HausaTv:
2025-08-12@10:58:48 GMT

Rahoto : Sama da mutum miliyan 80 aka raba da muhallansu a fadin duniya

Published: 13th, May 2025 GMT

Sabbin alkaluma da cibiyar sanya ido kan yadda ake raba mutane da muhallansu da kuma hukumar kula da yan gudun hijira ta Norweian Refugee Council suka fitar sun bayyana cewa yanzu haka akwai sama da mutum miliyan 80 da aka raba da muhallansu a fadin duniya, kuma wannan ne mafi yawa da aka taba samu a tarihi.

Alkaluman da cibiyar sun nuna cewa yawan mutanen ya nunka fiye da sau biyu a cikin shekaru shida.

Rahoton ya ce kimanin mutum miliyan 74 ne rikice-rikice suka tursasa wa barin gidajensu.

Yakin Sudan kawai ya tarwatsa mutum sama da miliyan 11 – wanda shi ne mafi yawa da aka samu a kasa daya.

Sai kuma bala’o’in da sauyin yanayi ke haifarwa wadanda suka yi sanadin korar kimanin mutum miliyan 45 daga gidajensu.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: mutum miliyan

এছাড়াও পড়ুন:

Za a biya ma’aikata 445 garatitun sama da biliyan ɗaya a Kebbi

Gwamnan Jihar Kebbi, Nasir Idris, ya amince da biyan sama da biliyan ɗaya a matsayin kuɗin garatitu ga iyalan ma’aikatan gwamnati 445 da suka rasu.

Wannan biyan zai shafi tsoffin ma’aikatan jihar, ma’aikatan wucin-gadi, ma’aikatan ƙananan hukumomi, da malaman firamare.

Tinubu ya yi alhinin rasuwar tsohon shugaban PDP, Audu Ogbeh Kotu ta ɗaure wata mata shekara 3 a kan damfara 

Ana sa ran biyan kuɗin zai fara daga kan watan Disamba 2024 zuwa Maris ɗin 2025.

Gwamna Idri, ya ce gwamnatinsa za ta ci gaba da kula da walwalar ma’aikata da iyalansu, musamman waɗanda suka sadaukar da rayuwarsu wajen yi wa jihar hidima.

Ya ce biyan haƙƙoƙin ma’aikata ba wasa ba ne, kuma gwamnatinsa za ta yi tsayin daka wajen ganin an biya su a kan lokaci.

Wasu tsoffin ma’aikata sun yaba da wannan mataki, amma sun roƙi gwamnan da ya ci gaba da biyan sauran waɗanda ba su shiga jerin wannan sahun ba.

Sun ce akwai ɗimbin masu jiran haƙƙinsu, kuma idan ana biyan kowa a hankali, cikin lokaci kaɗan za a rage yawan masu jiran kuɗi.

Sun kuma buƙaci gwamnati ta duba tsarin fansho na jihar don inganta shi.

A cewarsu, yawancin masu karɓar fansho a Kebbi na cikin halin ƙunci saboda kuɗin da ake ba su ba ya wadatarwa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Naira Miliyan 50 Ga Mata Da Matasa
  • Sojoji sun hallaka ’yan ta’adda sama da 400 a Zamfara
  • Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu
  • An kashe mutum 24 an sace 144 a mako guda a Zamfara — Rahoto
  • ‘Yan Sandan Nasarawa Sun Kama Mutum Shida Da Laifin Fashi Da Makami Da Garkuwa Da Mutane
  • Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Katin Duba Sakamakon Jarabawa Kyauta Ga Ɗalibai
  • Sojoji sun kashe Kwamandan Boko Haram a Borno
  • Za a biya ma’aikata 445 garatutin sama da biliyan ɗaya a Kebbi
  • Za a biya ma’aikata 445 garatitun sama da biliyan ɗaya a Kebbi