ne mai wakiltar shiyyar Edo ta Arewa a Majalisar Dattawan Nijeriya ya bayyana hakan ne a wata hirarsa da gidan talabijin na Channels a safiyar wannan Larabar.
Tsohon gwamnan na Jihar Edo ya faɗi hakan a lokacin da yake tsokaci kan sauya sheƙar da Sanatocin Kebbi uku suka yi daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Ya ce, Tinubu ya ɗauki ƙwararan matakai domin daidaita Nijeriya, yana mai cewa kafin gwamnatinsa manoma a wasu sassan ƙasar ba sa iya shiga gonakinsu amma yanzu lamarin ya sauya.
Da yake tsokaci kan guguwar sauyin sheƙa da ake gani a halin yanzu, Oshiomhole ya ce babu wani ɗan siyasa a Nijeriya mafi shahara da sauye-sauyen sheƙa a tsakanin jam’iyyu kamar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar.
“A yanzu babu wani ɗan siyasa a Nijeriya mafi dacewar rubuta littafi kan sauya sheƙa daga wannan jam’iyya zuwa wannan kamar Atiku,” in ji Oshiomhole.
Ya yi bayanin cewa Atiku ya fi kowane ɗan siyasa shahara idan an taɓo batun sauya sheƙa domin a cewarsa shi ne ya fara ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa ACN wadda ta rikiɗe zuwa APC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji sun yi juyin mulki a Guinea-Bissau
Sojoji a Guinea-Bissau sun ce sun yi juyin mulki tare da karɓe ragamar mulkin ƙasar.
Sun kuma sanar da dakatar da zaɓukan ƙasar tare da rufe iyakokinta nan take.
’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSSWannan na zuwa ne kwana uku bayan ƙasar ta gudanar da zaɓen ’yan majalisa da na shugaban ƙasa.
A yau ne aka wayi gari ana ji. harbe-harbe a kusa da fadar shugaban ƙasa, lamarin da ya tashi hankalin mutane.
Daga bisani kuma dakarun soji suka rufe babban titin da ke zuwa fadar shugaban ƙasar.
A cewar majiyar AFP, sojojin sun karanta sanarwar ƙwace mulkin ƙasar a hedikwatar rundunar da ke babban birnin ƙasar, Bissau.
Cikakken rahoto na tafe…