Shugaba da mataimakinsa an tsige su ne kan zargin almundahana, rashin ɗa’a, rashin mayar da hankali kan aiki da kuma cin zarafin ofisoshinsu.

 

Kafin masa wannan naɗin riƙon kwarya, Wali ya kasance Kansila da ke wakiltar gundumar Tumfafi kuma shi ne ya kasance shugaban Kansiloli na ƙaramar hukumar.

 

Gwamnatin jihar Bauchi ce ta sanar da rasuwar nasa a ranar Lahadi ta cikin sanarwar manema labarai da kakakin gwamnan jihar, Mukhtar Gidado, ya fitar.

 

Da ya ke miƙa ta’aziyyasa ga iyalan mamacin, gwamna Bala Muhammad ya misalta marigayin a matsayin jajirtaccen mutumin da ya hidimta wa jama’a tare da bayar da gudunmawarsa wajen kawo cigaba a ƙaramar hukumar Shira da ma jihar Bauchi.

 

Gwamnan ya yi addu’ar Allah jiƙan mamacin ya gafarta masa kura-kuransa tare da neman Allah ya bai wa iyalai haƙurin juriya.

 

Rasuwar Wali dai na zuwa ne kwanaki 13 kacal a gudanar da zaɓen cire girbi na wanda zai bayar da dama a zaɓi sabon shugaba da mataimakinsa na karamar hukumar Shira.

 

Shugaban hukumar zaɓe mai zaman kanta ta jihar Bauchi (BASIEC), Mr. Ahmed Makama, ya shaida wa ‘yan jarida cewa dukkanin shirye-shiryen da suka dace na gudanar da zaɓen cike girbi a ranar 24 ga watan Mayun 2025 ya kammala.

 

BASIEC dai tun da farko ta gudanar da zaɓen shugabannin ƙananan hukumomi na jihar ne a watan Agustan 2024, inda aka zaɓi shugabanni da mataimakansu a dukkanin faɗin ƙananan hukumomi 20 da suke jihar Bauchi.

 

Makama ya bada tabbacin gudanar da sahihi kuma ingantaccen zaɓe mai cike da adalci.

 

Ya sanar da cewa kuɗin fom na kujerar shugaban ƙaramar hukumar Shira Naira miliyan 1, yayin da na mataimaki ya kasance Naira dubu ɗari biyar. Ya nemi dukkanin masu sha’awar tsayawa takarar da su fito su fara nema domin ƙofa a buɗe take.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: hukumar Shira jihar Bauchi

এছাড়াও পড়ুন:

Muhawarar da ta ɓarke kan saya wa Sarkin Kano motocin naira miliyan 670

Wata muhawara ta kunno kai a Jihar Kano da ma wajenta bayan gwamnatin jihar ta ba da umarni a cire naira miliyan 670 daga asusun ƙananan hukumomin jihar domin saye da kuma gyaran motocin Mai Martaba Sarkin Kano, Muhanmmadu Sanusi II.

Gwamnatin jihar ta bayyana cewa za a kashe naira miliyan 50 daga cikin kudin wajen gyaran wasu motoci biyu na sarkin, ragowar kuma za a sayo wasu sababbin motoci huɗu.

Shekara 10: Me ya sa Kofin Zakarun Turai ya gagari Barcelona? Za a kwaso ’yan Nijeriya 15,000 da ke gudun hijira a ƙetare

Ɓullar takardar da ke ɗauke da umarnin ta haifar da ce-ceku-ce, amma gwamnatin jihar ta hannun Kwamishinan Watsa Labarai, Ibrahim Waiya, ta kare matakin da cewa ba sabon abu ba ne a harkar gudanarwa, kuma ba a kanta farau ba.

Takardar, daga Ma’aikatar Kananan Hukumomi da Masarautu ta umarci kowacce daga cikin kananan hukumomi 44 da ke jihar ta fitar da kudi naira miliyan 15.2 domin sayen sabbin motoci hudu da kuma gyaran wasu biyu domin amfanin Majalisar Masarautar Kano.

A cikin takardar mai lamba MLG/INSP/LGD/166T/6 da kwanan wata 23/03/2025, wadda Daraktan Harkokin Kananan Hukumomi, Abubakar S. Dabo, ya sa hannu a madadin kwamishinan ma’aikatar, ya ce cewa za a cire kudaden ne kai-tsaye daga asusun hadakar gwamnatin jihar da kananan hukumomi, tana mai umartar kowane shugabannnin karamar hukuma ya tabbatar da an bi ka’ida wajen cika umarnin.

An aika kwafin takardar ga Babban Mai Binciken Kudaden Kananan Hukumomi na Jihar Kano, tare da bayyana cewa za a gudanar da kwangilar ne ta hanyar wani kamfani mai zaman kansa mai suna Sottom Synergy Resources Limited a kan kudi naira miliyan dari shida da saba’in.

Ta ce, “An umarce ni da in sanar cewa gwamnati ta sahale kowace karamar hukuma ta bayar da jimillar kudi naira 15,227,272.72 … domin gyara motoci biyu da kuma sayen wasu hudu ga Majalisar Masarautar Kano ta hanyar Sottom Synergy Resources Ltd.”

Ta kara da cewa kashe naira miliyan 25 daga cikin kudaden wajen gyaran wata mota kirar Rolls Royce (1969), da wata kirar Cadillac Limousine, ita ma a kan naira miliyan 25.

Ragowar kuɗin kuma, za a sayo sababbin motoci guda hudu — Toyota Land Cruiser BDR (2024) a kan naira miliyan 264; Toyota Prado (2024) a kan naira miliyan 156; Toyota Hilud (2024) a kan naira miliyan 98; da bas kirar Toyota Hiace (2024) a kan naira million 98.

Gwamnatin Kano ta sha suka

Wannan lamari ya jawo suka ga Gwamnatin Kano, kasancewarta mai da’awar cewa ta damu da talakawa.

Kanawa sun rika tambayar aihinin abin da gwamnatin ta fi bai wa muhimmanci, ganin yadda yankunan kananan hukumomi suke fama da rashi da kuma tabarbarewar ababen more rayuwa.

Wasu kuma na zargin cewa wani shiri ne na wawure kudaden jama’a.

Ahmed Isma’ila ya rubuta a shafinsa na sada zumunta cewa, “Me zai sa a dauki kudin wani a ba wani. To Allah Ya fallasa su.

Ya kamata mutane su fahimci irin shugabannin da suke da su a Kano.”

Hassan Falgore kuma ya rubuta cewa, “Yanayin rayuwar talaka ne ya kamata kowace gwamnati ta fi ba wa muhimmanci, ba wani mutum daya da zai iya yin hakan da kansa ba.”

Shi kuwa @UncleAnss ya rubuta a shafinsa na D cewa, “Baya ga yawan kudin da ake magana naira miliyan 670 na sayen motoci ga Masarautar Kano, akwai tursasawar da gwamnatin jihar ta yi wa kananan hukumomi su hada kudin.

“Idan wannan ne abin da Abba ke ganin ya fi masa muhimmanci, to ai sai ya yi amfani kudaden gwamnatin jiha ya saya wa masarautar. Amma sam babu adalci a tatsi kowace karamar hukumar naira miliyan 15 domin sayen motocin.

“Kananan hukumomin fa, fama suke da matsalolin lalatattun makarantu da asibitoci da rashin ruwan sha da karancin ababen more rayuwa. Amma wai kudadensu za a tatsa a yi wannan.”

Salihu Tanko Yakasai, tsohon kakakin tsohon gwamnan jihar, Abdullahi Ganduje, ya ce, “Kowacce daga kananan hukumomi 44 za ta bayar da naira miliyan 15.2 — jimilla miliyan 670 — da za a ba wa masarauta karkashin jagorancin sarkin talakawa SLS, domin saye da kuma gyaran motocin Mai Martaba Sarki daga Gwamnatin Jihar Kano, Gwamnatin Talakawa.”

An maimata irin na Kebbi

Wannan ya yi kama da dambarwar da ta barke a lokacin da Gwamnan Kebbi, Nasir Idris, ya saya wa sarakunan yanka hudu da ke jihar sabbin motoci kirar Toyota Land Cruiser a watan Oktoban shekarar 2024.

Sayen motocin ya jawo masa suka, inda ’yan gwagwarmaya da mutanen jihar suka bayyana matakin a matsayin rashin lissafi, duba da talauci da matsin rayuwa da suka dabaibaye al’ummar jihar.

Haka aka sake yi masa ca a lokacin da ya saya wa ’yan majalisar dokoki da kwamishinoni da manyan jami’an gwamnatin jihar motocin alfarma da kudaden gwamnati.

Masu sukan nasa sun bayyan cewa ko da manufarsa ta kwarai ce, domin daga darajar sarakunan, amma yawan kudaden da kuma lokacin daa aka yi bai dace ba, gwamma ya yi amfani da kudaden wajen magance matsaloli da ke ci wa talakawa tuwo a kwarya.

Ba kan Abba farau ba — Kwamishina

Kwamishinan Yada Labarai na Jihar Kano, Ibrahim Abdullahi Waiya, ya shaida mana cewa, “Wannan abu ne da aka saba, kowace gwamnati kan yi lokaci zuwa lokaci, saboda haka babu dalilin wannan gutsuri-tsoma.

“Masarauta a karkashin gwamnati take kuma gwamnati ke yi mata duk abubuwan da za ta bukata na gudanarwa da kudade ta hannun kananan hukumomi, ai ba sabon abu ba ne.

“Misali a lokacin Shekarau an saya wa hakimai motoci kimanin 54, a zamanin Ganduje ma an saya wa sababbin masarautun da ya kirkiro motoci, to mene ne sabo?”

Ya ce masarautu ba su da hanyar samun kudade shiga na kashin kansu, da gwamnati suka dogara, kuma “Wadannan motoci na aiki ne, ba na sarki na kashin kansa ba. Kayan masarauta ne, kayan gwamnati ne.”

Waiya ya kuma yi nuni ga dokar da Gwamnatin Abacha ta kafa, wadda ta tanadi ware kaso 3% na kudaden kananan hukumomi ga masarautun, wanda ya ce gwamantin Kano na amfani da dokar.

Game da dacewar kashe kudaden lura da halin matsin rayuwa da ake ciki, Waiya ya ce, “Babu kowane irin nau’in rashin lissafi.

Akasarin motocin da sarki ke amfani da su sun tsufa, shi ya sa aka ware wani kaso mai tsoka domin gyaran su.

Gwamnati ta yi kokari wajen ganin ba a yi almubazzaranci ba.” Ya kuma ya yi kira ga jama’a da su yi watsi da duk wata jitajita da ke kokarin bata sunan gwamnatin jihar ko siyasantar da lamarin.

Kololuwar rashin lissafi ne — Hadimin Ganduje

Sai dai duk da wannan bayanin, akwai masu sukan gwamnatin, irin su Salihu Tanko Yakasai, tsohon Daraktan Yada Labarai ga tsohon Gwamnan Kano, Abdullahi Ganduje, wanda ba sa ga-maciji da gwamnati mai ci.

Ya bayyana shirin saye da gyaran motocin da cewa, “kololuwar rashin imani da munafinci ne,” da rashin sanin abin da ya kamata.

“Lokacin da Ganduje ya kirkiro sababbin masarautu ya saya musu motoci, sun yi ta sukan sa, yau sai ga shi su ke yin hakan — ko ma abin ya fi muni — da sunan muhimman bukatun gudanarwa.

“Jihar Kano na fama da matsalar ruwan sha mafi muni a tarihinta, amma gwamnatin ta zabi ta saya wa sarki motoci.

“Wannan ba bukatar gaggawa ba ce, domin motocinsa suna aiki, lafiyarsu kalau,” in ji shi. Ya kuma kalubalanci dalilin cirar kudin daga aljihun kananan hukumomi maimakon aljihun gwamnatin jihar ko na masarautar.

“Kamata ya yi shi sarki, mai da’awar tausayin talakawa ya sa a yi amfani da kudaden wajen samar wa talakawan ruwan sha da sauran muhimman ababen more rayuwa. Wannan shi ne abin da ya dace da matsayinsa da yake nuna wa duniya.”

Karya doka ne — Dakta Hayatu

Wani babban malami a Sashen Kimiyyar Siyasa a Jami’ar Bayero ta Kano, (BUK) Dakta Aminu Hayatu, ya bayyana cewa umarnin cirar kudin daga asusun kananan hukumomi karya doka ne.

“Tunda doka ta haramta wa gwamnoni taba kudaden kananan hukumomi, to wannan umarni ya saba wa kundin tsarin mulki,” in ji shi.

Ya bayyana cewa hukuncin Kotun Koli ya tabbatar da ’yancin kananan hukumomi na gudanar da kudadensu, kuma, yi wa tsarin doka danwaken zagaye abu ne mai hadari da barazana ga tsarin dimokuradiyya.

Malamin ya ce, “Da kananan hukumomin ne a kankin kansu suka tattauna suka amince su yi hakan ta hanyar da ta dace, to da shi ke nan, amma wannan akwai alamar an turtasa musu.”

Lokacin bai dace ba — Farfesa Fagge

Tsohon Mataimakin Shugaban Kungiyar Masana Kimiyyar Siyasa ta Nijeriya, Farfesa Kamilu Sani Fage, ya bayyana umarnin a matsayin kutungwila ga kokarin tabbatar da ’yancin kananan hukumomi, kuma lokacin da aka yi abin bai dace ba.

“Ba za a iya cewa aiki ne na gaggawa ko mai muhimmanci ga talakawa ba. Kamata ya yi gwamnatin ta mayar da hankali kan abubuwan da za su amfani rayuwar talakawa, musamman a irin wannan lokaci da ake fama da matsin tattalin arziki.

“Bai dace ba a irin wannna lokaci. Kwanan nan fa Kotun Koli ta tabbatar da ’yancin cin gashin kai na kananan hukumomi. Wannan umarni ya ci karo da umarninta, kuma zai haifar da rudadi,” in ji Farfesa Fagge.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Shugaba Tinubu Ya Rantsar Da Sabbin Kwamishinonin Hukumar INEC
  • Hajjin 2025: Rukunin Farko Na Alhazan Jihar Kwara Ya Tashi Zuwa Kasa Mai Tsarki
  • Muna bayan Tinubu a Zaɓen 2027 — Patience Jonathan
  • Muhawarar da ta ɓarke kan saya wa Sarkin Kano motocin naira miliyan 670
  • Nijeriya Za Ta Karɓi Baƙuncin Taro Karo Na 4 Na Ƙananan Sana’oi Na Ƙungiyar AU
  • Rikicin Filato Ya Sa Makiyaya Yin Asarar Naira Miliyan 300 Cikin Wata 2
  • Noman 2025: Dole Ne Manoma Su Kiyaye Hasashen Hukumar NiMet
  • Hukumar Fina-Finai Ta Kasar Sin Ta Kulla Takardar Hada Hannu Da Hukumar Al’adu Ta Kasar Rasha
  • Hamas ta yi tir da Isra’ila kan rufe makarantun MDD