Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Sabbin Kwamishinonin Hukumar INEC
Published: 12th, May 2025 GMT
Shugaba Bola Tinubu ya rantsar da sabbin Kwamishinonin Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) kafin fara taron Majalisar Zartaswa ta Tarayya a fadar gwamnati da ke Abuja.
Sabbin Kwamishinonin INEC din da aka rantsar su ne Mallam Tukur Yusuf, mai wakiltar yankin Arewa maso Yamma, da Farfesa Sunday Aja, mai wakiltar Jihar Ebonyi.
Haka kuma, an rantsar da mambobi biyu na Hukumar Da’a ta Kasa (CCB).
Mambobin su ne Ikpeme Ndem, daga Jihar Cross River, da Mai Shari’a Buba Nyaure mai ritaya, daga Jihar Taraba.
Daga Bello Wakili.
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
2027: Har Yanzu Ba Mu Saka Ranar Fara Sabunta Katin Zabe Ba — INEC
“Bisa ga al’adarta hukumar, INEC za ta sanar da ranar da za ta fara sabunta katunan masu zabe a lokacin da ya dace, wanda kuma za a raba cikakkun bayanai ta shafukan sada zumunta na hukuma,” in ji Oyekanmi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp