Kwamitin ya kuma haɗa da Honarabul Sulaiman Adamu Gummi, Kwamishinan Al’amuran Addinai, wanda ke riƙe da muƙamin mataimakin shugaba, sai kuma Alhaji Habibu Balarabe, Babban Sakataren Hukumar Zakka, a matsayin sakatare.

 

Yayin ƙaddamar da kwamatin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa ana sa ran tawagar za ta tabbatar da gudanar da aikin Hajji cikin nasara da walwala, aminci da jin daɗin alhazan Jihar Zamfara.

 

“Gwamnatin Jihar Zamfara, a madadin al’ummarmu, ta ba ku kwarin gwiwa sosai wajen ganin an aiwatar da kowane fanni na aikin Hajjin 2025 cikin inganci, mutunci, da gaskiya.

 

“Ina kira gare ku da ku ci gaba da ƙulla kyakkyawar alaƙa da Hukumar Alhazai ta Jihar Zamfara, da hukumomin Tarayyar da abin ya shafa, da kuma abokan hulɗar mu na Saudiyya, domin tabbatar da samun haɗin kai da warware matsalolin da suke faruwa a zahiri, dole ne ku rungumi hanyoyin tausayawa a cikin dukkan harkokin ku, da sanin cewa rayuwar ɗaruruwan ‘yan jihar na hannun ku.

 

“Gwamnatin jiha, Insha Allahu, za ta bayar da dukkan goyon bayan da suka dace domin ganin an sauke nauyin da aka ɗora muku yadda ya kamata, muna sa ran samun rahotannin ci gaban a kan lokaci, kuma a ƙarshen aikin hajjin za a fitar da cikakken rahoton da ya ƙunshi nasarori, ƙalubale, da shawarwarin manufofin gudanar da aikin hajji a nan gaba.

 

“Ku jakadu ne na Gwamnatin Jihar Zamfara da al’adunmu, da ɗabi’unmu, da mutuncin addininmu a duniya, don haka ina roƙon ku da ku nuna kyawawan halaye na tawali’u, haƙuri, ɗa’a, da sadaukarwa a duk tsawon wannan aiki, ku bar halinku ya zama abin koyi ga sauran mutane.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Jihar Zamfara

এছাড়াও পড়ুন:

Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin

A ranar 23 ga wata, Kirsty Coventry, wacce ta karbi ragamar shugabancin kwamitin wasannin Olympics ta kasa da kasa kwanan nan, ta yi hira ta musamman da wani shirin gidan talabijin na CCTV mai lakabin “High-End Interview” a birnin Lausanne na kasar Switzerland. Wannan ita ce hira ta farko da ta yi da kafar yada labarai tun bayan da ta karbi ragamar shugabancin kwamitin wasannin Olympics na duniya.

Coventry ta ce ya zama wajibi a kiyaye kima da kuzarin wasannin motsa jiki na Olympics, tare da kara kiyaye su da kuma karfafa su. Ta ce, tana fatan yin mu’amala mai zurfi da dukkan masu ruwa da tsaki a watanni masu zuwa, tare da haduwa tare wajen tsara fasalin aiki na nan gaba da kuma yin aiki tare don tabbatar da yiwuwarsa a zahiri.

A halin da ake ciki kuma, ta ce, tana matukar fatan sake ziyartar kasar Sin nan da wasu watanni masu zuwa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai, makarantun Islamiyya
  • Gwamnatin Katsina ta amince da ƙidayar almajirai da makarantun Islamiyya
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mayaƙan Bello Turji Da Yawa A Zamfara
  • Gwamnatin Gombe za ta sayi takin N8.8bn don tallafa wa manoma
  • Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci
  • Gwamnan Nasarawa ya sanya wa gadar sama sunan Tinubu
  • Gwamnan Sakkwato Ya Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 Don Rage Matsalar Rashin Gida
  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
  • Sabuwar Shugabar Kwamitin Wasannin Olympics Na Duniya Na Fatan Sake Ziyartar Kasar Sin
  • Sojoji Sun Hallaka ‘Yan Ta’adda 600 Cikin Mako 3