2027: Tsohon IGP ya fito takarar gwamna, ƙungiya ta mara masa baya a Nasarawa
Published: 9th, May 2025 GMT
Ƙungiyar Allied Group of Nasarawa Professionals (AGNP), wadda ta ƙunshi ’yan kasuwa da masu sana’o’in hannu, ta goyi bayan tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Mohammed Adamu, wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Gwamnan Jihar Nasarawa a 2027.
A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ofishinta da ke Keffi, AGNP ta ce matakin da Adamu ya ɗauka na tsayawa takara ya sanya al’ummar jihar cikin farin ciki.
“Wannan lokaci ne na kyawawan fata ga jiharmu,” in ji ƙungiyar.
Ƙungiyar ta yi alƙawarin tattara ƙuri’u aƙalla miliyan daya domin mara wa Adamu baya a zaɓen.
AGNP ta yaba wa Adamu bisa sauye-sauyen da ya kawo a lokacin da yake Sufeto Janar na ’Yan Sanda, musamman wajen samar da tsarin ‘yan sanda a cikin al’umma, amfani da leƙen asiri wajen yaƙar laifi da kuma fasahar zamani.
Ƙungiyar ta ce hakan na nuna irin cancantar da yake da ita wajen kawo ci gaba a Nasarawa.
“Waɗannan su ne irin manufofi masu amfani da jama’a ke buƙata a matakin jiha,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta samu sa hannun Daraktan ƙungiyar, Husseini Gana, da Sakataren Yaɗa Labarai, Saliu Hamzat.
Sun ce ƙungiyar ta yi nazari sosai kan masu neman takara kafin ta mara wa Adamu baya.
Sun kuma jaddada cewa Adamu ya taka rawar gani wajen hidimta wa jama’a, ayyukan jin-ƙai da kuma samar da ci gaba.
“Kodayake ba jam’iyya muke ba, amma muna da tabbacin cewa Mohammed Adamu shi ne ɗan takarar da ya fi cancanta ya gaji gwamnan yanzu,” in ji sanarwar.
Ƙungiyar ta ce ta riga ta fara shirin samun goyon bayan jama’a daga ƙauyuka da birane, inda ta tabbatar da cewa za ta samar wa Adamu ƙuri’a sama da miliyan ɗaya a lokacin zaɓen.
AGNP ta kuma buƙaci jam’iyyar APC mai mulki da ta bai wa Adamu tikitin takarar gwamnan jihar a 2027.
“Jagoranci da mulki al’amura ne na haɗin gwiwar kowa da kowa,” in ji Hamzat.
“Muna da yaƙinin cewa tare da Mohammed Adamu, Nasarawa za ta ga sabon salon ci gaba da ya dace.”
Tun da farko, Adamu ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan Jihar Nasarawa a ƙarƙashin jam’iyyar APC, a lokacin wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Lafia, babban birnin jihar.
Ya ce matakin ya biyo bayan kiraye-kirayen jama’a waɗanda ke da yaƙinin cewa yana da ƙwarewa da gogewa a fannin mulki.
Adamu ya yi alƙawarin kafa gwamnati mai sauraron jama’a da kula da buƙatunsu idan har aka zaɓe shi ya zama gwamnan jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ƙungiya Nasarawa takarar gwamna Tsohon Sufeto Janar Na Yan Sanda gwamnan jihar
এছাড়াও পড়ুন:
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa
A wani bangare na manufofinsu na kara yawan masu kada kuri’a, Alhaji Gamawa ya bayyana cewa, kungiyar mai zaman kanta za ta taimaka wa ‘yan kasa wajen karbar katin zabe, “Lokacin da INEC ta bude dandalin rajistar katin zabe, za mu taimaka musu wajen karbar katin zabe domin su bada gudunmawa a zabe da kuma amfani da ’yancinsu.
Gamawa ya kuma yi magana kan muhimmancin samun katin shaidar zama dan kasa, inda ya ce, yayin da tsaro ya yi karanci, abu ne mai sauki a laka wa dan Nijeriyar ba shi da katin dan kasa sharrin zama bako ko dan mamaya ko kuma sanya shi cikin masu garkuwa da mutane.
“Rashin katin shaidar zama dan kasa babbar matsala ce ga ’yan Nijeriya musamman wadanda ke zuwa yankin Kudancin kasar nan.
“Amotekun ko wasu kungiyoyin al’adu ne za su tare su, za a tattara su a ce su bayyana kansu da kuma inda suka fito, wasu ma suna zargin su ba ’yan Nijeriya ba ne.
“Wasu za su ce ‘yan Kaduna ne amma ina katin shaida? Babu wata shaida ko da ta lasisin tuki ce.”
Ya kuma bayyana cewa, kungiyarsa na shirin gudanar da wani taro na kwana daya domin karbar bakuncin Malamai akalla 200 a karamar hukumar Gamawa wadanda za su zo a wayar da kan jama’a game da gina kasa da hakkokin ‘yan kasa da ayyukansu sannan kuma su wayar da kan dalibai da ke karkashinsu.
A nasa jawabin, shugaban AIRLIN na Jihar Kaduna Alhaji Musa Muhammed ya ce, kungiyar ta dukufa wajen ganin ta kawo sauyi mai kyau da zai dawo da martaba da mutunta ‘yan Nijeriya.
Ya kara da cewa, AIRLIN gida ce ga kowa da kowa musamman wadanda suka yi imanin cewa akwai bukatar a sake farfado al’amuran da suka rushe a Nijeriya.
Taron dai ya samu halartar dukkan shugabannin kungiyar na jiha da na kananan hukumomin jihar, tare da ‘yan rakiyar shugaban na kasa da suka taho
daga Abuja.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp