Ko yanzu aka yi zaɓe Tinubu ne zai yi nasara — Oshiomhole
Published: 14th, May 2025 GMT
Tsohon Shugaban APC na ƙasa, Sanata Adams Oshiomhole ya bayyana cewa ko yau aka yi zaɓe, Shugaba Bola Ahmed Tinubu ne zai yi nasara.
Oshiomhole wanda shi ne mai wakiltar shiyyar Edo ta Arewa a Majalisar Dattawan Nijeriya ya bayyana hakan ne a wata hirarsa da gidan talabijin na Channels a safiyar wannan Larabar.
Tsohon gwamnan na Jihar Edo ya faɗi hakan a lokacin da yake tsokaci kan sauya sheƙar da Sanatocin Kebbi uku suka yi daga jam’iyyar PDP zuwa APC.
Ya ce, Tinubu ya ɗauki ƙwararan matakai domin daidaita Nijeriya, yana mai cewa kafin gwamnatinsa manoma a wasu sassan ƙasar ba sa iya shiga gonakinsu amma yanzu lamarin ya sauya.
Da yake tsokaci kan guguwar sauyin sheƙa da ake gani a halin yanzu, Oshiomhole ya ce babu wani ɗan siyasa a Nijeriya mafi shahara da sauye-sauyen sheƙa a tsakanin jam’iyyu kamar tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar.
“A yanzu babu wani ɗan siyasa a Nijeriya mafi dacewar rubuta littafi kan sauya sheƙa daga wannan jam’iyya zuwa wannan kamar Atiku,” in ji Oshiomhole.
Ya yi bayanin cewa Atiku ya fi kowane ɗan siyasa shahara idan an taɓo batun sauya sheƙa domin a cewarsa shi ne ya fara ficewa daga jam’iyyar PDP zuwa ACN wadda ta rikiɗe zuwa APC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Shugaban Ƙasa Zaɓe
এছাড়াও পড়ুন:
Ruwan Wutan sojan Nijeriya Ya Kashe ‘Yan Bindiga A Zamfara.
Dakarun Operation FANSAN Yamma (OPFY) sun yi nasarar fatattakar ‘yan ta’adda da dama a wani hari da suka kai ta sama da kasa a yankin Makakkari da ke dajin Gando a karamar hukumar Bukkuyum a jihar Zamfara.
Wannan farmakin wanda ya gudana a ranar 10 ga watan Agustan shekarar 2025, ya biyo bayan wasu bayanan sirri da suka samu cewa dimbin ‘yan ta’addan da ke biyayya ga marigayi Halilu Buzu da Alhaji Beti sun taru a cikin dajin inda suka shirya kai harin ramuwar gayya kan al’ummomin Addabka da Nasarawan Burkullu a garin Bukkuyum.
Jami’in yada labarai na rundunar ‘Operation Fansan Yamma OPFY’ Kyaftin David Adewusi, ya ce bayanan sirri sun nuna cewa, harin da suka shirya kai harin shi ne ramuwar gayya da suka sha a baya-bayan nan a arangamar da suka yi da jami’an tsaro da wasu rundunonin tsaro.
Ya bayyana cewa, a wani samame na hadin gwiwa na kasa da ya biyo baya, dakarun da ke karkashin sashe na 2 sun kame tare da fatattakar ‘yan ta’addan da suka gudu daga inda aka kai harin ta sama.
Kyaftin Adewusi ya tabbatar wa ‘yan kasa masu bin doka da oda cewa ‘yan ta’adda da sauran masu rike da makamai ba za su samu mafaka a yankin Arewa maso Yamma da wasu sassan shiyyar Arewa ta tsakiya ba.
Ya nanata kudurin sojojin na fatattakar abokan gaba a duk inda suka taru ko kuma suka matsa sannan ya bukaci mazauna yankin da su baiwa jami’an tsaro hadin kai ta hanyar ba da rahoton abubuwa, yana mai cewa bayanan da suka dace kan lokaci na da matukar muhimmanci wajen kare al’umma da kuma kawo karshen barazanar ta’addanci da ‘yan fashi.
REL/AMINU DALHATU.