Shugaba da mataimakinsa an tsige su ne kan zargin almundahana, rashin ɗa’a, rashin mayar da hankali kan aiki da kuma cin zarafin ofisoshinsu.

 

Kafin masa wannan naɗin riƙon kwarya, Wali ya kasance Kansila da ke wakiltar gundumar Tumfafi kuma shi ne ya kasance shugaban Kansiloli na ƙaramar hukumar.

 

Gwamnatin jihar Bauchi ce ta sanar da rasuwar nasa a ranar Lahadi ta cikin sanarwar manema labarai da kakakin gwamnan jihar, Mukhtar Gidado, ya fitar.

 

Da ya ke miƙa ta’aziyyasa ga iyalan mamacin, gwamna Bala Muhammad ya misalta marigayin a matsayin jajirtaccen mutumin da ya hidimta wa jama’a tare da bayar da gudunmawarsa wajen kawo cigaba a ƙaramar hukumar Shira da ma jihar Bauchi.

 

Gwamnan ya yi addu’ar Allah jiƙan mamacin ya gafarta masa kura-kuransa tare da neman Allah ya bai wa iyalai haƙurin juriya.

 

Rasuwar Wali dai na zuwa ne kwanaki 13 kacal a gudanar da zaɓen cire girbi na wanda zai bayar da dama a zaɓi sabon shugaba da mataimakinsa na karamar hukumar Shira.

 

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Mr. Ahmed Makama, ya shaida wa ‘yan jarida cewa dukkanin shirye-shiryen da suka dace na gudanar da zaɓen cike girbi a ranar 24 ga watan Mayun 2025 ya kammala.

 

BASIEC dai tun da farko ta gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi na jihar ne a watan Agustan 2024, inda aka zaɓi shugabanni da mataimakansu a dukkanin faɗin ƙananan hukumomi 20 da suke jihar Bauchi.

 

Makama ya bada tabbacin gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe mai cike da adalci.

 

Ya sanar da cewa kuɗin fom na kujerar shugaban ƙaramar hukumar Shira Naira miliyan 1, yayin da na mataimaki ya kasance Naira dubu ɗari biyar. Ya nemi dukkanin masu sha’awar tsayawa takarar da su fito su fara nema domin ƙofa a buɗe take.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hukumar Shira jihar Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

Tsohon Ministan Noma Audu Ogbeh ya rasu

Allah Ya yi wa tsohon Ministan Aikin Gona, Cif Audu Ogbeh rasuwa.

Iyalansa sun sanar cewa a safiyar Asabar Allah Ya yi masa cikawa, yana da shekara 78 a duniya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
  • Karamar Hukumar Birnin Kudu Ta Kaddamar Da Tantance Malamai Da Ma’aikatan Lafiya
  • EFCC ta kama ’yan damfara a ɗakin karatun Obasanjo 
  • Dole Ne Afrika Ta Mayar Da Hankali Wajen Amfana Da Damarmakin Da Ke Tekunanta – Ɗantsoho
  • Tsohon Shugaban PDP Audu Ogbeh Ya Rasu
  • Tsohon Ministan Noma Audu Ogbeh ya rasu
  • An Rantsar Da Sabbin Mataimaka Na Musamman A Karamar Hukumar Auyo
  • Obi ya ziyarci Bauchi, ya ba da tallafin N15m don inganta ilimi
  • PDP ta gargaɗi ’ya’yanta kan goyon bayan Tinubu a zaɓen 2027
  • Majalisar Kaduna Ta Amince da Dokokin Yawon Buɗe Ido da Zartar da Shari’a