Iran Ta Bayyana Damuwarsa Da Makaman Nukliyar HKI A Sanda Ake Takura Mata
Published: 11th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana fuska biyu na kasashen yamma, dangane da shirin magakamashin nukliya na kasarsa, da kuma yadda basa magana kan makaman nukliya wanda HKI take da su.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya Asabar, a birnin Doha na kasar Qatar a inda yake halattan taron JMI da kasashen larabawa a jiya Asabar.
Ministan ya kara da cewa, wannan rashin adalci ne a fili sannan nuna fuska biyu, Iran wacce babu tabbas kan shirinta na makamashin nukliya na soje ne, an cika duniya da cewa tana son ta mallaki makaman nukliya amma ga HKI wacce aka tabbatar da cewa tana da makaman na nukliya, babu magana a kan nata.
Aragchi ya kammala da cewa shirin nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya ce, kuma babu wata anniya ta maida shin a kera makaman nukliya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makaman nukliya
এছাড়াও পড়ুন:
Pakisatan Ta Kore Cewa Ta Keta Yarjejeniyar Tsagaita Wutar Yaki
Ma’aikatar harkokin wajen kasar Pakistan ta jadada cewa ko kadan sojojin kasar ba su keta tsagaita wutar yaki da Indiya ba.
A cikin wata sanarwa da ma’aikatar harkokin wajen ta Pakistan ta fitar ta ce; kasar tana ci gaba da aiki da tsagaita wutar yaki wacce aka sanar da ita, kuma sojojin kasar sun kai zuciya nesa, duk da cewa Indiya ce ta keta wutar yakin.
Saanrwar da Pakistan ta biyo bayan zargin da Indiya ta yi wa kasar ne cewa tana keta yarjejeniyar wutar yaki bayan an cimma yarjejeniya a kan hakan.
Jami’i a ma’aikatar harkokin wajen Indiya Bigram Maisari ne ya bayyana hakan a wani taron manema labaru da ya gabatar a yau, sannan ya kara da cea; Muna yin kira ga kasar Pakistan da ta dauki matakan da su ka dace domin kawo karshen keta wutar yakin da take yi.
Shi kuwa Fira ministan yankin Jammo da Kashmir Umar Abdullah cewa ya yi an ji kararrakin fashewar abubuwa masu karfi a garin Sirinigar, da shi ne babbar birnin Kashmir dake karkashin Indiya.
Wasu shaidun ganin ido sun kuma bayyana cewa, an ga jirage marasa matuki suna zarya a sararin samaniyar yankin.
Tun da fari, Fira ministan Pakistan Shahbaz Sharif ya bayyana cewa; Kasarsa ta yi nasara akan makiya, yana mai jinjinawa sojojin kasar da su ka mayar da martani akan wuce gona da irin Indiya da karfi, kuma cikin kwarewa”
Shahbaz ya kuma ce; Indiya ta shelanta yaki akanmu ba tare da wani dalili ba, yana siffata abinda Indiya din ta yi da cewa; Abin kunya ne.”