’Yan bindiga sanye kayan ’yan sanda sun kai hari a wata makarantar sakandaren gwmanati inda suka harbe wani malami har lahira sannan suka sace mata uku a Jihar Zamfara.

Cikin matan da aka sace har da matar malamin a wannan mummunan lamari ya faru a Makarantar Sakandare ta Gwamnati da ke Raka, a ranar Asabar.

Wani jami’in gudanarwa na makarantar, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa maharan sun shiga harabar makarantar ne ta wata ƙofa da ke bayan katangar makarantar.

“Sun mamaye harabar makarantar sanye da cikakkun kayan ’yan sanda, da hula da takalman roba. Sun yi amfani da kofar da ke bayan katangar wajen shiga da kuma guduwa bayan harin,” in ji shi.

Rahotanni sun nuna cewa an kashe malamin ne a lokacin da yake ƙoƙarin turjewa.

“Ya fuskanci ’yan bindigar har ma ya yi nasarar rinjayar ɗayansu kafin a harbe shi har lahira,” kamar yadda majiyar ta bayyana.

Daga bisani maharan sun sace matar malamin da wasu mata biyu a lokacin harin.

Shaidu daga ma’aikatan makarantar sun bayyana cewa, “Ƙarar harbe-harben bindigar da ya ɓarke ya sa ɗalibai suka fara ihu ‘ɓarayi,’ wanda da farko ya sa wasu ma’aikata zaton ƙaramar sata ce. Sai dai, yawan harbe-harben da aka yi a jere ya kawar da wannan zaton,” in ji wani ma’aikaci.

Ya ƙara da cewa ’yan sanda da sojoji sun isa wurin ne bayan maharan sun riga sun gudu.

“Babban ɗan sanda na yankin (DPO) ya taimaka wajen kai gawar malamin gidansa da ke cikin gari domin shirye-shiryen jana’iza,” kamar yadda majiyar ta ƙara bayyanawa.

Makarantar Sakandare ta Gwamnati da ke Raka, kwanan nan ta sauya tsarin karatunta zuwa ne je-ka-ka-dawo saboda rashin tsaro da ya addabi yankin.

Ma’aikatan makarantar sun tabbatar da cewa, “Wannan shi ne karo na farko da aka kai mana hari. Mutanen yankin sukan zo nan don shakatawa,” in ji wani ma’aikaci cikin baƙin ciki.

Tagwayen hare-hare a Zamfara

Wannan harin da aka kai makarantar ya zo daidai da jerin hare-hare da ’yan bindiga suka kai a wasu ƙananan hukumomi da dama a Jihar Zamfara.

A Ƙaramar Hukumar Anka, an ruwaito cewa ’yan bindiga sun sace mata biyu da yara shida na wani magidanci Abdullahi Azee.

A ƙauyen Madira da ke Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda, an kashe mutane biyu.

Bugu da ƙari, a Damba da ke Ƙaramar Hukumar Gusau, an sace wani mutum da matarsa, da jaririnsu ɗan wata huɗu.

A halin da ake ciki, a Ƙaramar Hukumar Maru, ƙoƙarin da aka yi na mamaye ƙauyen Kadauri ya ci tura sakamakon haɗin gwiwar ’yan banga na yankin da jami’an tsaro, wanda ya tilasta wa maharan janyewa.

Jihar Zamfara ta ci gaba da zama cibiyar ayyukan ’yan bindiga da satar mutane a ’yan shekarun nan, duk da ƙarin yawan jami’an tsaro da aka tura.

Lokacin da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya bayyana cewa ba shi da masaniya game da harin da aka kai makarantar.

Ya ba da tabbacin cewa zai yi bincike domin tabbatar da bayanan sannan ya ba da amsa.

Sai dai, har zuwa lokacin da ake rubuta wannan labarin, ba a samu wani ƙarin bayani daga rundunar ’yan sandan ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Makaranta sakandare Zamfara Ƙaramar Hukumar Jihar Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Ebonyi, ta kama wani mutum mai suna Chukwuma Onwe, ɗan Ƙaramar Hukumar Izzi, bisa zargin sayar da ɗan da aka haifa masa kwanaki biyar kan Naira miliyan 1.5.

An gano cewa Onwe ya sayar wa wata mata mai suna Chinyere Ugochukwu jaririn, wacce ake zargin tana cikin ƙungiyar safarar yara zuwa ƙasashen waje.

ASUU za ta fara yajin aikin mako 2 daga ranar Litinin Egbetokun ya sauke kwamishinan ’yan sandan Abuja

Dukkaninsu suna hannun ’yan sanda.

Wata majiyar ’yan sanda ta bayyana cewa matar Onwe, mai suna Philomena Iroko, ce ta fallasa shi bayan ta samu labari daga maƙwabta cewa mijinta ya sayar da jaririn da suka haifa.

Da ta tabbatar da hakan, sai ta garzaya ta kai rahoto ofishin ’yan sanda, inda aka kama Onwe ba tare da ɓata lokaci ba.

Kakakin rundunar jihar Ebonyi, SP Joshua Ukandu, ya tabbatar da cewa an ceto jaririn daga hannun wacce ta saya shi.

Ya ce an kama Onwe da Chinyere Ugochukwu a ranar Juma’a a unguwar Azugwu, Ƙaramar Hukumar Abakaliki, kuma suna tsare a hannun ’yan sanda domin ci gaba da bincike.

Matar Onwe, Philomena, ta ce ta yi mamaki matuƙa cewa mijinta ya sayar da jaririn nasu.

Ta bayyana cewa tun bayan haihuwarta, Onwe, ya ce zai kai jaririn wajen ’yar uwarsa domin ta sa masa albarka, sai dai daga baya aka gano cewa ya sayar da shi.

Ta ce, “Yaronmu bai wuce kwanaki biyar da haihuwa ba, amma mijina ya sayar da shi.

“Ban taɓa tunanin zai yi haka ba. Ina roƙon jama’a da masu hannu da shuni su taimaka min a wannan hali da na tsinci kaina.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wata Kotu a Faransa ta yi watsi da rufe wata makarantar musulmi a birnin Nice  
  • Mutumin da ya sayar da ɗansa kan N1.5m ya shiga hannu a Ebonyi
  • Ayyukan Da Suka Sauya Fuskar Zamfara A Ƙarƙashin Gwamna Dauda Lawal
  • Maryam Sanda na cikin waɗanda Tinubu ya yi wa afuwa
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Babban Kwamanda Ya Jagoranci Ceton Mutanen Da Aka Sace A Kwara
  • Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida
  • ’Yan bindiga sun kashe Civilian JTF 8 a Zamfara