Aminiya:
2025-08-11@10:25:31 GMT

JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025

Published: 9th, May 2025 GMT

Hukumar JAMB mai shirya jarrabawar neman shiga makarantun gaba da sakandire a Nijeriya, ta sanar da sakin sakamakon jarrabawar da ɗalibai suka zana a bana.

Wata sanarwa da shugaban hukumar, Farfesa Ishaq Oloyede ya fitar ranar Juma’a, ta ce an riƙe sakamakon ɗalibai 39,834 wanda a cikin wannan adadi tana bincike kan sakamakon ɗalibai 1,426.

An kama mutum 78 da makamai da kwayoyi a Kano Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare

A ranar Litinin ne JAMB ta fitar da alƙaluman sakamakon bana tana mai cewa yawancin ɗaliban da suka zauna jarabawar sun gaza samun maki 200 daga cikin maki 400.

JAMB ta ce ɗalibai miliyan 1.95 ne suka rubuta jarabawar daga cikin 2,030,862 da suka yi rajista, amma cikin wannan adadi, miliyan 1,534,654 ne wanda ya kai kaso 78 cikin 100 suka samu maki ƙasa da 200.

Alƙaluman sakamakon ya nuna cewa kashi 0.63 ne na ɗalibai ƙalilan da suka samu makin da ya haura 300, wanda a jimlace suka kai ɗalibai 12,414.

A matakin maki tsakanin 250 zuwa 299 kuma, an samu ɗalibai 73,441 yayin da ɗalibai 334,560 suka samu maki tsakanin 200 zuwa 249.

Rukunin da ya fi yawan ɗalibai shi ne na maki 160 zuwa 199, inda aka samu ɗalibai dubu 983,187 wato kashi sama da 50 cikin 100 ke nan.

Haka kuma, ɗalibai dubu 488,197 suka samu maki tsakanin 140 zuwa 159, sannan dubu 57,419 suka samu tsakanin 120 zuwa 139.

Ɗalibai 3,820 kuma sun samu maki tsakanin 100 zuwa 119, sannan ɗalibai dubu 2,031 sun gaza samun ko da maki 100.

 

 

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ɗalibai Jarrabawa

এছাড়াও পড়ুন:

Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina

A cewarsa, daga cikin waɗanda Allah ya yi wa rasuwa akwai mahaifiyar yaran wato Mariya Sani, ‘yar shekara 45 da kuma Mujahid Sani, ɗan shekaru 20, sai Zahariya Sani, ‘yar shekara 18.

Sauran sun haɗa da Hauwa Sani, ‘yar shekara 15 da Amira Sani, ‘yar shekara 3 da kuma Nura Sani, ɗan shekara 5.

Muhammad ya bayyana cewa yanzu haka akwai waɗanda suka samu raunuka, inda suke asibitin Katsina domin karɓar magunguna.

Mahaifin yaran ya bayyana irin kaɗuwar da ya yi lokacin da ya samu labarin faruwar wannan al’amari, wanda ya ce ya yi wa Allah godiya, su kuma da suka rasu Allah ya jikansu.

Yanzu haka dai ‘yan’uwa da abokan arziki na ci gaba da zuwa yi wa Malam Muhammadu ta’aziyyar rasuwar iyalansa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ana Neman Daukar Karin Matakin Kawar Da Shingayen Dake Hana ‘Ya’ya Mata Zuwa Makaranta A Zamfara
  • Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
  • Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin
  • Ma’aikatan shari’a 97 sun samu ƙarin girma a Borno
  • NDLEA Ta Kama Fasto Bisa Laifin Safarar Miyagun Kwayoyi A Legas 
  • Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027
  • Gwamnatin Jigawa Ta Raba Katin Duba Sakamakon Jarabawa Kyauta Ga Ɗalibai
  • Iran Ta Yi Maraba Da Sulhuntawa Tsakanin Armenia Da Azerbaijan
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Mayar Da Dalibai 184 Da Suka Zo Hutu Daga Cyprus
  • Bango Ya Kashe Mutum 6, Ya Raunata Wasu A Katsina