Zamfara Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Kula Da Aikin 2025 Domin Kyautata Jin Dadin Alhazan Jihar
Published: 12th, May 2025 GMT
Kwamitin ya kuma haɗa da Honarabul Sulaiman Adamu Gummi, Kwamishinan Al’amuran Addinai, wanda ke riƙe da muƙamin mataimakin shugaba, sai kuma Alhaji Habibu Balarabe, Babban Sakataren Hukumar Zakka, a matsayin sakatare.
Yayin ƙaddamar da kwamatin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ana sa ran tawagar za ta tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin nasara da walwala, aminci da jin daɗin alhazan Jihar Zamfara.
“Gwamnatin Jihar Zamfara, a madadin al’ummarmu, ta ba ku kwarin gwiwa sosai wajen ganin an aiwatar da kowane fanni na aikin Hajjin 2025 cikin inganci, mutunci, da gaskiya.
“Ina kira gare ku da ku ci gaba da ƙulla kyakkyawar alaƙa da Hukumar Alhazai ta Jihar Zamfara, da hukumomin Tarayyar da abin ya shafa, da kuma abokan hulɗar mu na Saudiyya, domin tabbatar da samun haɗin kai da warware matsalolin da suke faruwa a zahiri, dole ne ku rungumi hanyoyin tausayawa a cikin dukkan harkokin ku, da sanin cewa rayuwar ɗaruruwan ‘yan jihar na hannun ku.
“Gwamnatin jiha, Insha Allahu, za ta bayar da dukkan goyon bayan da suka dace domin ganin an sauke nauyin da aka ɗora muku yadda ya kamata, muna sa ran samun rahotannin ci gaban a kan lokaci, kuma a ƙarshen aikin hajjin za a fitar da cikakken rahoton da ya ƙunshi nasarori, ƙalubale, da shawarwarin manufofin gudanar da aikin hajji a nan gaba.
“Ku jakadu ne na Gwamnatin Jihar Zamfara da al’adunmu, da ɗabi’unmu, da mutuncin addininmu a duniya, don haka ina roƙon ku da ku nuna kyawawan halaye na tawali’u, haƙuri, ɗa’a, da sadaukarwa a duk tsawon wannan aiki, ku bar halinku ya zama abin koyi ga sauran mutane.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: Jihar Zamfara
এছাড়াও পড়ুন:
Tsaron makarantu: ’Yan Sanda da Shugabannin Makarantu sun tsara sabbin matakai a Gombe
Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe ta ƙaddamar da sabbin matakan ƙarfafa tsaro a makarantu bayan wani taron tattaunawa da aka gudanar tsakanin Kwamishinan ’Yan Sanda na jihar, Bello Yahaya, da shugabannin Ƙungiyar Malaman Sakandare reshen jihar.
An gudanar da taron ne a Hedikwatar Rundunar ’Yan Sanda ta Jihar Gombe, bisa umarnin Sufeton ’Yan Sanda na Ƙasa, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, na ƙara tsaurara tsaro a makarantu a faɗin ƙasar nan.
Kakakin rundunar, DSP Buhari Abdullahi ya bayyana cewa tattaunawar ta mayar da hankali kan duba tsarin tsaro na yanzu a makarantu, musamman waɗanda ke yankunan da ke da ƙalubale, tare da gano wuraren da ake buƙatar gaggawar gyara.
CP Bello Yahaya ya tabbatar da kudirin Rundunar ’Yan Sanda ta Najeriya na ci gaba da kare cibiyoyin ilimi, yana mai cewa makarantu dole ne su kasance wurare masu aminci domin koyo da koyarwa.
Ya jaddada muhimmancin yin nazarin tsaro a kai a kai, tsara matakan rigakafi, da kuma tabbatar da ci-gaba da haɗin gwiwa tsakanin shugabannin makarantu, Ma’aikatar Ilimi da hukumomin tsaro.
Kwamishinan ya bayyana cewa rundunar ta ƙara karfafa sintiri, sa ido, da kuma gaggawar amsa kira a yankunan makarantu da aka fi ganin haɗarin tsaro.
Ya kuma bukaci shugabannin makarantu su riƙa kasancewa a shirin tuntuɓar ofisoshin ’yan sanda mafi kusa, tare da hanzarta ba da rahoton duk wani abin da ya haifar da zargi.
Ya yaba wa shugabannin ANCOPSS bisa jajircewarsu wajen aiki tare da hukumar ’yan sanda domin ƙarfafa tsaro a makarantu.
A nasu ɓangaren, shugabannin ANCOPSS sun gode wa rundunar ’yan sanda bisa ƙoƙarin da take yi na tabbatar da lafiyar dalibai da malamai, tare da alƙawarin yin aiki kafada da kafaɗa da rundunar da Ma’aikatar Ilimi domin ƙarfafa duk tsare-tsaren tsaro a makarantun sakandare.
Rundunar ta kuma yi kira ga iyaye, malamai, shugabannin al’umma, da mazauna unguwanni da su kasance masu lura da faɗakarwa, tare da tallafa wa duk wani yunƙurin inganta tsaro a makarantu, domin kiyaye rayuwar ɗalibai nauyi ne da ya rataya a kan kowa.