Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta bukaci Gwamnatin Jiha da kananan hukumomin jihar goma sha uku da su gaggauta bayar da kayayyakin tallafi ga wadanda guguwar iska ta shafa a fadin jihar.

Majalisar ta bayyana cewa hakan na da muhimmanci domin inganta rayuwar wadanda abin ya shafa da rage musu radadin halin da suke ciki.

Shugaban Majalisar, Dr. Danladi Jatau, ne ya bayyana hakan bayan Hon. Hudu A Hudu ya gabatar da batun a matsayin lamari mai muhimmanci ga jama’a, yayin zaman majalisar da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Shugaban majalisar ya ce abin jimami ne kwarai yadda guguwar iska ta lalata gidaje, makarantu, gine-gine da wasu muhimman kayayyaki da suka kai daruruwan miliyoyin Naira tare da jikkata mutane da dama.

“Ina godiya da wannan kuduri da Hon. Hudu A Hudu ya gabatar domin wannan iftila’in ya shafi mazabata kai tsaye, inda guguwar ruwan ta rushe dakin jarrabawa na GSS Bassa. Har ila yau, kusan dukkan mazabu a fadin jihar sun fuskanci wannan matsala kamar yadda yawancin ‘yan majalisa suka bayyana.

“Shawarar mu ita ce, dukkan shugabannin kananan hukumomi 13 na jihar su tattara bayanan gine-gine da mutanen da abin ya shafa tare da nemo hanyoyin da za a tallafa musu.

“Muna kira ga Mai Girma Gwamna da ya umurci hukumar bada agajin gaggawa ta jihar NASEMA da ta gaggauta daukar mataki ta hanyar raba kayayyakin tallafi ga wadanda abin ya shafa,” in ji shi.

Har ila yau, majalisar ta bayyana cewa guguwar ta bar iyalai da dama cikin kunci yayin da wasu ke kwance a asibitoci.

Tunda farko, Honarabul Hudu A Hudu, dan majalisa mai wakiltar Mazabar Awe Arewa, yayin da yake gabatar da batun, ya ce al’ummar Mahanga da ke mazabarsa da wasu yankuna sun rasa matsugunansu sakamakon guguwar.

“Wannan lamari ya shafi rayuwarsu ta yau da kullum matuka, inda gidaje fiye da 30 da mutane 500 suka samu matsala.

“Ina kira gare ku da ku goyi bayan wannan kuduri domin gwamnati ta zo ta taimaka wa mutanena.” Inji shi

 

Daga Aliyu Muraki

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Guguwa nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara

Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta kama wasu mutane biyu da ake zargin ’yan kungiyar asiri ne tare da kwato musu wasu abubuwa na bata gari a Ilorin.

 

A cikin wata sanarwa da jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, Adetoun Ejinre-Adeyemi ya fitar, ya ce, ‘yan sandan da ke aiki bisa sahihiyar bayanan sirri daga majiyoyin tsaron al’umma, sun dauki wami mataki kan wani harin fashi da makami da ya afku a wani dakin kwanan dalibai da ke unguwar Eleko, Ilorin.

Sanarwar ta ce ba tare da bata lokaci ba jami’an ‘yan sanda da ‘yan banga, sun kai ga kama wasu maza biyu da ake zargi.

 

Ta ce wadanda ake zargin sun hada da Ishola Adeyemi, da Ismail Rafiu dukkansu na Ibadan, jihar Oyo.

 

A cewarsa yayin da ake yi musu tambayoyi na farko, wadanda ake zargin sun amsa cewa wani Qudus mai suna “Tiny”, memba ne na kungiyar Ido Cult Fraternity, ya gayyace su zuwa Ilorin don kawar da wani dan kungiyar asiri.

 

Ya yi nuni da cewa, a lokacin da harin nasu bai yi nasara ba, sai suka koma yin fashi a gidajen kwanan dalibai a yankin.

 

Ya yi bayanin cewa wadanda ake zargin, tare da baje kolin da aka kwato an mika su zuwa Sashen Yaki da Fashi, Sashen Binciken Laifukan Jiha (SCID), hedikwatar Jiha, don ci gaba da bincike da kuma gurfanar da su a gaban kotu.

 

REL/ALI MUHAMMAD RABIU

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Wani Bangaren Majalisar Dokokin Jihar Zamfara Ta Bukaci Gwamnatin Tarayya Da Ta Karbe Mulkin Jihar
  • Sin Ta Ware Yuan Miliyan 170 Domin Ayyukan Tallafi Ga Sassan Da Ambaliyar Ruwa Ta Shafa
  • Majalisar Kano Ta Karbi Kudirin Karamin Kasafin Kudi Na Shekarar 2025
  • ‘Yan Sanda Sun Kama Wasu Da Ake Zargin ‘Yan Kungiyar Asiri Ne A Jihar Kwara
  • Yajin Aikin NLC Da TUC Ya Gurgunta Ayyukan Gwamnati A Taraba.
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Karɓi Ƙarin Kasafin Kuɗi Na 2025
  • Inganta Harkokin Gwamnati: Oyebanji Ya Sauke Kwamishinoni 19
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Za a samu ambaliya da ruwa mai karfi a jihohi 15 a Arewa —NEMA
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas