HausaTv:
2025-08-12@09:06:08 GMT

 Falasdinawa Da Dama Sun Yi Shahada A Yau Talata

Published: 13th, May 2025 GMT

A daidai lokacin da  sake bude yaki a Gaza ya cika kwanaki 57,sojojin HKI suna ci gaba da kai hare-hare akan al’ummar Gaza da hakan ya yi sanadiyyar shahadar Falasdinawa da dama.

Cibiyar watsa labaru ta Falasdinu ta sanar da cewa; Sojojin na HKI sun kai hare-hare masu yawa a sassa mabanbanta na gaza wanda ya fara tun daga watan Maris, da hakan ya kara jefa Falasdinawa cikin wahala, bayan yunwar da suke fama da ita.

Da safiyar yau Talata sojojin na HKI sun kai hare-hare  sau 3 a garin Abasan a gabashin Khan-Yunus.

A cikin birnin Gaza kuwa sojojin na HKI sun baje wasu gidaje da kasa a karo na uku.

A garin Khan-Yunsu wani matashi mai suna Amid Hamdun al-Qudrah, ya yi shahada.

A unguwar “Shuja’iyyah” ma wani Bafalasdine mai suna Muhammad Mu’in  al-Ja’abari ya yi shahada sanadiyyar raunin da ya samu a harin baya.

A unguwar “Zaytun” kuwa sojojin na HKI su kai hare-hare ne har sau 8 a yau Talata.

A daren jiya wasu Falasdinawa 3 daga iyali 1 sun yi shahada a cikin tantin ‘yan hijira a yankin ‘al’amudi’ a arewacin Gaza.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kai hare hare

এছাড়াও পড়ুন:

Gaza: Yunwa ta kashe Falastinawa 5 a cikin kasa da Sa’o’i 24 da suka gabata

Ma’aikatar lafiya a Gaza ta sanar da isar shahidai 69 da wadanda suka jikkata su 362 zuwa asibitoci a cikin kasa da sa’o’i 24 da suka gabata.

Daga cikin shahidan akwai wadanda yunwa ce ta kashe su, da kuam wadanda suka yi shahada a wajen neman samun agajin abinci, ida Isra’ila take kai hari kansu abbu kakkautawa.

A cikin rahotonta na kididdiga na yau da kullun, ma’aikatar ta gano mutuwar mutane biyar da suka hada da yaro daya sakamakon yunwa a cikin sa’o’i 24 da suka gabata, wanda adadin wadanda suka yi shahada sakamakon yunwa ya kai 222, ciki har da yara 101.

Ma’aikatar ta tabbatar da cewa adadin wadanda suka mutu a harin ta’addancin Isra’ila ya karu zuwa shahidai 61,499 da kuma jikkatar 153,575 tun daga ranar 7 ga Oktoba, 2023.

Haramtacciyar Kasar Isra’ila na ci gaba da yakin kisan kiyashi da kuma azabtarwa da yunwa a Gaza. Asibitin Al-Awda ya sanar da mutuwar wasu mutane da suka hada da yaro daya da kuma jikkata wasu 26, sakamakon harin Isra’ila a kan ma’aikatan agaji a kudancin Wadi Gaza, da kuma hare-haren da aka kai kan wasu yankuna a tsakiyar zirin Gaza cikin sa’o’i 24 da suka gabata.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ministan tsaron Italiya ya caccaki gwamnatin Netanyahu kan batun Gaza August 12, 2025 Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Wannan Talata August 11, 2025 Iran: Lebanon Tana Da ‘Yancin Kare Kanta Da Makamanta August 11, 2025 Mali: An Kama Sojoji Fiye da 40 Bisa Zargin Yunkurin Juyin Mulki August 11, 2025 Iraki: Larijani Da Sudani Sun Gana A Bagdaza August 11, 2025 Mafi yawan Kasashen Duniya Sun Amince Da Samarda Kasar Falasdinu August 11, 2025 Mahukuntan Iraki: Adadin Masu Ziyarar Arba’een Daga Kasashen Ketare Zai Iya Haura Miliyan 40 August 11, 2025 Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza August 11, 2025 Kwamitin Tsaron MDD Ya Gudanar Da Zaman Taro Kan Aniyar Isra’ila A Kan Gaza August 11, 2025 Shugaban Iran: Dole ne duniya ta kawo karshen laifukan yakin Isra’ila a Gaza August 11, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gaza: Yunwa ta kashe Falastinawa 5 a cikin kasa da Sa’o’i 24 da suka gabata
  • Araghchi: Mataimakin Shugaban IAEA Zai Ziyarci Tehan َA Gobe Talata
  • Sojojin Mamayar Isra’ila Sun kai Wasu Munanan Hare-Hare Kan Yankunan Zirin Gaza
  • HKI Ta Kai Hare-Hare A Kan Garuruwa Da Dama A Yankin Quneitra Na Kasar Siriya
  • Yadda Wasu Jihohi Suka Yi Watsi Da Gine-ginensu Da Ke Legas
  • Ana Zanga-Zanga A Isra’ila Kan Shirin Netanyahu Na Mamaye Gaza
  • Jefa Agajin Abinci Ta Sama A Zirin Gaza Ya Janyo Shahadan Falasdinawa 23 Tare Da Jikkata Wasu 124
  • Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar
  • Falasdinawa 11 Ne Suka Rasa Rayukansu Saboda Yunwa A Gaza
  • Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shari Share Falasdinawa Daga Kn Doron Kasa