Manistan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya gana da tokwaransa na kasar Saudiya Faisal Bin Farhan a birnin Jeddah inda bangarorin biyu suka tattauna kan al-amuran da suka shafi yankin, musamman batun Falasdinawa da kuma halin da suke ciki musamman a yankin gaza.

Inda HKI take kashesu da yuwan,  sannan tana ci gaba da rusa gidajensu a yankin yamma da kogin Jordan.

Har’ila yau, kasashen biyu a matsayin manya-manyan kasashen a yankin yammacin Asiya sun yi kokarin kyautata dangantaka a tsakaninsu. Kuma Aragchi ya je kasar ta saudiya ne don kyautata dangantaka tsakanin kasashen biyu da kuma zurgaga al-adu da al-amura da suka hada kasashen biyu daga ciki har da kasancewarsu kasashe musulmi.

A wani bangare Aragchi ya fadawa tokwaransa inda aka kwana dangane da tattaunawar da kasar take yi da kasar Amurka dangane da shirinta na makamashin Nukliya.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza:Falasdinawa 7 Sun Yi Shahada Da Safiyar Yau Asabar

Da safiyar yau Asabar Falasdinawa 7 sun yi shahada sanadiyyar harin da HKI ta kai a yankin Gaza.

Sojojin HKI sun kai harin ne a kan sansanin ‘yan hijira na unguwar ” al-Sabrah” a cikin birnin Gaza, da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa 5 a iyalai daya na Dulaibh. Shahidan su nel Saqar Ahmad Fu’ad dulaibh, da matarsa Hindu, da ‘ya’yansu Ahmad, Hamzah, da Abdulazizi.

Haka nan kuma ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-haren ta jirgin sama maras matuki a unguwar “Tuffah” dake birnin Gaza, da ya yi sanadiyyar shahadar mutum daya.

Su ma jiragen ruwan HKI sun kai wasu hare-haren munanan a garin Rafah da ya yi sanadiyyar shahadar Muhammad Sa’id al-Burudawil.

A tsakiyar birnin Gaza, ma dai ‘yan sahayoniyar sun kai wasu hare-hare da manyan bindigogi da ya yi sanadiyyar shahadar karamin yaron Bafalasdine guda.

A wani gefen hukumar Gaza ta sanar da cewa yunwa, tana barazana ga rayuwar kananan yaran da sun kai 65,000 saboda ci gaba da hana shigar da kayan abinci cikin yankin na Gaza, da HKI take yi, na tsawonn watanni 2 a jere.

Tsawon kwanaki 40 kenan da dukkanin gidajen burodi a cikin yankin na Gaza su ka rufe kofofinsu saboda rashin fulawa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tehran ta bayyana aniyarta na karfafa hadin gwiwar ‘yan sanda da Nijar
  • Putin  Na Rasha Ya Gana Da Shugabannin Afirka Akan Batun Tsaro
  •   Iran Ta Yi Maraba Da Tsayar Da Wutar Yaki A Tsakanin Indiya Da Pakistan
  • Iran Ta Bayyana Damuwarsa Da Makaman Nukliyar HKI A Sanda Ake Takura Mata
  • Shugaban Putin Ya Gana Da Sisi Don Karfafa Harkokin Kasuwanci Tsakanin Kasashen Biyu
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce Kafa Hujja Da ‘Yan Tawaye Kan Iran Yankewar Kauna ce Ga Makiyanta
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Yi Allah Wadai Da Kai Hari Kan Ofishin Jakadancin Kasarsa A Kasar Sweden
  • Gaza:Falasdinawa 7 Sun Yi Shahada Da Safiyar Yau Asabar
  • Ministan harkokin wajen Iran zai Ziyarci Saudiyya da Qatar