Iran Da Amurka Sun Fahinci Juna Sosai A Zagaye Na 4 A Tattaunawa A Mascat
Published: 12th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa tattaunawa ba kai tsaye ba tsakanin JMI da Amurka zagaye na hudu, yana tafiya kamar yadda ya dace. Kuma kasashen buyu sun kara fahintar ra’yin juna.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran da nakalto Aragchi yana fadar haka a wani hira da da ya gabatar bayan kammala zagaye na 4 na tattaunawar a jiya.
Ministan y ace bangarorin biyu sun tattauna babututuwan da suke da zurfi a cikin matsalolin da kasashen biyu suke son su warware, na farko gamsar da Amurka kan cewa shirin makamashin Nukliya na kasar Iran ban a tsaro bane. Da kuma maganar daukewa Iran takunkuman tattalin arzikin da aka dora mata.
Yace tattaunawar jiya yafi magana a kan bayanai masu zurfi kan wadanan matsaloli biyu da sannan babu batun magana ta sama sama.
Steve Witkoff mai bawa shugaban kasar Amurka shawara a kan al-amuran gabas ta tsakiya ne ya jagoranci tawagar Amurka kuma ministan harkokin wajen Omman ne mai kai kawo tsakanin bangarorin b iyu.
Tun ranar 12 ga watan Afrilu ne aka fara tattaunawa ba kai atsaye ba tsakanin Amurka da iran kan shirinta na makamashin nukliya ba kai tsaye ba. Bayan da Amurka ta rubutawa Iran wasika dangane da hakan.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce Kafa Hujja Da ‘Yan Tawaye Kan Iran Yankewar Kauna ce Ga Makiyanta
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Amfanin da fira ministan gwamnatin mamaya ya yi da ƙungiyar ta’addanci babbar alama ce ta cikakkiyar yanke ƙauna
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Matakin da fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya dauka na yi amfani da wata karkatacciyar kungiyar ta’addanci ta “MKO” wato kungiyar Munafukai wajen yada labaran karya game da shirin makamashin nukiliyar Iran, don tsoratar da al’ummar duniya kan Iran, wata babbar alama ce ta yanke kauna.
A sakon da ya wallafa shafinsa na X ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Yayin da ake ci gaba da zaman tattaunawa ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, ana ci gaba da fitar da karin “hotunan tauraron dan adam don yada tsoro da fargaba kan Shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya, inda ake murguda gaskiya zuwa karya.
Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu, a matsayinsa na mai neman kawo cikas da zagon kasa, ya yi amfani da dukkan tsoffi da sabbin ma’aikatan da ya dauka a matsayin wani bangare na manufofinsa na “kayyade ayyuka ga Trump.”
Araghchi ya ce: A wannan karon, Netanyahu ya koma yin amfani da bayin Saddam Hussain ‘yan kungiyar ta’addanci ta “MKO” da suka kasance kaskantattu su na shirya masa karairayi kan Shirin nukiliyar Iran, inda dogaro da rahotonnin kungiyar “MKO” babbar alama ce ta yanke ƙauna.