Bayan Cin Kamfanin META Tarar Dala Miliyan 220: Sun Yi Bazaranar Katse Kafofin Facebook, WhatsApp, Da Instagram A Nijeriya
Published: 10th, May 2025 GMT
BBC ta rawaito cewa, babban abin da ke damun kamfanin na Meta shi ne, yadda al’amarin ya shafi Hukumar Kare Bayanan Sirri ta Nijeriya (NDPC), wanda kamfanin ke zargin karya dokokin kare bayanan sirrin kasar.
Baya ga tarar Hukumar FCCPC, hukumar ta NDPC ta ci tarar kamfanin Meta dala miliyan 37.8, bisa zargin satar bayanan sirri, yayin da hukumar kula da tallace-tallace (ARCON) ta fitar da wani hukuncin daban na dala miliyan 37.
Daga cikin ka’idojin da ake da su, akwai bukatar kamfanin na Meta ya samu izini kafin tura bayanan ‘yan Nijeriya zuwa kasashen waje, yanayin da kamfanin ke ganin “ba abu ne mai yiwuwa ba.”
Hukumar NDPC ta kuma bai wa kamfanin Metar umarnin kirkira da kuma nuna abubuwan ilimantarwa a kan hadarin bayanan sirri ta kebabbiyar hanya a kan shafukan nata. Dole ne a samar da wadannan bidiyoyi tare da cibiyoyin da aka amince da su da kuma masu zaman kansu, sannan kuma dole ne su magance ayyukan sarrafa bayanai da rashin adalci.
Amma kamfanin na Meta ya ja baya a kan wadannan umarni, yana mai bayyana su a matsayin “wadanda ba sa aiki” tare da tabbatar da cewa; hukumomin Nijeriya sun gaza aiwatar da fassarar dokokin bayanan nasu yadda ya kamata.
Hukumar ta FCCPC ta ci gaba da cewa, tarar ta biyo bayan cikakken binciken da aka gudanar tsakanin watan Mayun 2021 zuwa Disambar 2023, tare da hadin gwiwar hukumar ta NDPC.
Har ila yau, kamar yadda rahotannin ke nunawa, akwai yiwuwar a wayi gari a ga dib, wadannan shafuka na Facebook da na Instagram sun daina aiki a Nijeriya, sakamakon wannan dimbin tara da kamfanin Metan ya koka a kai.
Idan za a iya tunawa, a bara ne hukumomin sanya ido na Nijeriya suka lafta wa kamfanin tara ta fiye da dala miliyan 290, bisa zargin kamfanin da karya wasu dokoki.
Kazalika, sai ga shi kuma kamfanin na Meta bai samu nasara a karar da ya shigar a wata babbar kotu da ke Abuja ba, inda ya kalubalanci matakin.
Har wa yau, kamfanin Meta ya rubuta a takardun shigar da karar da ya yi cewa; “Za a iya tursasa wa mai shigar da kara rufe ayyukan shafukansa na Facebook da Instagram a Nijeriya, domin rage hatsarin da zai iya fadawa a ciki, idan bai bi umarnin da ya kamata ya bi ba.”
Bugu da kari kuma, kamfanin Meta ne ke da manhajar WhatsApp, duk da cewa dai kamfanin bai ambaci shafin na WhatsApp din ba a jerin bayanan nasa.
Duk da cewa, babbar kotun ta bai wa kamfanin wa’din zuwa karshen watan Yuni, domin biyan wannan tara, amma da aka tuntubi kamfanin na Meta kan matakin da zai dauka, bai ce ko uffan ba.
Wadane Tasiri Manhajojin Facebook, Instagram Da WhatsApp Ke Da Su Kan ‘Yan Nijeriya
Ganin yadda ‘yan Nijeriya suka rumgumi wadannan shafuka ko manhajoji (Facebook, Instagram da WhatsApp), wasu suke ganin ba karamin nakasu za a samu ba, idan wannan kamfani na Meta ya janye daga Nijeriya.
Facebook ne shafin da al’umma suka fi amfani da shi a Nijeriya, domin kuwa miliyoyin al’ummar kasar ke amfani da shi a kowace rana. Wannan dalili, ya zama kusan na komai da ruwanka, kama daga abubuwan da suka shafi tallata hajoji, samun kowane labaru da dumi-duminsu da sauran makamantansu.
Har ila yau, shafin Facebook ya zama wata matattara ko dandali da ‘yan siyasa ke amfani da shi, musamman wajen yada farfagandar siyasa ko tallata manufofinsu ko kuma ayyuka da suka gudanar.
Kazalika, hatta kafofin yada labarai na amfani da wannan manhaja, wajen bayyana labaru da sauran shirye-shiryen da suke gudanarwa na yau da kullum.
A bangaren kasuwanci kuwa, wannan shafi ya shahara kwarai da gaske, domin kuwa kamfanoni da sauran ‘yan kasuwa; na amfani da shi, domin tallata hajojinsu iri daban-daban. Hatta masu shirya fina-finai, su ma ba a bar su a baya ba, domin kuwa sukan dan gutsuro wani abu daga ciki su nuna, don jan hankalin masu kallo.
Haka zalika, bangaren manhajar WhatsApp, ita ma na da nata matukar muhimmancin, musamman ta fuskar kasuwanci, sada zumunta, fadakarwa, ilimantarwa, tura wasu sakwanni masu muhimmanci da sauran makamantansu.
Wannan manhaja ta Whatsapp, kusan an fi amfani da ita wajen gudanar da kasuwanci, musamman ga daidaikun ‘yan kasuwa masu tasowa, har ma da wadanda wuyansu ya yi kauri.
Babban abin sha’awar shi ne, mata da dama daga gidajensu; na aiwatar da sana’o’i iri daban-daban, ta hanyar amfani da wannan manhaja, suna tallatawa ana kuma saya daga inda suke; ba tare da wata wahala ko kai-komo ba.
Haka nan, ga wadanda suke da ‘yan’uwa da sauran abokan arziki a kasashen ketare, wannan manhaja ta Whatsapp na matukar taimaka musu ta hanyar magana ko bidiyo kai tsaye a tsakaninsu, maimakon magudan kudaden da za su batar ta hanyar amfani da kiran waya.
Sannan uwa-uba, shafin Whatsapp; na da matukar muhimmanci wajen tura sakwannin karatuttuka, jaridu, labaru, hotuna, bidiyo da kuma sakon magana a kowane lokaci.
Haka zalika, ita ma manhajar Instagram na da nata muhimmancin, wajen tura sakwanni, sada zumunta, bidiyo, tallata hajoji da sauran abubuwa masu muhimmanci.
Koda-yake, akwai abubuwa da dama da ake ganin cewa; wadannan manhajoji sun taimaka wajen gurbacewarsu, wanda ko shakka babu, haka abin yake; musamman a bangaren gurbacewar tarbiyya da sauran abubuwan da suka shafi aikata ta’addanci da sauran makamantansu.
Duk da cewa, manhajojin sun taimaka wajen wayar da kan al’umma ta fuskoki daban-daban da suka hada addini, siyasa da sauran al’amuran rayuwa na yau da kullum, amma fa akwai abubuwa da yawa da suka yi tasiri a kan al’ummar wannan kasa ta hanyar amfani da manhajojin.
Kafin zuwan shafukan na Facebook, Instagram da Whatsapp, matasa da dama ba su da hanyoyin kale-kallen bidiyo da sauran hotunan batsa, barkatai. Amma bayan fitowarsu, yanzu za a iya cewa; lamarin ya riga ya zama jiki a tsakanin matasanmu.
Sannan, akwai sauran ayyukan rashin gaskiya da ta’addanci da matasa ke gani, maimakon su wa’antu; sai su buge da koya suna aikatawa. Akwai abubuwan da suka shafi damfara, aikewa da labarun karya da farfaganda, domin neman abun duniya ko wata daukaka a tsakanin al’umma.
Amma duk da wadannan abubuwa da ke faruwa a tsakanin manhajojin, muna iya cewa; amfaninsu ya fi rashin amfaninsu yawa a tsakanin al’ummar wannan kasa.
Shi yasa muke ganin janyewar kamfanin Meta daga Nijeriya, ba karamin koma-baya zai kawo mana ba. Amma wannan ya rage ga mahukunta, wajen dubawa tare da aiwatar da abin da ya dace, tun kafin alakar ta yi tsami.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: wannan manhaja
এছাড়াও পড়ুন:
Matsalar Tsaro: Yadda Dabarun Uba Sani Suka Mayar Da Tsoro Zuwa Kyakkyawar Fata A Jihar Kaduna
Bisa ga imanin da yake da shi ya bayyana cewa “Ba za ka iya samar da zaman lafiya da bama-bamai ba; sai dai ka gina shi da amana,” ya kaddamar da abin da yanzu ake kira ‘Samfurin Zaman Lafiya na Kaduna’.
Tsarin Hadin Gwiwa:r Gwamnatin Kaduna Da ofishin ONSA
A tsakiyar wannan sauyi akwai hadin gwiwa mai karfi a tsakanin Ofishin Mai Ba Shugaban Kasa Shawara Kan Tsaro (ONSA) da Gwamnatin Jihar Kaduna. Tare suka kafa kwamitin fasaha na hadin gwiwa wanda ya kunshi masu ruwa da tsaki, masana halayyar dan’Adam, da shugabannin kananan hukumomi, wannan tawaga ba ta zo da tankoki ko jiragen yaki ba, ta zo da tausayawa, tattaunawa da bayanai.
A babban aikinsu na farko, ’yan bindiga sun saki fursunoni 58 ba tare da an harba ko da harsashi guda daya ba. Sakamakon matakan gina amana, an sake ’yantar da fiye da mutane 80 a cikin makonni kadan da suka biyo baya. Yau, adadin ya haura fursunoni 500, duk an sako su lafiya lau, babban tarihi a tsawon fafutukar zaman lafiya ta Jihar Kaduna.
“Zaman lafiya da muke ginawa a Kaduna ya ta’allaka ne a kan tattaunawa, ba mulki da karfi ba,” in ji Gwamna Uba Sani.
Mahimmin Sauyi: Tattaunawa da Bukatu
Nasara ta fara bayyana ne a zagaye na biyu na zaman tattaunawa tsakanin kwamitin musamman na ONSA–Kaduna da shugabannin Kungiyoyin makamai. Wannan ba irin tattaunawar da aka saba ba ce, amma an gina ta ne a kan gaskiya da fahimtar juna.
‘Yan bindiga sun gabatar da sharuddan su na zaman lafiya sun kuma hada da;
1. Sake bude kasuwannin yankunan.
2. Samun damar ‘ya’yansu na zuwa makarantu
3. Birnin Gwari, Giwa da Kudancin Kaduna su samu kulawa a asibitoci.
Maimakon a yi watsi da wadannan bukatu a matsayin dabara kawai, gwamnati ta gane cewa su ne ainihin bukatun ’yan kasa da ke tsakanin neman rayuwa ko mika wuya. Gwamna Sani ya gaggauta amincewa a bude kasuwanni, tare da umartar a dawo da al’amuran rayuwa yadda suka saba a yankunan da abin ya shafa.
An samu Sakamakon nan take kuma a bayyane. Hanyoyin da suka zama tamkar matattu a Giwa da Birnin Gwari yanzu sun cika da ayyuka. Matafiya sun tabbatar da cewa mutum na iya wucewa ta wadannan yankuna “ko da da daddare” kuma ya isa lafiya, abin da ba zai yiwu a tunanin mutane ba shekaru biyu da suka gabata.
Limaman addini, Turji da Muhallin Al’amura
A gefe guda, wasu malaman addini karkashin jagorancin Sheikh Musa Yusuf (Asadus Sunnah) sun bayyana a bainar jama’a cewa sun gudanar da tarurruka a cikin dajin da sanannen shugaban ’yan fashi Bello Turji da wasu kwamandojinsa.
A cewar rahoton jaridar Banguard ta ranar 5 ga Agusta, 2025, malamin ya bayyana cewa “an saki fursunoni 32 kuma an mika makamai” bayan tattaunawar da aka yi da Turji.
Wannan rahoton yana da mahimmanci ga tsarin sulhun Kaduna domin yana nuna yadda masu ruwa da tsaki na cikin gida da hukumomin yankin ke kirkirar damar shimfida zaman lafiya a matakin jiha: sakin fursunoni, ba da izini ga manoma su koma gonakinsu, da takaitaccen sauke makamai wanda ke rage cutarwa kai tsaye a kasa.
Daga ’Yan Fashi zuwa Masu wanzar da Zaman Lafiya
Watakila shaidar da ta fi daukar hankali game da wannan sauyi ita ce bayyanar tsoffin ’yan fashi da suka tuba, yanzu sun zama masu kiyaye zaman lafiya a yankuna da suka taba tarwatsawa.
A Birnin Gwari, tsohon fitaccen dan fashi ‘Jan Bros’ yanzu yana sintiri a cikin dazukan da shi da mutanensa suka buya a da, yana tabbatar da cewa babu sababbin barazana.
A Kudu maso Gabashin Kaduna, wani sanannen mutum da ake kira ‘Yellow 1 Million’ ya zama mai sulhu kuma mai fafutukar wanzar da zaman lafiya, sannan yana hani da tashin hankali.
Wadannan sauye-sauyen na iya zama kamar abin mamaki, kuma su ne sahihan ayyukan shirin zaman lafiya da ya yi kokarin tattaunawa maimakon kawar da su gaba daya. Kamar yadda wani masani kan tsaro ya ce, “Kaduna ta yi abin da wasu jihohi ke mafarkin yi, ta mayar da tsoffin abokan gaba zuwa masu rike da ragamar zaman lafiya.”
Samfurin Zamani lafiya
Samfurin Zaman Lafiyar Kaduna ba gwaji ne na lokaci daya ba, tsari ne mai dorewa, mai ci gaba da sauyawa.
A makon jiya ma, kwamitin musamman ya sake gudanar da taro, a wannan karon tare da shugabannin ’yan fashi, dagatai daga Kajuru, Kauru, Kagarko da Kachia, tare da sarakunan gargajiya da shugabannin kananan hukumomi.
Taron, wanda Asadus Sunnah ya jagoranta, ya mayar da hankali kan karfafa abin da aka riga aka cimma da kuma hana komawar rikici.
Wannan ci gaba na tattaunawa, amincewa da sa ido, su ne suka bambanta hanyar Kaduna da wadancan yunkurin zaman lafiya na dan lokaci da aka yi a wasu sassan Nijeriya.
Farfado Da Tattalin Arziki: Zaman Lafiya Na Haifar Da Riba
Zaman lafiya ya fara haifar da sakamako a zahiri. Ayyukan noma a Giwa da Birnin Gwari da Kudancin Kaduna sun kai matakin da ya fi kowanne shekaru da suka gabata. Kasuwancin shanu, wanda matsalar tsoro ya dakile a da, ya sake farfadowa — yanzu manyan motoci 20 zuwa 30 na dauke da shanu suna bi ta hanyoyin da matsalar tsaro ya kange tsawon shekaru da dama.
Farfadowar kasuwanci ba wai ta tattalin arziki kadai ba ce; alama ce da ke nuna cewa an maido da mutunci da darajar al’umma.
“Duk wani kasuwa da aka sake bude nasara ce a kan tsoro,” in ji Gwamna Sani. “Duk wani yaro da ya koma makaranta shaida ce cewa tattaunawa na iya kayar da rashin bege.”
Samar Da Zaman Lafiya Ba Tare da Makami Ba A Yankunan Afrika
Sabon salon wannan aiki na Kaduna ya wuce iyakokin Nijeriya wajen tasiri. A fadin Afirka, al’ummomi sun dade suna gwagwarmaya da rashin nasarar amfani da karfin soja kadai. Daga shirin Afuwa na Yankin Neja Delta zuwa sulhun bayan kisan kare dangi a Rwanda, har zuwa tattaunawar da aka yi da rundunar Lord’s Resistance Army a Uganda — darasin daya ne: zaman lafiya na dindindin ba ya fitowa daga bakin bindiga ana gina shi ne ta hanyar shigar da kowa, tausayi da adalci.
Gwamna Uba Sani da tawagar ONSA sun daidaita wannan basira zuwa yanayin gida. Hanyar da suka bi ta nuna cewa ikon tattaunawa, idan an gina shi kan amincewa kuma doka ta tallafa, na iya dawo da zaman lafiya ko a wurare mafi tsauri.
Ka’idoji Uku Da Tushen Zaman Lafiyar Kaduna:
Ana samun zaman lafiya ne tare da tafiya da al’umma, ba wai a umarce su daga ofisoshin gwamnati ba. Sarakunan gargajiya, matasa, mata, da jami’an tsaro suna zama ne a tebur daya.
2. Shigar da Kowa cikin Tattalin Arziki: Farfado da kasuwanni, makarantu da asibitoci yana cire tushen da ke bai wa ’yan tawaye karfi.
3. Amincewa ta Hanya Mai Dorewa: Tattaunawa ta ci gaba, ba na lokaci-lokaci ba. Shigar ONSA yana tabbatar da rikon kwakwalwar hukuma da ci gaba a tsakanin hukumomi.
Wadannan ka’idojin sun yi daidai da abin da Babban Mashawarcin Shugaban Kasa Kan Harkar, Nuhu Ribadu, ya lura, wanda a wata hira da Channels TB a ranar 29 ga Yuli, 2025, ya yaba da hadin gwiwar dabarar rashin amfani da karfi kuma ya tabbatar da cewa “daruruwan fursunoni sun sami ‘yanci a fadin kasa ta hanyar ayyukan zaman lafiya da aka tsara tare.” Ribadu ya kuma bayyana cewa “A yanzu samun sahihan bayanan sirri, shigar al’umma, da dakatar da harkokin ta’addanci na dindindin” maimakon kawai kai farmaki da kama mutane.
Mataki na gaba
Ko da yake har yanzu akwai wasu barazanar lokaci-lokaci, tubalan zaman lafiya a Kaduna sun fi karfi fiye da da. Gwamna Uba Sani ya tsaya tsayin daka: “Ba mu ayyana nasara ba; muna ayyana sadaukarwa. Kowace rana da muka kiyaye wannan zaman lafiya rana ce da ta kara kusantar da mu ga dorewar kwanciyar hankali ga al’ummarmu.”
Kalmominsa yanzu suna yaduwa a cikin Birnin Gwari da sauran sassan Kudancin Kaduna da Giwa wadanda a da ake jin harbin bindiga, amma yanzu aka maye gurbinsu da dariyar yara da kuma walwalar kasuwanci.
Darasi Ga Nijeriya Da Afirca
Dabarun wanzar da Zaman Lafiyar Kaduna shi ne shaida wa mai rai cewa ko a cikin mafi hadarin yankin Nijeriya, zaman lafiya na iya samu ta hanyar tattaunawa kuma da hanyar ci gaban al’umma. Yana tabbatar da gaskiya mai sauki ba tare da tsorata dan’Adam ba.
Ta hanyar hadin gwiwa da Ofishin Mashawarcin Tsaron Kasa, Gwamna Uba Sani ya nuna cewa yakin neman zaman lafiya ba a kan dazuka ko hare-haren sama ake samun nasara ba, sai ta dabaru cikin zukatan da suke shirye su yafe, shugabanni kuma su shirya su saurari al’ummar da suke da karfin gwiwar sake ginuwa.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA