Iran ta yi tir da sabbin takunkuman da ta danganta da na rashin adalci da Amurka ta kakaba mata.

Amurka dai ta kakaba wa Iran sabbin takunkuman, ne duk da ci gaba da tattaunawar nukiliyar da ake yi tsakanin kasashen biyu.

A cikin wata sanarwa da ta fitar jiya Litinin, ma’aikatar harkokin wajen Amurka ta ayyana wasu ‘yan kasar Iran guda uku da wani kamfani mai suna Fuya Pars Prospective Technologists, bisa zargin cewa suna da hannu wajen gudanar da bincike da kuma ayyukan da suka shafi makaman nukiliya.

Amurka, ta ce takunkumin ya shafi toshe duk wasu kadarori na mutanen a Amurka tare da hana mu’amalar kasuwanci da su.

Sabon takunkumin ya zo ne kwana guda bayan Iran da Amurka sun gudanar da zagaye na hudu na tattaunawa da nufin kulla sabuwar yarjejeniya kan shirin nukiliyar Iran da kuma cire takunkumin da aka kakabawa Tehran.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida

Gwamnan ya buƙaci kamfanin da ke aikin da ya yi aiki mai kyau kuma ya kammala a kan lokaci.

Ya ce dole ne a gina gidajen cikin inganci domin taimakawa wajen rage matsalar rashin gidaje da jama’a ke fuskanta a jihar.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
  • Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)
  • NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?
  • Sheikh Dahiru Bauchi ya cika shekara 101 a duniya
  • Sabbin Dokokin Haraji Za Su Fara Aiki A Janairun 2026 — Adedeji
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
  • Isra’ila da Iran sun ci gaba da musayar wuta duk da sanarwar tsagaita wuta
  • Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
  • DAGA LARABA: Ko Najeriya Na Da Kudin Renon Sabbin Jihohi?