Majalisar Da Take Kula Da Nukiliyar Pakistan Za Su Yi Taron Gaggawa
Published: 10th, May 2025 GMT
Fira ministan kasar Pakistan Shahbaz Sharif ya kira yi Majalisar kasa wacce take kula da makaman Nukiliyar kasar da su yi taro.
Wannan matakin da ake yi wa Kallon mai hatsari yana faruwa ne a daidai lokacin da kasar ta Pakistan take yaki da Indiya.
Ita dai Majalisar kasar Pakistan dake kula da makaman Nukiliya da kuma manufofin kasa na koli, ta kunshi manyan kwamandojin soja, da fararen hula, aikinta kuma shi ne kula da manyan batutuwa da su ka shafi kasa daga ciki har da siyasar makaman Nukiliya da kuma makamai masu linzami.
Tashar talabijin din “Sama News” ta bayar da labarin dake cewa; Mahalarta taron za su yi bitar halin da ake ciki ne na yaki, da kuma tattaunawa matakan da za a dauka a fagen diplomasiyya da kuma hanyoyin tsaro da kare kai.
Ita dai kasar Indiya tana cewa ba za ta taba zama wacce za ta fara amfani da makamin Nukiliya ba, don haka ba za ta zama ta farko da za ta kai wa Pakistan hari ba. Ita kuwa Pakistan ta gina akidarta ta tsaro ne akan cewa za ta iya fara amfani da makamin Nukiliya da Zarar ta faminci cewa wanzuwar kasar tana fuskantar rushewa.
Jamhuriyar Musulunci ta Iran tana aiki tukuru domin ganin ta shiga Tsakani da kawo karshen rikicin dake tsakanin kasashen biyu da suke makwabtanta.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Putin : zamu dauki mataki idan Amurka ta koma gwajin makaman nukiliya
Shugaban Rasha Vladimir Putin ya yi gargadin cewa Moscow za ta dauki “matakan mayar da martani” idan Amurka ta koma gwada makaman nukiliya, a yayin da ake kara samun takun saka tsakanin manyan kasashen biyu masu makamman nukiliya.
A yayin wani taro da ya yi da Majalisar Tsaron Rasha a ranar Laraba, Putin ya umarci Ma’aikatar Harkokin Waje, Ma’aikatar Tsaro, hukumomin leken asiri, da su tantance yiwuwar sake fara gwaje-gwajen makamman nukiliya da kuma gabatar da shawarwari don matakan farko.
“Dangane da wannan batu, ina umurtar ma’aikatun dasu gabatar da shawarwari kan matakan farko da za su iya mayar da hankali kan shirye-shiryen gwaje-gwajen makaman nukiliya,” in ji Putin.
Umarnin da ya bayar ya nuna martani ne ga umarnin da shugaban Amurka Donald Trump ya bayar a ranar 30 ga Oktoba na cewa Washington za ta koma gwajin makamman nukiliya, wanda hakan ya kawo karshen dakatar da gwaje-gwajen irin wadanan miyagun makamai da aka yi tun 1992.
Trump ya yanke wannan shawara ne ‘yan kwanaki bayan ya la’anci Moscow saboda gwajin sabon makami mai linzami na Burevestnik, makamin da ke amfani da makamashin nukiliya wanda zai iya ɗaukar makamin nukiliya.
Rasha ba ta yi wani gwajin nukiliya ba tun bayan rugujewar Tarayyar Soviet a 1991, amma Kremlin yanzu ta nuna cewa za ta iya sake duba wannan matsayin idan Amurka ta fara.
kasashen Rasha da Amurka su ne manyan kasashen duniya masu karfin nukiliya, inda na farko ke da kusan makamin kare dangi 5,459, na biyu kuma ya kai kimanin makamin kare dangi 5,177.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran, China da Rasha sun tattauna gabanin taron Kwamitin Gwamnonin IAEA November 6, 2025 Shugabannin Iran Da Faransa Sun Yi Wata Tattaunawa Ta Wayar Tarho November 6, 2025 Najeriya Ta Sake Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar November 6, 2025 Gharibabadi: Kyakkyawar Alaka Tsakanin Iran Da Saudiyya Na Da Babban Tasiri Ga Yankin Da Ma Duniya November 6, 2025 Majalisar tsaron Sudan ba ta amince da batun tsagaita wuta ba tare da janyewar RSF ba November 6, 2025 Masu Sa Ido na Tarayyar Afirka: Zaben Tanzania Ya Keta Ka’idojin Demokradiyya November 6, 2025 An Kama ‘Yan Jarida 3 A Nijar Bisa Tuhumar Fitar Da Bayanai Na Hukuma November 5, 2025 Sudan Ta Sake Jaddada Tuhumar Kasar UAE Da Taimakon Rundunar RSF November 5, 2025 Shugaban Mali Ya Yi jawabi Akan Hana Shigar Da Man Futur Da Masu Ikirarin Jihadi Suke Yi November 5, 2025 Iran : bisa sharadi ne muka saki ‘yan Faransa daga gidan yari November 5, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci