Iran Ta Bayyana Damuwarsa Da Makaman Nukliyar HKI A Sanda Ake Takura Mata
Published: 11th, May 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya bayyana fuska biyu na kasashen yamma, dangane da shirin magakamashin nukliya na kasarsa, da kuma yadda basa magana kan makaman nukliya wanda HKI take da su.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya Asabar, a birnin Doha na kasar Qatar a inda yake halattan taron JMI da kasashen larabawa a jiya Asabar.
Ministan ya kara da cewa, wannan rashin adalci ne a fili sannan nuna fuska biyu, Iran wacce babu tabbas kan shirinta na makamashin nukliya na soje ne, an cika duniya da cewa tana son ta mallaki makaman nukliya amma ga HKI wacce aka tabbatar da cewa tana da makaman na nukliya, babu magana a kan nata.
Aragchi ya kammala da cewa shirin nukliyar kasar Iran ta zaman lafiya ce, kuma babu wata anniya ta maida shin a kera makaman nukliya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: makaman nukliya
এছাড়াও পড়ুন:
Ko Maƙiyina Ba Na Yi Masa Fatan Tsintar Kansa A Halin Da Na Samu Kaina – Ummi Nuhu
“Na taɓa zama abar kwatance, musamman a ɓangaren da shafi kuɗi, suna, girmamawa, amma kuskuren da na yi ya zama dalilin da yasa masana’antar ta juya min baya, sakamakon babu abin da na iya ko na sani face; harkar ta fim. Halin da ake ciki yanzu, babu wani tallafi, babu aikin yi, akwai lokacin da ina da ɗimbin masoya da suke son aurena da kuma nuna min soyayya, amma sai na kasa zaɓen wanda zan ci gaba da rayuwata da shi a wancan lokaci.
Babban dalilin da ya jawo min koma-baya a harkar fim shi ne, hatsarin da na samu na mota, wanda Allah ya jarrabce ni da shi, na yi hatsarin mota da har sai da na samu karaya huɗu a ƙafata, sannan kuma na samu buguwa a kaina da har sai da na manta da komai na rayuwa da na sani a wancan lokaci, bugu da gari; fuskata ta samu raunuka masu yawa da suka canza mani fasalin fuskar tawa, hakan ya sa na ɗauki tsawon lokaci ina jinya.
Da ta ke amsa tambaya a kan ko ‘yan’uwan sana’arta na Kannywood sun taimaka mata a lokacin da take cikin wannan mawuyacin hali? Ummi ta ce, duk da babu wani wanda ya ɗauki nauyin jinyarta a wancan lokaci, amma dai ba za ta taɓa mantawa da yadda suka riƙa zuwa har gida suna gaishe ta ba, “Ni na ɗauki nauyin jinyar kaina, saboda bakin gwargwado ina da abin da zan iya ɗaukar nauyin jinyata”, in ji Ummi.
Dangane da da-na-sanin da ta ke yi a rayuwa kuma, Ummi ta ce; babu wani abu da take da-na-sanin rashin yi da ya wuce aure, domin da a ce ta yi aure, zuwa yanzu wataƙila da Allah ya azurta ta da samun zuri’a, waɗanda za su riƙa kula da ita yanzu da kuma bayan ta tsufa. “Don haka, ina fatan yin aure kafin rayuwata ta zo ƙarshe”.
Daga ƙarshe, tsohuwar jarumar ta buƙaci matasa masu tasowa a masana’antar Kannywood, da kada su maimaita irin kuskuren da da yawa daga cikin tsoffin jarumai mata suka yi, “Ina shawartar duka wata mace mai lokaci a masana’antar Kannywood yanzu, da ta tabbatar da cewa; ta saka hannun jari a wasu wuraren kasuwanci da za su riƙa samar mata da wani abu ta yadda ko da lokacin ɗaukakarta ya wuce, za ta ci gaba da yi; domin kula da rayuwarta.
Dalili kuwa shi ne, duk irin ɗaukakar da kika samu a yanzu, lokaci na nan zuwa da dole zai gushe, ki zama kamar ba ki taɓa samun wannan ɗaukaka ba, kamar yadda yanzu ake yi babu mu, duk kuwa da irin shaharar da muka samu a lokutan baya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp