HausaTv:
2025-10-13@20:18:53 GMT

Rahoto : Sama da mutum miliyan 80 aka raba da muhallansu a fadin duniya

Published: 13th, May 2025 GMT

Sabbin alkaluma da cibiyar sanya ido kan yadda ake raba mutane da muhallansu da kuma hukumar kula da yan gudun hijira ta Norweian Refugee Council suka fitar sun bayyana cewa yanzu haka akwai sama da mutum miliyan 80 da aka raba da muhallansu a fadin duniya, kuma wannan ne mafi yawa da aka taba samu a tarihi.

Alkaluman da cibiyar sun nuna cewa yawan mutanen ya nunka fiye da sau biyu a cikin shekaru shida.

Rahoton ya ce kimanin mutum miliyan 74 ne rikice-rikice suka tursasa wa barin gidajensu.

Yakin Sudan kawai ya tarwatsa mutum sama da miliyan 11 – wanda shi ne mafi yawa da aka samu a kasa daya.

Sai kuma bala’o’in da sauyin yanayi ke haifarwa wadanda suka yi sanadin korar kimanin mutum miliyan 45 daga gidajensu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: mutum miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi wa Maryam Sanda afuwa, wadda aka yanke wa hukuncin kisa a shekarar 2020 bisa laifin kashe mijinta, Bilyaminu Bello, ɗan tsohon shugaban jam’iyyar PDP, Alhaji Haliru Bello.

Maryam,’ mai shekara 37, ta shafe shekaru shida da watanni takwas a gidan yarin Suleja kafin yi mata afuwa.

Talauci da tsangwama na hana yara mata karatu a Gombe — Kwamishina Gwamnan Kebbi ya bai wa sojoji kyautar motoci 6 da babura 30 don inganta tsaro

Rahotanni sun nuna cewar an yi mata afuwar ne bayan yin nadama da aikata kyakkyawan halaye.

Iyayen Maryam sun roƙi gwamnati da ta sake ta saboda ’ya’yanta biyu da ta ke da alhakin kula da su, tare da alƙawarin sauya halayenta.

Shugaba Tinubu, ya kuma yi wa wasu mutane afuwa da suka haɗa da Manjo Janar Mamman Vatsa, Ken Saro-Wiwa, da kuma Sir Herbert Macaulay.

Gaba ɗaya mutane 175 ne shugaban ya yi musu afuwa, ciki har da masu manyan laifuka, tsoffin fursunoni, da waɗanda suka yi kyakkyawan tuba.

Wannan shi ne karon farko da Shugaba Tinubu ya yi amfani da ikon yafe laifi don tausaya wa waɗanda suka aikata laifuka tun bayan hawansa mulki.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zaben Kamaru: Issa Tchiroma Bakary ya lashe yankunan da Biya ke da rinjaye
  • Shugaba Xi Jinping Ya Gabatar Da Shawarwari Hudu A Taron Kolin Mata Na Duniya
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Ko Kin San… Yadda Za Ki Gyara Kanki Da Kanki?
  • ’Yan sanda sun ceto mutum 10 daga hannun ’yan bindiga a Kaduna
  • Tinubu ya yi wa Maryam Sanda afuwa
  • Ranar Malamai Ta Duniya: Rashin Kulawa Ke Sa Malamai Barin Aiki
  • Sojoji Sun Kashe Ƴan Ta’adda 9, Sun Ƙwato Naira Miliyan 5 A Borno
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba