Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta bukaci Gwamnatin Jiha da kananan hukumomin jihar goma sha uku da su gaggauta bayar da kayayyakin tallafi ga wadanda guguwar iska ta shafa a fadin jihar.

Majalisar ta bayyana cewa hakan na da muhimmanci domin inganta rayuwar wadanda abin ya shafa da rage musu radadin halin da suke ciki.

Shugaban Majalisar, Dr. Danladi Jatau, ne ya bayyana hakan bayan Hon. Hudu A Hudu ya gabatar da batun a matsayin lamari mai muhimmanci ga jama’a, yayin zaman majalisar da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Shugaban majalisar ya ce abin jimami ne kwarai yadda guguwar iska ta lalata gidaje, makarantu, gine-gine da wasu muhimman kayayyaki da suka kai daruruwan miliyoyin Naira tare da jikkata mutane da dama.

“Ina godiya da wannan kuduri da Hon. Hudu A Hudu ya gabatar domin wannan iftila’in ya shafi mazabata kai tsaye, inda guguwar ruwan ta rushe dakin jarrabawa na GSS Bassa. Har ila yau, kusan dukkan mazabu a fadin jihar sun fuskanci wannan matsala kamar yadda yawancin ‘yan majalisa suka bayyana.

“Shawarar mu ita ce, dukkan shugabannin kananan hukumomi 13 na jihar su tattara bayanan gine-gine da mutanen da abin ya shafa tare da nemo hanyoyin da za a tallafa musu.

“Muna kira ga Mai Girma Gwamna da ya umurci hukumar bada agajin gaggawa ta jihar NASEMA da ta gaggauta daukar mataki ta hanyar raba kayayyakin tallafi ga wadanda abin ya shafa,” in ji shi.

Har ila yau, majalisar ta bayyana cewa guguwar ta bar iyalai da dama cikin kunci yayin da wasu ke kwance a asibitoci.

Tunda farko, Honarabul Hudu A Hudu, dan majalisa mai wakiltar Mazabar Awe Arewa, yayin da yake gabatar da batun, ya ce al’ummar Mahanga da ke mazabarsa da wasu yankuna sun rasa matsugunansu sakamakon guguwar.

“Wannan lamari ya shafi rayuwarsu ta yau da kullum matuka, inda gidaje fiye da 30 da mutane 500 suka samu matsala.

“Ina kira gare ku da ku goyi bayan wannan kuduri domin gwamnati ta zo ta taimaka wa mutanena.” Inji shi

 

Daga Aliyu Muraki

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Guguwa nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya bayyana cewa: Majalisar Shawarar Musulunci ta Iran ta sha bamban da majalisun da ke goyon bayan masu goyon baya masu laifi misalin masu kisan gilla a Gaza

Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya jaddada a yau Laraba cewa: Matsayin majalisar shawarar Musulunci ta Jamhuriyar Musulunci ta Iran ya bambanta da kasashen duniya, kuma ya sha bamban da majalisar da ke goyon bayan zalunci, nuna wariya, banbance-banbancen ra’ayi da masu aikata laifuka irin su kisan gilla a Gaza.

Yayin ganawarsa da mambobin majalisar shawarar Musulunci a ranar Laraba, Jagora ya yi la’akari da cewa: Majalisun dokokin duniya suna da kamanceceniya ta fuskar nauyi doka. Duk da haka, ya jaddada cewa ma’auni na farko don kimanta taro shine ainihin nauyin su, watau, “manufofin su, alkiblar motsi, da matsayi.” Wannan shi ne ya sanya matsayin Majalisar Shawarar Musulunci ke da shi a duniya. A dabi’ance, ci gaba da wanzuwar wannan matsayi mai mahimmanci da daraja yana buƙatar yanayi da wajibai waɗanda dole ne membobin su kiyaye.

A farkon jawabin nasa, Ayatullah Khamenei ya bayyana Eid al-Ghadir a matsayin biki mai girma ga daukacin al’ummar musulmin duniya, mai cike da ilmin addinin Musulunci. Ya taya al’ummar Iran masu girma da alfahari murnar zagayowar wannan rana mai albarka, da kuma maulidin Imam Hadi (a.s). Ya dauki matakin shari’a na majalisun dokoki a kasashe na duniya a matsayin mai sanar da doka. Ya kara da cewa, “Dokar ita ce ainihin sharadi na zamantakewar bil’adama, kuma dokokin da tunani na gamayya da zababbun wakilan jama’a suka samar sun fi samun karbuwa da kima.” Jagoran ya yi nuni da cewa ma’auni na gaskiya na majalisu ya bambanta da juna, sabanin nauyinsu na shari’a. Ya ce, “Mataki da kimar majalisar da ta ginu a kan addini, wadda ta kunshi mutane masu tsoron Allah, masu gaskiya, ta mai da hankali kan adalci, da goyon bayan wadanda aka zalunta, da fuskantar azzalumai”.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Ta Yi Barazanar Matakai Masu Tsauri Kan Masu Fasa Bututun Mai
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Iran tana da hakkin mayar da martani ga Isra’ila : Sanarwar Ma’aikatar harkokin waje
  • Cikakken Jerin Sunaye: Tinubu Ya Karrama ‘Yan Nijeriya 102 Don Bukin Ranar Dimokuradiyya Ta 2025
  • Guguwa ta hallaka mutum 6, ta jikkata 30 a Taraba
  • Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa
  • Dalilin da babu abin da gwamnatin NNPP ta taɓuka a Kano — APC
  • Jagora Ya Bambance Tsakanin Majalisun Dokokin Kasashe A Fagen Gudanar Da Ayyukan Kasa
  • Birnin Los Angeles Na Amurka Ya Rikice Yadda Ake Dauki Ba Dadi Tsakanin Al’ummar Jihar Da Jami’an Tsaro
  • Mokwa: Zulum ya kai ziyarar jaje Neja, ya bayar da tallafin N300m