Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Ta Iran Ya Jaddada Bukatar Hukunta Haramtacciyar Kasar Isra’ila
Published: 14th, May 2025 GMT
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ya yi kira da a kakaba takunkumi ga gwamnatin mamayar Isra’ila da kuma kafa ‘yantacciyar kasar Falasdinu
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Muhammad Baqir Qalibaf ya yi kira ga kasashen musulmi da su kakaba takunkumin siyasa da tattalin arziki da na soji kan gwamnatin yahudawan sahayoniyya domin kawo karshen kisan kiyashin da take yi a Gaza.
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana hakan ne a yau Laraba, yana mai jaddada cewa: A yau, tsarin rayuwa da tattalin arzikin gwamnatin ‘yan sahayoniyya ya ratsa ta wasu kasashen musulmi, kuma lokaci ya yi da kasashen musulmi za su tilasta wa wannan gwamnatin mamaya ta hanyar yanke shawarar gama-gari don kawo karshen killace Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ta
এছাড়াও পড়ুন:
Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
Yau Jumma’a da safe, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gana da firaministan kasar Senegal Ousmane Sonko da shugaban kasar Ecuador Daniel Noboa a birnin Beijing, fadar milkin kasar Sin. Wadannan shugabannin biyu sun zo kasar Sin ne domin halartar taron dandalin tattaunawa kan tattalin arzikin duniya na lokacin zafi na Davos.
A yayin ganawarsa da Ousmane Sonko, Xi Jinping ya ce, kasar Sin tana son zurfafa hadin gwiwar dake tsakanin Sin da Senegal, tare da aiwatar da “Manyan matakai 10 bisa hadin gwiwar abokantaka” yadda ya kamata, da kuma kaddamar da karin ayyukan tallafawa al’umma, tare da sa kaimi ga kamfanonin kasar Sin su zuba jari a kasar Senegal domin raya sabbin makamashi, da gina ababen more rayuwa na zamani da dai sauransu, ta yadda Sin da Senegal za su kasance abokan juna dake hadin gwiwa da cimma moriyar juna.
A nasa bangare kuma, Ousmane Sonko ya ce, kasar Senegal da kasar Sin mambobin kasashe masu tasowa ne dake da buri iri daya, kuma kasar Segenal tana son yin mu’amala da kasar Sin kan harkokin kasa da kasa da na shiyya-shiyya, tana kuma tsayawa tsayin daka wajen karfafa huldar abokantaka bisa manyan tsare-tsare da kasar Sin, domin inganta yanayin adalci na duniya, tare da kiyaye moriyar kasashe masu tasowa.
Ban da haka kuma, bayan ganawar shugaba Xi Jinping da shugaban kasar Ecuador Daniel Noboa, an kulla shirin “Hadin gwiwa tsakanin gwamantin Jamhuriyyar Jama’ar kasar Sin da gwamantin Jamhuriyar kasar Ecuador, wajen inganta shawarar ‘Ziri daya da hanya daya’”. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp