’Yan bindiga sanye kayan ’yan sanda sun kai hari a wata makarantar sakandaren gwmanati inda suka harbe wani malami har lahira sannan suka sace mata uku a Jihar Zamfara.

Cikin matan da aka sace har da matar malamin a wannan mummunan lamari ya faru a Makarantar Sakandare ta Gwamnati da ke Raka, a ranar Asabar.

Wani jami’in gudanarwa na makarantar, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa maharan sun shiga harabar makarantar ne ta wata ƙofa da ke bayan katangar makarantar.

“Sun mamaye harabar makarantar sanye da cikakkun kayan ’yan sanda, da hula da takalman roba. Sun yi amfani da kofar da ke bayan katangar wajen shiga da kuma guduwa bayan harin,” in ji shi.

Rahotanni sun nuna cewa an kashe malamin ne a lokacin da yake ƙoƙarin turjewa.

“Ya fuskanci ’yan bindigar har ma ya yi nasarar rinjayar ɗayansu kafin a harbe shi har lahira,” kamar yadda majiyar ta bayyana.

Daga bisani maharan sun sace matar malamin da wasu mata biyu a lokacin harin.

Shaidu daga ma’aikatan makarantar sun bayyana cewa, “Ƙarar harbe-harben bindigar da ya ɓarke ya sa ɗalibai suka fara ihu ‘ɓarayi,’ wanda da farko ya sa wasu ma’aikata zaton ƙaramar sata ce. Sai dai, yawan harbe-harben da aka yi a jere ya kawar da wannan zaton,” in ji wani ma’aikaci.

Ya ƙara da cewa ’yan sanda da sojoji sun isa wurin ne bayan maharan sun riga sun gudu.

“Babban ɗan sanda na yankin (DPO) ya taimaka wajen kai gawar malamin gidansa da ke cikin gari domin shirye-shiryen jana’iza,” kamar yadda majiyar ta ƙara bayyanawa.

Makarantar Sakandare ta Gwamnati da ke Raka, kwanan nan ta sauya tsarin karatunta zuwa ne je-ka-ka-dawo saboda rashin tsaro da ya addabi yankin.

Ma’aikatan makarantar sun tabbatar da cewa, “Wannan shi ne karo na farko da aka kai mana hari. Mutanen yankin sukan zo nan don shakatawa,” in ji wani ma’aikaci cikin baƙin ciki.

Tagwayen hare-hare a Zamfara

Wannan harin da aka kai makarantar ya zo daidai da jerin hare-hare da ’yan bindiga suka kai a wasu ƙananan hukumomi da dama a Jihar Zamfara.

A Ƙaramar Hukumar Anka, an ruwaito cewa ’yan bindiga sun sace mata biyu da yara shida na wani magidanci Abdullahi Azee.

A ƙauyen Madira da ke Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda, an kashe mutane biyu.

Bugu da ƙari, a Damba da ke Ƙaramar Hukumar Gusau, an sace wani mutum da matarsa, da jaririnsu ɗan wata huɗu.

A halin da ake ciki, a Ƙaramar Hukumar Maru, ƙoƙarin da aka yi na mamaye ƙauyen Kadauri ya ci tura sakamakon haɗin gwiwar ’yan banga na yankin da jami’an tsaro, wanda ya tilasta wa maharan janyewa.

Jihar Zamfara ta ci gaba da zama cibiyar ayyukan ’yan bindiga da satar mutane a ’yan shekarun nan, duk da ƙarin yawan jami’an tsaro da aka tura.

Lokacin da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya bayyana cewa ba shi da masaniya game da harin da aka kai makarantar.

Ya ba da tabbacin cewa zai yi bincike domin tabbatar da bayanan sannan ya ba da amsa.

Sai dai, har zuwa lokacin da ake rubuta wannan labarin, ba a samu wani ƙarin bayani daga rundunar ’yan sandan ba.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Makaranta sakandare Zamfara Ƙaramar Hukumar Jihar Zamfara yan bindiga

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kaduna, ta bayyana sabbin nasarorin da ta samu wajen yaƙi da laifuka a jihar, ta hanyar holen mutum 34 da ta kama da aikata laifuka daban-daban.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar, Rabi’u Muhammad, ya ce wannan ci gaba ya samu ne saboda sabbin dabarun aiki da kuma bayanan sirri da aka samu daga al’umma da hukumomin tsaro.

Jami’an tsaro sun ƙaddamar da shirin murƙushe ’yan bindiga a Kaduna Zulum ya ba kowanne ɗalibin Borno da ke karatu a Indiya tallafin N500,000

A Anguwar Barnawa da wasu wurare a Kaduna, rundunar Operation Fushin Kada ta kama mutane 13 da ake zargi da aikata fashi da makami da satar wayoyi a otel-otel da gidaje.

An ruwaito sun taɓa kashe ɗan sanda a shekarar 2024, kuma suna samun bayanai daga dilolin miyagun ƙwayoyi a wuraren shaƙatawa. A

An ƙwato bindiga ƙirar gida, gatari da adduna 13, mota, kwamfuta huɗu, wayoyi 13 da talabijin huɗu.

Haka kuma, a Nunbu Bashayi da ke Sanga, an kama mutane bakwai da ake zargi da garkuwa da mutane tare da neman kuɗin fansa.

Dukkanimsu sun amsa laifinsu kuma ana neman ragowar waɗanda suke tsere.

A wani samame daban, ’yan sanda sun kama wasu mutane huɗu da ake zargi da aikata fashi, fyaɗe da damfara.

Sun saba kai hari gidajen mutane, ɗaukar kuɗaɗen mutane, aikata fyaɗe sannan su riƙa ɗaukar bidiyo tsoratar da mutane.

A Zariya kuwa, an kama wasu mutane tara da suka haɗa da maza da mata waɗanda ake zargi da yi wa direban Adaidaita sahu fashi ta hanyar zuba masa magani a abin sha.

Rundunar ta kuma kama wani likitan bogi mai suna Adamu Abubakar Muhammed wanda ya yi wa mutane tiyata ba tare da shaidar karatun likitanci ba.

Ya yi amfani da takardun bogi wajen yin aiki na tsawon wata guda kafin a gano shi.

Kwamishinan, ya ce duk waɗanda aka kama suna hannun rundunar, kuma za a gurfanar da su kotu bayan kammala bincike.

Ya gode wa jami’an tsaro da al’umma kan haɗin kai, inda ya yi da a ci gaba da bayar da sahihan bayanai domin inganta tsaro a jihar da ƙasa baki ɗaya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An gano gawawwakin mata uku ’yan Kamaru da aka sace a Anambra
  • Wata mata ta kashe ’yar shekara 7 a Ribas
  • An janye ’yan sanda 11,566 daga gadin manyan mutane a faɗin Nijeriya
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kashe Sama da Naira Miliyan 5 Don Tallafawa Shirin AGILE
  • Ɗan bindiga ya harbe sojoji 2 a fadar shugaban Amurka
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • An ceto ’yan mata 24 d aka yi garkuwa da su a makaranta a Kebbi
  • ’Yan bindiga sun sace mutum 8 a Kano
  • Abin da ya sa nake haxa harkar fim da harkar karatu-Nabila