2027: Tsohon IGP ya fito takarar gwamna, ƙungiya ta mara masa baya a Nasarawa
Published: 9th, May 2025 GMT
Ƙungiyar Allied Group of Nasarawa Professionals (AGNP), wadda ta ƙunshi ’yan kasuwa da masu sana’o’in hannu, ta goyi bayan tsohon Sufeto Janar na ’Yan Sanda, Mohammed Adamu, wanda ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar Gwamnan Jihar Nasarawa a 2027.
A wata sanarwa da ƙungiyar ta fitar a ofishinta da ke Keffi, AGNP ta ce matakin da Adamu ya ɗauka na tsayawa takara ya sanya al’ummar jihar cikin farin ciki.
“Wannan lokaci ne na kyawawan fata ga jiharmu,” in ji ƙungiyar.
Ƙungiyar ta yi alƙawarin tattara ƙuri’u aƙalla miliyan daya domin mara wa Adamu baya a zaɓen.
AGNP ta yaba wa Adamu bisa sauye-sauyen da ya kawo a lokacin da yake Sufeto Janar na ’Yan Sanda, musamman wajen samar da tsarin ‘yan sanda a cikin al’umma, amfani da leƙen asiri wajen yaƙar laifi da kuma fasahar zamani.
Ƙungiyar ta ce hakan na nuna irin cancantar da yake da ita wajen kawo ci gaba a Nasarawa.
“Waɗannan su ne irin manufofi masu amfani da jama’a ke buƙata a matakin jiha,” in ji sanarwar.
Sanarwar ta samu sa hannun Daraktan ƙungiyar, Husseini Gana, da Sakataren Yaɗa Labarai, Saliu Hamzat.
Sun ce ƙungiyar ta yi nazari sosai kan masu neman takara kafin ta mara wa Adamu baya.
Sun kuma jaddada cewa Adamu ya taka rawar gani wajen hidimta wa jama’a, ayyukan jin-ƙai da kuma samar da ci gaba.
“Kodayake ba jam’iyya muke ba, amma muna da tabbacin cewa Mohammed Adamu shi ne ɗan takarar da ya fi cancanta ya gaji gwamnan yanzu,” in ji sanarwar.
Ƙungiyar ta ce ta riga ta fara shirin samun goyon bayan jama’a daga ƙauyuka da birane, inda ta tabbatar da cewa za ta samar wa Adamu ƙuri’a sama da miliyan ɗaya a lokacin zaɓen.
AGNP ta kuma buƙaci jam’iyyar APC mai mulki da ta bai wa Adamu tikitin takarar gwamnan jihar a 2027.
“Jagoranci da mulki al’amura ne na haɗin gwiwar kowa da kowa,” in ji Hamzat.
“Muna da yaƙinin cewa tare da Mohammed Adamu, Nasarawa za ta ga sabon salon ci gaba da ya dace.”
Tun da farko, Adamu ya bayyana aniyarsa ta tsayawa takarar gwamnan Jihar Nasarawa a ƙarƙashin jam’iyyar APC, a lokacin wani taro da ya yi da shugabannin jam’iyyar a Lafia, babban birnin jihar.
Ya ce matakin ya biyo bayan kiraye-kirayen jama’a waɗanda ke da yaƙinin cewa yana da ƙwarewa da gogewa a fannin mulki.
Adamu ya yi alƙawarin kafa gwamnati mai sauraron jama’a da kula da buƙatunsu idan har aka zaɓe shi ya zama gwamnan jihar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Ƙungiya Nasarawa takarar gwamna Tsohon Sufeto Janar Na Yan Sanda gwamnan jihar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
Daga Usman Muhammad Zaria
Majalisar Zartarwa ta Jihar Jigawa ta amince da bayar da rancen kudi ga hukumar gidaje ta jihar domin gina gidaje 52 a Dutse.
A cikin wata sanarwa da kwamishinan yada labarai na jihar, Alhaji Sagir Musa Ahmed ya fitar, ya bayyana cewa gidajen za su kunshi masu dakuna uku da kuma dakuna biyu kowanne.
Ya ce aikin zai kasance a gaban tsohuwar unguwar majalisar dokoki, kusa da hanyar wucewa ta Jami’ar Tarayya da je Dutse, a matsayin wani shiri na asusun gina gidaje karkashin ma’aikatar gidaje, ci gaban birane da tsare-tsaren yankuna, ta hannun hukumar gidaje ta jihar.
Alhaji Sagir ya bayyana cewa, wannan mataki na nuna kudirin gwamnati wajen magance matsalar gidaje a babban birnin jihar, kara habaka ci gaban birane, tare da samar da ayyukan yi ga matasan jihar.
Ya ce an tsara wannan asusu ne domin tabbatar da dorewa, ta yadda za a ci gaba da zuba jari a ayyukan samar da gidaje masu araha a fadin jihar.
Haka kuma ya kara da cewa, gwamnatin jihar tana da kudirin ci gaba da inganta rayuwar al’ummarta, ta hanyar ayyuka masu amfani da jama’a, da ke inganta walwala, karfafa tattalin arziki, da tallafa wa matasa.
Kwamishinan ya kuma bayyana cewa, majalisar ta amince da bayar da kwangilar gyara da inganta gidan baki guda biyu (Malam Adamu Chiroma House da kuma Senator Francis Ella House) da ke cikin G9 Quarters a Dutse, da kudin sama da naira miliyan 219.7.
Ya ce aikin zai haɗa da cikakken gyara da inganta gine-ginen, gyaran hanyoyin ruwa da kuma girka tankokin ruwa ga kowanne daga cikin gidajen biyu.
Ya ce hakan na da nufin tabbatar da wadataccen ruwan sha mai dorewa a wuraren.
Alhaji Sagir Musa Ahmed ya kara da cewa, amincewar da aka yi da wannan kwangila na nuna jajircewar gwamnatin jihar wajen kula da dukiyar jama’a da kuma tabbatar da cewa gine-ginen gwamnati suna cikin yanayi mai kyau da nagarta.