Yadda rashin wutar lantarki ta gurguna harkar lafiya a Najeriya
Published: 9th, May 2025 GMT
Matsalar wutar lantarki a asibitoci a Najeriya ta jefa marasa lafiya cikin halin ni-’yasu, lamarin da ke kara ta’azzara halin da majinyata ke ciki, har ta kai ga asarar rayuwa.
Rashin wuta ya yi sanadin mutuwar jariri a cikin wata mai juna biyu, wata ta yi awa 15 tana jiran a yi mata tiyatan haihuwa, wata kuma ta mutu sakamakon dauke wuta a yayin da ake tsada da yi wa mata tiyata, a Asibitin Jummai Babangida Aliyu, da ke jihar Neja.
’Yan uwa sun shaida wa wakilinmu cewa an shafe sama da kwana uku a jere babu wutar lantarki a asibitin gwamnatin, a yayin da rashin wuta da yanayi na tsananin zafi ya tilasta wa ’yan uwan majinyata amfani da fankoki masu amfani da caji domin samun iska a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ke Jihar kano.
Bincikine wakilanmu ya gano matsalar lantarkin na kawo tsaiko ga gudanar a tiyata da ayyukan karbar haihuwa da awon masu juna biyu a asibitoci.
Masan sun ƙalubalanci sojoji kan maharan ƙasashen waje NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso GabasMajinyata a asibitocin da muka ziyarta sun bayyana cewa rashin wutar ta sa ana dage lokacin da aka shirya yi musu tiyata baya ga kawo tsaiko ga sauran nau’ikan aikin kula da lafiya.
Wannan matsala ta shafi asibitocin koyarwa, inda yawan kudin wutar da ake kamfananonin rarraba lantarki ke bin su ya yi yi musu katutu. Shugabannin asibitocin koyarwar sun bayyana cewa sun yi kokari biyan bashin, amma duk da haka sai sun kara neman wasu kudaden domin samar wa wata hanyar samun lantarki, saboda matsalar rashin samun wutar gwamnati da ta ki ci ta ki cinyewa.
A cikin wannan hali, a watan Fabrairu Ministan Lantarki, Adebayo Adelabu, ya sanar da shirin sake kara kudin wutar, bisa hujjar cewa gwamnati ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin lantarki ba.
‘Dauke wuta ana cikin yi wa matata tiyata ya yi ajalinta’
A kwanan baya ne wani magidanci a Jihar Neja, Umar B. Shehu ya wallafa a shafinsa na Facebook, yadda dauke wutar da aka yi a yayin da ake tsaka da yi wa matsarsa tiyatar kabar ciki, ya yi sanadiyyar mutuwarta a Babban Asibitin Jummai Babangida da ke garin Minna, hedikwatar jihar.
Malam Umar ya ce, bayan minit biyar da fara yi wa matarsa, Ummi Yusuf Makusidi tiyata, “NEPA suka dauke wuta kuma babu mai a injin janareton bangaren aikin tiyatan da ke Asibitin Jummai Babangida Aliyu.
“Bayan minti biyar aka kawo mai, bayan an zuba kuma sai janareto ya ki tashi, sai da aka nemo makanike. Duk matata tana cikin dakin tiyata, wata mai aikin jinya ta ce kada in damu an ci gaba da aikin ba tare da wutar lantarki ba, suna amfani da abin haskawa — cocila — kamar yadda suka saba.
“Bayan da makaniken ya zo kuma, akwai abubuwan da dole sai ya je ya sayo a unguwar Ogbomosho da ke Minna. Duk dai matata tana cikin dakin tiyata.
“Bayan awa daya aka dawo da wuta, amma makaniken yana kan gyaran janareto. A haka a ci gaba da aikin tiyata. Aikin da bai wuci ya dauki awa daya da rabi ba, tun karfe hudu na yamma sai da ya kai karfe 7 da dare.”
A lokacin da wakilinmu ya ziyarci asibitin da misalin karfe biyar na yamma ranar Asabar, ya lura babu wutar lantarki a daukacin asibitin. ’Yan uwan ajinyata da ke asibitin sun shaida masa cewa kwanansu uku babu wutar lantarki a asibitin, likitoci sun tura wasu, musmman mata masu juna biyu da ke nakuda zuwa asibitocin kudi.
Awa 15 muna jiran tiyataWani magidanci mai suna Ali Isah, wanda ya shaida mana yadda ’yarsa ta shafe awa 15 tana jiran a yi mata tiyata bayan an biya kudin aikin a asibitin.
Ya ce, “an kawo nan ne da misalin karfe 3 na dare za ta haihu. Nas ta shaida mana cewa aikin CS za a yi mata, amma ga shi yanzu karfe biyar na yamma, ba a yi aikin ba, kuma mun biya N40,000 kudin aikin.
“Dan uwana ya ba mu shawara mu je asibitin kudi, amma mun riga mun biya kudi a nan asitin na Jummal Babangida.”
Dan uwan wani mara lafiya a asibitin ya ce, “da ya mutu a cikin wata mai juna biyu ranar Juma’a bayan sun shafa awanni suna jiran a yi mata aiki, ba a yi ba. Dalilin da suka bayar shi ne rashin wutar lantarki da ruwa.
“Mijin matar da kansa ya sayo ruwa amma suka ce babu wuta. Kafin a tura matar zuwa Asibitin MI Wushishi, dan ya riga ya mutu. Yanzu kwana uku ke nan babu wuta a nan asibitin,” in ji shi.
Laifin lalacewar tiransufoma ne — Gwamnatin NejaMun tuntubi Gwamnatin Jihar Neja inda Kwamishinan Kula da Lafiya a Mataki mai Zurfi, Bello Tukur ya musanta cewa rashin wutar lantarki na kawo cikas wajen gudanar da ayyuka a asibitin.
Ya ce, “Ba gaskiya ba ne, tiransufoma ne ya samu matsala, kuma an kira Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na AEDC su zo su duba, bayan sun duba suka ce dole sai Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya zo ya duba layin wutar.
“Mun riga mun biya kudin da ake bukata kuma yanzu haka suna aikin. Muhimman sassan asibitin kamar bangaren haifhuwa da dakin haihuwa da bangaren masu jego suna da janareto.
“Ba za a iya kunna babban janareton da ke iya daukar asibitin gaba daya ba, saboda dole sai wutar ta bi ta babban layin, wanda shi ne ya lalace. Yanzu haka ma’aikatan AEDC da TCN na aikin gaya domin ganin ya ci gaba da aiki a asibitin.
Majinyata na zuwa da fankokinasu Asibitin Aminu KanoWani mara lafiya a Asibitin Koyarwa na Aminu Kano da ya bayyana sunansa a matsayin Malam Umar, ya ce, “Marasa lafiya na amfani fankokinsu masu daukar caji a sibitin, saboda zafi, idan aka dauke wuta.
“Babu wutar sola, shi ya sa aka dauki lokaci idan aka dauke wuta kafina dawo da ita ko a kunna janareto.”
Wakilimu ya lura cewa an samar da wutar lantar mai amfani da hasken rana a dakin kula da lafiya na gaggaaw da wadanda suka yi hadari.
Dalilin da muka ninka kudin aiki — Asibitin AKTH
Shugaban Kwamitin Shawarwari na Asibitin, Farfesa Muhammad Abba Suwaid, wanda ya yi magana a madadin shugaban asibitin, Farfesa Abdurrahman Abba Sheshe, ya ce asibitin na shan man fetur na Naira miliyan 30 zuwa miliyan 100 a kowane wata, amma ba zai iya biyan abin da ya fi kashi 30% na kudin ba, shi ya sa a yanzu haka ake bin su bashi da ya kai naira miliyan 700 na kudin wuta.
“Wannan ya shafi yadda ake kula da majinyata, saboda dole ta sa asibitin kara kucin aiki da kashi 100% domin mu iya biyan kudin, amma hakan ma ya gagar.
“Hukumar gudanarwar asibitin na shirni sanya wuta mai amfani da hasken rana a wurare masu muhimmanci da suka hada da dakunan tiyata da wurin jinya mai tsanani da wasu dakunan majinyata.”
Jinkirin gwaji ya yi ajalin kawuna — LadiWata wadda aka garzaya da kawunta wani asibitin gwamnati ranga-ranga a bara, Ladi Adukwu, ta ce likitoci sun tura su a yi masa hoto ranar Asabar, amma ma’aikatan sashen suka ce a jira sai ranar Litinin da safe za a yi.
Ladi ta ce, washegari, ranar Lahadi da safe kawun nata ya rasu. “Da an yi masa a ranar, wata kila da an gano abin da damun an yi masa magani kafin hakan ta kasance.”
Daga Ojoma Akor (Abuja) Ahmad Datti (Kano) Adebyo Gbenga (Legas), Abubakar Akote (Minna).
Fassara: Sagir Kano Saleh
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: lafiya Tiyata wutar lantarki a rashin wutar rashin wuta
এছাড়াও পড়ুন:
Aragchi: Muna Bukatar Rage Zaman Daradar Da Kuma Tabbatar Da Zaman Lafiya A Tsakanin Pakisatan Da Indiya
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana cewa akwai bukatar kasashen Indiya da Pakisatan su daure su daina musayar wuta a tsakaninsu saboda tabbatar da zaman lafiya a yankin Asiya.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a safiyar yau Alhamis bayan isarsa birnin News Delhi.
A jiya larabace sojojin kasar Indiya suka cilla makamai masu linzami kan kasar Pakisatan da kuma yankin Kashamir da ke karkashinn ikon Pakisatn. Inda mutane 31n sauka rasa rayukansu a yayinda wasu 46 suka suka ji Rauni.
Shehbaz Sharif firai ministan kasarPakisatan ya bayyana cewa kasar Pakisatan zata rama, kuma ya sha alwashin maida martani kan duk wani jinin mutanen Pakisatan da sojojin Indiya suka zubar.
Har’ila yau ministan harkokinn wajen kasar Iran ya je kasar ta Indiya ne don halattan taron kwamitin tattalin arziki na hadin giwa tsakanin kasashen biyu. Ministan ya kara da cewa zai tattauna da tokwaransa na kasar Indiya kan yakin da ya barke a tsakanin kasashen biyu.
Sannan a wani labarin kuma kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Esmail Bakaei ya bayyana cewa kasashen Indiya da Iran zasu rattaba hannu a kan wasu yarjeniyoyi tsakanin kasashen biyu a wannan ziyarar Aragchi zuwa kasar ta Indiya.