Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
Published: 9th, May 2025 GMT
Farfesa Bamaiyi ya bayyana ainihin aikin IAR a matsayin habaka nau’ikan dimbin amfanin gona da kuma jure fari wadanda suka dace da bukatun noma a Nijeriya.
Ya bayyana masarar TELA a matsayin wata sabon salo da kirkira ta zamani a kimiyyance domin magance matsalolin da ake ci gaba da addabar amfanin gona, kamar kwari da canjin yanayi.
Aikin “Masarar TELA bai takaita kan inganci da wadatar abinci ba, har ma tana ba da kariya ga rayuwar manoma, da inganta noman da kuma magance ainihin illar da tsutsotsi ke haifarwa, gami da juriya a yayin fari,” in ji shi.
Shi ma da yake jawabi a yayin ziyarar, Farfesa Muyideen Oyekunle, wani masani a fannin tsirrai kuma daya daga cikin jagorori masu bincike kan aikin masarar Tela, ya gano yadda akre bunkasa wannan noma tun a farkon shekarar 2019.
Ya jaddada cewa bayan shekaru masana kimiyya, tantance hadarin, da kuma bin ka’ida, sun tabbatar da cewa masara ba ta da wata illa ga dan’Adam da muhalli.
“Bincikenmu ya tabbatar da cikakkiyar hujja akan haka, kuma ya yi daidai da ka’idojin aminci na duniya. Abubuwan da ke tattare da GMOs ba a ma fara bayyana shi ba.
TELA maize ta samu duk wani bincike da ya dace a ce an yi domin kare lafiyar halittu, kuma muna da yakinin cewa ba ta da wata illa ga lafiyar dan’Adam,” in ji Farfesa Oyekunle.
Wata kwararriya daga Cibiyar, Farfesa Memuma Abdulmalik, wadda ta tabbatar da hakan, ta bayyana cewa an samar da TELA maide ne domin noman masara mai inganci tare da kawar da duk wani nau’i na kwari da kuma fari.
A cewarta, wadannan gyare-gyaren ba sa canza tsarin abinci mai gina jiki ko amincin amfanin gona.
“Manufar inganta kwayoyin halittar TELA maize ita ce kare amfanin gona daga kamuwa da tsutsotsi dake addabai tsirrai da kuma sanya jurewar fari. Bayan wannan babu abu abu mai cutarwa ga masarar ko kuma haifar da wani hadari ga muhalli,” in ji ta.
A nasa bangaren, Farfesa Shehu Ado ya bayyana cewa daga cikin amfanin masarar TELA maize, yana matukar rage bukatar magungunan kashe kwari, wadanda galibi ke haifar da illa ga lafiya da muhalli fiye da amfanin gona.
Ya kara da cewa, “Ta hanyar rage dogaro ga magungunan noma masu cutarwa, masara ta TELA maize na ba da gudummawa ga tsarin noma mai dorewa kuma wanda ya dace da muhalli,” in ji shi.
Masanan sun kuma yi nuni da cewa, bayanai marasa tushe da ake yadawa game da GMOs ya haifar da koma-baya ga sabbin ayyukan noma da za su ceto rayuka a Nijeriya. Sun bukaci kafafen yada labarai da su rika gaggauta yada sahihan bayanai masu alaka da kimiyya.
Masarar TELA maize, wadda aka samar a karkashin gidauniyar TELA ta fasahar noma ta Afrika wato (AATF) tare da hadin gwiwar IAR da sauran masu ruwa da tsaki, na ci gaba da gudanar da gwaje-gwajen gonaki da yawa, kuma a halin yanzu an amince da noman a yankuna da dama a Nijeriya.
Yayin da ake ci gaba da muhawarar jama’a game da kayan amfanin gonar, kungiyar IAR ta sake jaddada aniyarta ta tabbatar da gaskiya, aminci, da samar da mafita wadanda ke karfafa wa manoma domin tabbatar da an samar da isasshen abinci a kasa.
Nijeriya na iya tanadin Naira Biliyan 900 duk shekara ta hanyar TELA Maize – IAR
Cibiyar Binciken Aikin Noma ta Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya ta bayyana cewa Nijeriya za ta iya yin tanadin sama da Naira biliyan 900 a duk shekara ta hanyar amfani da irin masarar TELA da aka samar ta hanyar kwayoyin halitta.
A cewar cibiyar, daga cikin irin gudunmawar da masarar TELA za ta bayar, akwai rage dogaro da magungunan kashe kwari da ake shigowa da su daga waje da ake amfani da su don yakar kwari masu lalata amfani kamar farin Dan go.
Babban daraktan hukumar ta IAR, Farfesa Ado Adamu Yusuf, ya bayyana irin gagarumar fa’idar da masara ta TELA ke samarwa a fannin tattalin arziki da noma, sannan ya jaddada bukatar a gaggauta gyara kura-kuran da jama’a ke yi game da amfanin gonakin fasahar kere-kere.
A cewarsa, Nijeriya na kashe sama da Naira biliyan 900 (kimanin Dalar Amurka miliyan 600) a duk shekara wajen shigo da magungunan kashe kwari don magance kwarin masara kamar farin Dan go, ban da kudin aikace-aikace.
Ya lura cewa bullo da masarar TELA mai jure kwari da jure fari (SAMMAZ 72T zuwa 75T) zai rage kashe kudaden da ake yi sosai, tare da habaka amfanin gona, da kuma adana ajiyar waje.
Muhimman fa’idodin masarar TELA da aka bayyana a yayin ziyarar sun haɗa da: jurewar kwari, jure fari, ƙara yawan amfanin gona da kuma samar da abinci.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Masara masarar TELA tabbatar da
এছাড়াও পড়ুন:
Majalisa ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a Bauchi
Majalisar Dokokin Bauchi ta buƙaci ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi a fadin jihar domin haɓaka ci gaba, inganta shugabanci, da kawo sauƙin gudanar da mulki.
Wannan na ƙunshe ne a wani ƙudiri da dan majalisar mai wakiltar mazabar Disina, Sale Hodi Jibir, ya gabatar a yayin zaman da Kakakin Majalisar, Abubakar Y. Sulaiman, ya jagoranta.
Gwamna ya yi wa iyalan ’yan wasan Kano da suka rasu a hatsari goma ta arziki Ministocin Ghana biyu sun rasu a hatsarin jirgin samaA cewar Jibir, ƙudurin yana dogaro ne da tanadin kundin tsarin mulki na 1999 wanda ya bai wa majalisun dokokin jihohi damar fara shirin ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi, matuƙar an cika wasu sharuɗa da suka haɗa da goyon bayan kashi biyu bisa uku na mambobin majalisa, da mincewar ƙananan hukumomin da abin ya shafa da kuma gudanar da zaɓen raba gardama.
Jibir ya bayyana cewa ƙirƙirar sabbin ƙananan hukumomi zai sauƙaƙa rarraba albarkatu cikin adalci da inganta shugabanci da gudanarwa a matakin ƙasa da ƙarfafa haɗin kan al’umma da ci gaban tattalin arziki.
Ya kuma ce yankuna da dama a Jihar Bauchi sun gabatar da buƙatar a ware musu ƙaramar hukuma, musamman duba da girman yankunansu, yawan al’umma, bambancin al’adu da kuma ƙalubalen gudanar da mulki.
Jibir ya buƙaci a kafa kwamitin wucin gadi na musamman domin tattarawa da tantance buƙatun al’umma, da tuntuɓar sarakunan gargajiya da shugabannin al’umma da nazarce-nazarce kan fadin ƙasa, da yawan jama’a da yanayin tattalin arziki na yankunan da ake neman a samar musu da ƙananan hukumomi.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, ƙudirin wanda ya samu goyon bayan wasu mambobin majalisar da suka buƙaci a gaggauta aiwatar da shi domin amfanin jama’a sun haɗa da Jamilu Umaru Dahiru da Musa Wakili Nakwada da Ibrahim Tanko Burra da Sa’idu Sulaiman Darazo da Dokta Nasiru Ahmed Ala.
A wani ɓangare na zaman, majalisar ta amince da rahoton kwamitinta na ma’aikata, dangane da ƙorafe-ƙorafen rashin biyan ’yan fansho da albashin ma’aikatan ƙananan hukumomi a faɗin jihar.