Manistan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya gana da tokwaransa na kasar Saudiya Faisal Bin Farhan a birnin Jeddah inda bangarorin biyu suka tattauna kan al-amuran da suka shafi yankin, musamman batun Falasdinawa da kuma halin da suke ciki musamman a yankin gaza.

Inda HKI take kashesu da yuwan,  sannan tana ci gaba da rusa gidajensu a yankin yamma da kogin Jordan.

Har’ila yau, kasashen biyu a matsayin manya-manyan kasashen a yankin yammacin Asiya sun yi kokarin kyautata dangantaka a tsakaninsu. Kuma Aragchi ya je kasar ta saudiya ne don kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu da kuma zurgaga al-adu da al-amura da suka hada kasashen biyu daga ciki har da kasancewarsu kasashe musulmi.

A wani bangare Aragchi ya fadawa tokwaransa inda aka kwana dangane da tattaunawar da kasar take yi da kasar Amurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya ce ma’aikatar harkokin wajen kasar, da ofishin jakadancin kasar a Philippines, sun gabatar da korafi da babbar murya dangane da kalaman da aka jiyo jagoran Philippines na yi game da batun yankin Taiwan na Sin.

Kakakin wanda ya bayyana hakan a Juma’ar nan, ya ce, yayin ziyarar da ya gudanar a kasar India, shugaban na Philippine ya shaidawa ‘yan jarida cewa, idan har yaki ya barke tsakanin Sin da Amurka, tabbas kasarsa za ta shiga, saboda kasancewarta a kewayen yankin, da ma ‘yan Philippines da dama dake zaune a Taiwan, wadanda ya zama wajibi a aiwatar da matakan mayar da su gida.

Jami’in Sin ya kara da cewa kasar Sin daya ce tak a duniya, kuma Taiwan bangare ne na Sin da ba za a iya balle shi ba. Kazalila, batun Taiwan harka ce ta cikin gidan kasar Sin, kuma tushe na babbar moriyar kasar. Don haka warware batun yankin na Taiwan na wuyan kasar Sin ita kadai, kuma ba za ta taba hakuri da tsoma hannun wasu sassan waje ba. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dangantaka Tsakanin Iran da Saudiya Yana Taimakawa Zaman Lafiya A yankin
  • HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya
  • An Zabi Alkalan Wasa Biyu Daga Kasar Iran Don Alkalanci A gasar Kwallon Kafa ta Mata
  • Jami’in Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ya Bayyana Cewa: Iran Ta Cimma Matsayi A Yaki Kwanaki 12
  • Gwamna Yusuf Ya Amince Da Korar Wasu Mataimaka Biyu Bisa Hannu Akan Belin Wani Dilan Miyagun Kwayoyi
  • Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar
  • An kashe manomi da dabbobi 39 a Bauchi
  • Sin Ta Gabatar Da Korafi Da Babbar Murya Dangane Da Kalaman Jagoran Philippines 
  • Isra’ila za ta mamaye ilahirin Zirin Gaza ya koma karkashinta – Netanyahu
  • Iran Ta Kira Taron Gaggawa Na Kasashen Kungiyar OIC Dangane Da Gaza