Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata
Published: 13th, May 2025 GMT
A daidai lokacin da sake bude yaki a Gaza ya cika kwanaki 57,sojojin HKI suna ci gaba da kai hare-hare akan al’ummar Gaza da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa da dama.
Cibiyar watsa labaru ta Falasdinu ta sanar da cewa; Sojojin na HKI sun kai hare-hare masu yawa a sassa mabanbanta na gaza wanda ya fara tun daga watan Maris, da hakan ya kara jefa Falasdinawa cikin wahala, bayan yunwar da suke fama da ita.
Da safiyar yau Talata sojojin na HKI sun kai hare-hare sau 3 a garin Abasan a gabashin Khan-Yunus.
A cikin birnin Gaza kuwa sojojin na HKI sun baje wasu gidaje da kasa a karo na uku.
A garin Khan-Yunsu wani matashi mai suna Amid Hamdun al-Qudrah, ya yi shahada.
A unguwar “Shuja’iyyah” ma wani Bafalasdine mai suna Muhammad Mu’in al-Ja’abari ya yi shahada sanadiyyar raunin da ya samu a harin baya.
A unguwar “Zaytun” kuwa sojojin na HKI su kai hare-hare ne har sau 8 a yau Talata.
A daren jiya wasu Falasdinawa 3 daga iyali 1 sun yi shahada a cikin tantin ‘yan hijira a yankin ‘al’amudi’ a arewacin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kai hare hare
এছাড়াও পড়ুন:
Iran: Babban Kwamandan Sojojin Ruwa Na JMI Yace Sojojinsa A Shirye Suke Su Shiga Yaki Da Makiya
Babban hafsan hafsoshin sojojin JMI ya bayyana cewa sojojin kasar musamman sojojin ruwa a shirye suke su shigaba yaki dank are kasar a ko yauce, ya kuma kara da cewa idan makiya sun yi wani kuskure zasu yi nadamar hakan.
Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ya nakalto Manjo Janar Mohammad Hussain Bakiri yana fadar haka a jiya litinin a lokacinda shi da wasu manya manayan jami’an sojojin kasar suka kai ziyarar ganewa kansu irin shirin da sojojin kasar suke ciki a tashoshin jiragen ruwa da suke gabar tekun Farisa da kuma arewacin mashigar ruwa ta Hurmus
Tare da manjo janar Bakiri dai akwai kwamandan sojojin ruwa na dakarun IRGC Manjo Janar Abdolrahim Mousavi, sai kuma Manjo Janar Hossein Salami shugaban Lundunonin IRGC da kuma wasu manya-manyan jami’an sojojin kasar.
A wani labarin kuma Janar Salami babban kwamandan sojojin IRGC gaba daya ya bayyana cewa Iran zata kai hari a kan duk wani wurin da makami ya rashi zuwa kasar.