A sanarwar da mataimaki na musamman ga ministan kan harkar yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim ya fitar, ya bayyana cewa a jawabin sa na buɗe taron, ministan ya nuna jin daɗin sa kan yadda haɗin kai ke ƙaruwa a tsakanin manyan masu ruwa da tsaki a fannin yaɗa labarai a cikin gwamnatin.

 

Ya ce haɗin kan da daidaiton manufa sun ƙara inganta isar da saƙo da kuma fahimtar manufofin gwamnatin Tinubu.

 

Ministan ya yaba da yadda Ma’aikatar Yaɗa Labarai da Wayar da Kai take aiki tare da shugabannin hukumomin yaɗa labarai da kuma mataimakan shugaban ƙasa a ɓangaren watsa labarai da dabarun sadarwa.

 

Ya ce wannan haɗin gwiwa ya taimaka wajen tabbatar da cewa saƙonnin gwamnati suna da tsari, suna dogara da hujjoji, kuma suna amsa buƙatun jama’a.

 

Ya jaddada cewa wannan haɗin gwiwa ya taimaka wajen gina amincewar jama’a da kuma ƙara wayar da su game da tasirin Ajandar Sabunta Fata a ɓangarori masu muhimmanci kamar tattalin arziki, ababen more rayuwa, lafiya, ilimi da ayyukan jinƙai.

 

Ministan ya buƙaci masu ruwa da tsaki da su ci gaba da haɗa kai, tare da tabbatar da aiki cikin ƙwarewa, domin ƙara ƙarfafa wayar da jama’a kan nasarorin gwamnati a cikin gida da waje.

 

Ƙungiyar ta cimma matsaya kan a ƙara mayar da hankali wajen nuna nasarori a fannonin raya karkara, noma, gine-ginen ababen more rayuwa da kuma yaƙi da rashin tsaro, waɗanda su ne suka shafi rayuwar al’umma kai-tsaye.

 

Don ƙarfafa wannan yunƙuri, Idris ya buƙaci da a ci gaba da gudanar da tarurrukan tuntuɓa a jihohi da Babban Birnin Tarayya.

 

Ya ce tarurrukan tuntuɓar za su ba da damar tattaunawa kai-tsaye tsakanin wakilan gwamnati da jama’a, wanda hakan zai taimaka wajen gina amincewa, gaskiya da kuma gwamnatin da jama’a ke da tasiri a cikin ta.

 

Ƙungiyar ta bayyana aniyar ta ta ci gaba da yaɗa bayanai da za su ƙarfafa tattaunawar ƙasa, domin nuna tasirin ƙoƙarin gwamnati da kuma ƙarfafa haɗin kai da shiga cikin harkokin mulki.

 

Taron ya samu halartar shugabannin hukumomin yaɗa labarai da suka haɗa da Darakta Janar na NTA, Kwamared Abdulhamid Dembos; Darakta Janar na FRCN, Dakta Mohammed Bulama; Darakta Janar na Hukumar Wayar da Kai ta Ƙasa (NOA), Malam Lanre Issa-Onilu; Darakta Janar na VON, Malam Jibrin Baba Ndace; Darakta Janar na ARCON, Dakta Olalekan Fadolapo; da Sakataren Zartarwa na Hukumar Kula da Jaridu ta Ƙasa, Dakta Dili Ezegha.

 

Sauran su ne Manajan Darakta na NAN, Malam Ali M. Ali; Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Dabarun Sadarwa, Mista Bayo Onanuga; Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Yaɗa Labarai da Hulɗa da Jama’a, Mista Sunday Dare; da Mai ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Dabarun Bayanai, Mista Daniel Bwala.

 

Haka zalika, akwai masu taimaka wa Shugaban Ƙasa da suka haɗa da Tope Ajayi (kan Harkokin Labarai), Abdulaziz Abdulaziz (kan Jaridu), Mista Otega Ogra (kan Sadarwar Zamani), Linda Akhigbe (kan Sadarwa ta Dabaru), da kuma Ali Audu (kan Harkokin Jama’a).

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Darakta Janar na yaɗa labarai da Shugaban Ƙasa

এছাড়াও পড়ুন:

Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya  

Babban Hafsan Hafsoshin sojin Iran ya bayyana cewa; Martanin da Iran za ta mayar kan duk wani hari zai kasance murkushewa ne, kuma ba zata jira izinin kowa ba

Babban hafsan hafsan sojin kasar Iran ya gargadi makiya, yana mai cewa: Suna yi wa shahidai alkawari cewa: Za su ci gaba da bin tafarkinsu, kuma duk wani sabon harin wuce gona da iri kan Iran zai fuskanci azamar mayar da martani daban da na baya.

Babban hafsan hafsoshin sojin kasar ta Iran Manjo Janar Abdulrahim Mousavi ya jaddada matsayin wadanda suka yi shahada a safiyar yau Alhamis a yayin bikin tunawa da ranar shahidan Iraniyawa a hare-haren wuce gona da iri, yana mai daukar su a matsayin ginshikan tabbatar da tsaron kasar Iran a yau da gobe.

Manjo Janar Mousavi ya ce: “Taron tunawa da shahadar wadannan kananan yara, da kumajin al’ummar Iran – tun daga jarirai da yara zuwa malamai, masu ceto, ‘yan jarida, likitoci, shugabanni, da sauran kungiyoyi – ya zo daidai da ranar Arba’in na shugaban shahidai Jagoran al’umma Abu Abdullah al-Hussein {a.s} yana ci gaba da nuna al’adar wannan al’umma a cikin tarihin Ashura.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Dakarun Kare Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Jaddada Shirinsu Na Tunkarar Duk Wata Barazana August 7, 2025 Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Gaza Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa August 7, 2025 Human Rights Watch Ta Ce: Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Rusa Makarantu Fiye Da 500 A Gaza August 7, 2025 Amurka Ta Kwace Dalar Amurka Miliyon $584 Na Jami’ar California Saboda Gaza August 7, 2025 Mutanen Kasar Lebanon Suna Tsoron HKI Zata Shiga Kasar Daga Kasar Siriya August 7, 2025 Amurka ta Fara Janye Wasu Sojojinta Daga Wurare 3 A Kasashen Iraki Da Siriya August 7, 2025 Kasar Masar Ta Zama Mai Shiga Tsakanin Iran Da IAEA Da Kuma Amurka August 7, 2025 Araqchi: Ba a kayyade wani lokacin shiga wata sabuwar tattaunawa da Amurka ba August 7, 2025 Ghana: Ministocin tsaro da muhalli sun rasa rayukansu a hatsarin jirgi mai saukar ungulu August 7, 2025 Jamus: Shahararrun mutane da ‘yan jarida sun bukaci a daina baiwa Israila makamai August 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
  • Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi
  • PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027
  • Jirgin Shugaban Ƙasa Ya Laƙume Naira Biliyan 26.38 Cikin Wata 18 Ƙarƙashin Tinubu
  • Tallafin Kammala Makarantun Share Fagen Shiga Firamare Na Gwamnatin Kasar Sin Zai Amfani Mutane Kimanin Miliyan 12
  • Manjo Janar Mousawi: Martanin Iran Nan Gaba Zai Kasance Mafi Muni Kan Makiya  
  • Ranar Cutar Daji Ta 2025: Akwai Matakan Kariya Daga Kamuwa Da Cutar Kansa -Masana
  • Yadda sabbin takunkuman Trump za su shafi tattalin arziƙin duniya
  • Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi
  • Tinubu Ya Umurci A Bada Kulawar Lafiya Kyauta Ga Tsofaffin Ma’aikata Masu Karamin Fansho