Ƙungiyar Allied Group of Nasarawa Professionals (AGNP), wadda ta ƙunshi ’yan kasuwa da masu sana’o’in hannu, ta goyi bayan tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Mohammed Adamu, wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Gwamnan Jihar Nasarawa a 2027.

A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ofishinta da ke Keffi, AGNP ta ce matakin da Adamu ya ɗauka na tsayawa takara ya sanya al’ummar jihar cikin farin ciki.

’Yan sanda sun kama harsasai 500 a Filato Jami’an tsaro na ba da gudunmawar aikata miyagun laifuka a Nijeriya — Zulum

“Wannan lokaci ne na kyawawan fata ga jiharmu,” in ji ƙungiyar.

Ƙungiyar ta yi alƙawarin tattara ƙuri’u aƙalla miliyan daya domin mara wa Adamu baya a zaɓen.

AGNP ta yaba wa Adamu bisa sauye-sauyen da ya kawo a lokacin da yake Sufeto Janar na ’Yan Sanda, musamman wajen samar da tsarin ‘yan sanda a cikin al’umma, amfani da leƙen asiri wajen yaƙar laifi da kuma fasahar zamani.

Ƙungiyar ta ce hakan na nuna irin cancantar da yake da ita wajen kawo ci gaba a Nasarawa.

“Waɗannan su ne irin manufofi masu amfani da jama’a ke buƙata a matakin jiha,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta samu sa hannun Daraktan ƙungiyar, Husseini Gana, da Sakataren Yaɗa Labarai, Saliu Hamzat.

Sun ce ƙungiyar ta yi nazari sosai kan masu neman takara kafin ta mara wa Adamu baya.

Sun kuma jaddada cewa Adamu ya taka rawar gani wajen hidimta wa jama’a, ayyukan jin-ƙai da kuma samar da ci gaba.

“Kodayake ba jam’iyya muke ba, amma muna da tabbacin cewa Mohammed Adamu shi ne ɗan takarar da ya fi cancanta ya gaji gwamnan yanzu,” in ji sanarwar.

Ƙungiyar ta ce ta riga ta fara shirin samun goyon bayan jama’a daga ƙauyuka da birane, inda ta tabbatar da cewa za ta samar wa Adamu ƙuri’a sama da miliyan ɗaya a lokacin zaɓen.

AGNP ta kuma buƙaci jam’iyyar APC mai mulki da ta bai wa Adamu tikitin takarar gwamnan jihar a 2027.

“Jagoranci da mulki al’amura ne na haɗin gwiwar kowa da kowa,” in ji Hamzat.

“Muna da yaƙinin cewa tare da Mohammed Adamu, Nasarawa za ta ga sabon salon ci gaba da ya dace.”

Tun da farko, Adamu ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan Jihar Nasarawa a ƙarƙashin jam’iyyar APC, a lokacin wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Lafia, babban birnin jihar.

Ya ce matakin ya biyo bayan kiraye-kirayen jama’a waɗanda ke da yaƙinin cewa yana da ƙwarewa da gogewa a fannin mulki.

Adamu ya yi alƙawarin kafa gwamnati mai sauraron jama’a da kula da buƙatunsu idan har aka zaɓe shi ya zama gwamnan jihar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Ƙungiya Nasarawa takarar gwamna Tsohon Sufeto Janar Na Yan Sanda gwamnan jihar

এছাড়াও পড়ুন:

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi

Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.

An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.

Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.

An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.

Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.

Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu Ya Janye Dokar Ta-baci A Jihar Rivers
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • ‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
  • Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Ta Kama Bisa Kuskuren Safarar Ƙwayoyi
  • Tun Tinubu yana Gwamna ba abin da ya fi shahara da shi kamar tara haraji – Adebayo
  • ALGON ta karrama Gwamna Buni da lambar yabo kan kawo ci gaba a Yobe
  • An kama tsohon minista kan zargin kisan kai domin tsafi a Nijar
  • Arewa Ba Zata Ƙarɓi Mulki A 2027 Ba, Gwamna  Bago