Majalisar Dokokin Jihar Nasarawa ta bukaci Gwamnatin Jiha da kananan hukumomin jihar goma sha uku da su gaggauta bayar da kayayyakin tallafi ga wadanda guguwar iska ta shafa a fadin jihar.

Majalisar ta bayyana cewa hakan na da muhimmanci domin inganta rayuwar wadanda abin ya shafa da rage musu radadin halin da suke ciki.

Shugaban Majalisar, Dr. Danladi Jatau, ne ya bayyana hakan bayan Hon. Hudu A Hudu ya gabatar da batun a matsayin lamari mai muhimmanci ga jama’a, yayin zaman majalisar da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Shugaban majalisar ya ce abin jimami ne kwarai yadda guguwar iska ta lalata gidaje, makarantu, gine-gine da wasu muhimman kayayyaki da suka kai daruruwan miliyoyin Naira tare da jikkata mutane da dama.

“Ina godiya da wannan kuduri da Hon. Hudu A Hudu ya gabatar domin wannan iftila’in ya shafi mazabata kai tsaye, inda guguwar ruwan ta rushe dakin jarrabawa na GSS Bassa. Har ila yau, kusan dukkan mazabu a fadin jihar sun fuskanci wannan matsala kamar yadda yawancin ‘yan majalisa suka bayyana.

“Shawarar mu ita ce, dukkan shugabannin kananan hukumomi 13 na jihar su tattara bayanan gine-gine da mutanen da abin ya shafa tare da nemo hanyoyin da za a tallafa musu.

“Muna kira ga Mai Girma Gwamna da ya umurci hukumar bada agajin gaggawa ta jihar NASEMA da ta gaggauta daukar mataki ta hanyar raba kayayyakin tallafi ga wadanda abin ya shafa,” in ji shi.

Har ila yau, majalisar ta bayyana cewa guguwar ta bar iyalai da dama cikin kunci yayin da wasu ke kwance a asibitoci.

Tunda farko, Honarabul Hudu A Hudu, dan majalisa mai wakiltar Mazabar Awe Arewa, yayin da yake gabatar da batun, ya ce al’ummar Mahanga da ke mazabarsa da wasu yankuna sun rasa matsugunansu sakamakon guguwar.

“Wannan lamari ya shafi rayuwarsu ta yau da kullum matuka, inda gidaje fiye da 30 da mutane 500 suka samu matsala.

“Ina kira gare ku da ku goyi bayan wannan kuduri domin gwamnati ta zo ta taimaka wa mutanena.” Inji shi

 

Daga Aliyu Muraki

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Guguwa nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu

Yan Majalisar Tarayya daga yankin Kudu sun yi kira ga Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya yi wa jagoran ƙungiyar IPOB, Nnamdi Kanu, afuwa bayan da kotu ta yanke masa hukuncin ɗaurin rai da rai.

Kungiyar ’Yan Majalisar Wakilai daga yankin Kudu maso Gabas ta yi kira ga Shugaba Tinubu da ya yi amfani da ikon da kundin tsarin mulki ya ba shi, wajen yi wa Nnamdi Kanu afuwa wanda kotu ta same shi da laifin ta’addanci.

Alƙali James Omotosho na Babban Kotun Tarayya da ke Abuja ne ya yanke hukuncin, inda ya same shi da laifi a kan tuhumar da ake masa guda bakwai, sannan ya yanke masa hukuncin daurin rai da rai.

Tuni aka tura Nnamdi Kanu zuwa gidan yari a Jihar Sakkwato inda yake zaman waƙafi.

A cikin sanarwa bayan taron gaggawa da suka gudanar a Abuja, ’yan majalisar sun ce duk da cewa suna girmama kotu da tsarin shari’a, lamarin ya rikiɗe zuwa matsalar ƙasa mai tasiri ga rayuwar jama’a, tattalin arziki da tsaro.

Da yake karanta sanarwar, Hon. Iduma Igariwey ya ce yin afuwa zai taimaka wajen rage tashin hankali da dawo da zaman lafiya a yankin.

Sun lissafa dalilai guda huɗu da suka sa suka yi wannan kira.

Dalilan da suke bayyana su ne ƙaruwa da rashin tsaro da tashin hankali da ke da alaƙa da tsare Kanu; Wahalar rayuwa da tattalin arziki da jama’a ke fuskanta da kuma buƙatar shugabanci mai tausayawa wajen shawo kan matsalolin ƙasa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Majalisar Wakilai ta nemi gwamnati ta gaggauta dauko Jonathan daga Guinea Bissau
  • Gwamna Kefas Ya Bayyana Alhininsa Bisa Rasuwar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamna Radda Ya Sanya Hannu Kan Kasafin 2026 Ya Zama Doka
  • Jihar Jigawa Za Ta Rufe Karbar Kudaden Aikin Hajjin 2026 Ranar 24 Ga Watan Disamba
  • Tinubu ya aike wa Majalisar Dattawa sunayen jakadu
  • Aljeriya Ta Bukaci Kasashen Duniya Su Dauki Mataki Don Kawo Karshen Ta’asan HKI A Yankin Asiya Ta Kudu
  • Tinubu Ya Nuna Farin Cikinsa Bisa Bayyanar Daliban Kebbi, Ya Bukaci a Ceto Sauran
  • Yan Majalisar Kudu Sun Nemi Gafarar Tinubu Ga Nnamdi Kanu
  • Abbas Arakci Ya Yi Gargadi Akan Abin Zai Biyo Bayan Keta Dokokin Duniya Da “Isra’ila” Take Yi A Cikin Wannan Yankin