Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da sabbin Kwamishinonin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) kafin fara taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya a fadar gwamnati da ke Abuja.

 

Sabbin Kwamishinonin INEC din da aka rantsar su ne Mallam Tukur Yusuf, mai wakiltar yankin Arewa maso Yamma, da Farfesa Sunday Aja, mai wakiltar Jihar Ebonyi.

 

Haka kuma, an rantsar da mambobi biyu na Hukumar Da’a ta Kasa (CCB).

 

Mambobin su ne Ikpeme Ndem, daga Jihar Cross River, da Mai Shari’a Buba Nyaure mai ritaya, daga Jihar Taraba.

 

Daga Bello Wakili.

 

 

 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya

A kokarin ta na ci gaba da kula da harkokin ilimi a yankin, Karamar Hukumar Birnin Kudu dake Jihar Jigawa ta kaddamar da aikin tantance malaman makaranta na B teach da kuma ma’aikatan lafiya na wato B health.

 

A jawabin sa wajen fara tantance malaman da ma’aikatan lafiyar, Shugaban karamar hukumar, Dr Muhammad Uba Builder, yace aikin tantancewar ya zama wajibi domin tabbatar da ma’aikata na gaskiya da kuma gano na bogi.

Yana mai cewar akwai rahotannin daya nuna wasu suna aiki 2 wasu kuma suna amfani da takardun bogi.

 

A don haka, yace duk wanda aka samu da hakan zai rasa aikin sa gami da kama shi don fuskantar hukunci.

 

Builder Muhammad Uba, yace an ware ranar asabar domin tantance malaman da kuma ma’aikatan lafiya domin tabbatar na gaskiya da adalci.

Yayi nuni da cewar, duk malamin da aka samu da takardun bogi, shakka babu za’a maye gurbin sa da wani.

 

Kazakika, Builder yaja hakalin su da su kasance masu tsoran Allah wajen gudanar da aikin su tare da ganin suna zuwa wuraren ayyukansu akan lokaci.

 

A jawabin sa, kansila mai gafaka na sashen ayyuka na karamar hukumar, Malam Haladu Maigari ya zayyana ayyukan raya kasa da shugaban karamar hukumar ya aiwatar karkashin jagorancin Builder Muhammad Uba.

Ya kuma baiwa malaman da ma’aikatan lafiyan shawarar fadin gaskiya na al’amurran su.

 

A jawaban su, jami’in shirin B Teach, Malam Nazifi Bala da kuma jami’in shirin B Health Malam mujitafa Ibrahim sun yabawa shugaban karamar hukumar bisa kokarin sa na rage zaman kashe wando ga matasan yankin karamar hukumar ta Birnin kudu.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Jinjinawa NAFDAC Bisa Matsayin Da Ta Taka A Hukumar Lafiya Ta Duniya
  • Hukumar Alhazai ta Jihar Kaduna Ta Bukaci Maniyyatan Aikin Hajjin 2026 Su Fara Biyan Kudaden Ajiya
  • INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • UADD Ta Yaba Wa Gidauniyar Tunawa Da Sardauna Kan Himma Da Kishin Kasa 
  • Shirin Iskar Gas Na CNG Abin A Yaba Wa Shugaba Tinubu Ne -Shugaban IPMAN Na Ƙasa
  • Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10
  • Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh
  • Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shari Share Falasdinawa Daga Kn Doron Kasa