Iran ta yi tir da sabbin takunkumin ‘rashin adalci’ da Amurka ta kakaba mata
Published: 13th, May 2025 GMT
Iran ta yi tir da sabbin takunkuman da ta danganta da na rashin adalci da Amurka ta kakaba mata.
Amurka dai ta kakaba wa Iran sabbin takunkuman, ne duk da ci gaba da tattaunawar nukiliyar da ake yi tsakanin kasashen biyu.
A cikin wata sanarwa da ta fitar jiya Litinin, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ayyana wasu ‘yan kasar Iran guda uku da wani kamfani mai suna Fuya Pars Prospective Technologists, bisa zargin cewa suna da hannu wajen gudanar da bincike da kuma ayyukan da suka shafi makaman nukiliya.
Amurka, ta ce takunkumin ya shafi toshe duk wasu kadarori na mutanen a Amurka tare da hana mu’amalar kasuwanci da su.
Sabon takunkumin ya zo ne kwana guda bayan Iran da Amurka sun gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa da nufin kulla sabuwar yarjejeniya kan shirin nukiliyar Iran da kuma cire takunkumin da aka kakabawa Tehran.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Barin PDP Zuwa Wata Jam’iyyar Alamun Rashin Jarumta Ne – Gwamnan Bauchi
ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Sanatan Bauchi Ta Arewa Ya Fice Daga Jam’iyyar PDP October 11, 2025
Siyasa Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu October 9, 2025
Labarai Kotu Ta Yi Watsi Da Ƙarar Da Aka Shigar Da Tinubu Kan Sanya Dokar Ta-Ɓaci A Ribas October 2, 2025