Aminiya:
2025-10-13@20:16:35 GMT

Za a kwaso ’yan Nijeriya 15,000 da ke gudun hijira a ƙetare

Published: 11th, May 2025 GMT

Gwamnatin Nijeriya ta ce tattaunawa ta yi nisa domin kwaso ’yan ƙasar guda 15,000 da suke gudun hijira a ƙasashen Kamaru da Nijar da Chadi da wasu ƙasashen cikin mutunci.

Kwamishinan hukumar kula da ’yan gudun hijira ta Nijeriya, Alhaji Tijjani Ahmed ne ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai a Abuja.

Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin An kama matashi da kawunan mutanen a Legas

Ya ce akwai aƙalla ’yan Nijeriya miliyan shida da ke zaman gudun hijira a cikin ƙasar, sannan akwai wasu dubbai da suke zaune a wasu ƙasashen na duniya.

“Akwai ’yan Nijeriya 15,000 da suke so su dawo da kansu; haka kuma muna da ’yan ƙasashen waje aƙalla 100,000 da suke zaman gudun hijira a ƙasar nan.

“Dukkan mutanen nan suna da alhaki a hukumarmu na ba su kulawar da ta dace,” in ji shi.

Ahmed ya yi godiya ga Shugaban Bola Tinubu bisa gudunmuwar da yake ba ma’aikatar jinƙai, sannan ya nanata ƙudurinsu na tabbatar da kwaso ’yan ƙasar da ke zaune a wasu ƙasashen.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gudun hijira Kamaru Nijar gudun hijira a

এছাড়াও পড়ুন:

Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa

Wani mummunan rikicin ƙabilanci a ƙaramar hukumar  Birniwa ta jihar Jigawa ya yi ajalin mutane biyu, yayin da wasu bakwai suka samu munanan raunuka.

Kakakin ’yan sanda ta jihar, DSP Lawan Shiisu Adam, ya tabbatar da faruwar lamarin yayin da yake zantawa da manema labarai. Ya ce tawagar jami’an tsaro ƙarƙashin Operation Salama sun garzaya wurin domin dawo da zaman lafiya tare da cafke wasu mutane bakwai da ake zargi da hannu a rikicin.

Ganau sun ce lamarin ya faru ne lokacin da wasu da ake zargin Fulani ne suka kai farmaki ƙauyen Dagaceri, inda suka ƙona gidaje tare da kai wa mazauna garin hari da kibau a lokacin da suke barci. Rahotanni sun ce gidaje da dama sun ƙone a harin da ya faru a tsakar dare.

DSP Shiisu ya ƙara da cewa jami’an tsaro sun ƙwato wayoyin hannu da layu daga hannun waɗanda ake zargi.

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja

Wannan lamari dai ya ƙara haifar da damuwa kan yadda rikicin ƙabilanci ke sake bayyana a wasu sassan jihar Jigawa.

A watan Satumbar 2024, akalla mutane 15 ne aka kashe a wani rikici makamancin wannan tsakanin kungiyoyin Fulani a ƙauyukan Zangon Maje da Yankunama a ƙaramar hukumar Jahun.

Sai dai duk da waɗannan matsalolin, Jihar Jigawa na daga cikin jihohin da suka fi zaman lafiya a Arewacin Najeriya.

Wani bincike mai zaman kansa da gwamnatin jihar ta gudanar a baya-bayan nan ya nuna cewa Jigawa na cikin jihohi biyar mafi kwanciyar hankali ta fuskar tsaro a cikin gida.

A watan Yuli 2025  Gwamna Umar Namadi ya gudanar da  bikin maido da zaman lafiya a ƙaramar hukumar  Guri, bayan shekaru da dama na rikicin manoma da makiyaya.

Yayin da hukumomin tsaro ke ci gaba da gudanar da bincike don gano musabbabin harin, mazauna yankin na kira ga gwamnati da ta ƙara  tsaurara matakan tsaro da kuma samar da  tsarin gargadin gaggawa na al’umma domin hana ci gaba da  zubar da jini.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin kabilanci: Mutane 2 sun mutu, wasu 7 sun jikkata a Jigawa
  • Zaɓen Kamaru: Tchiroma Bakary na da kwarin gwiwa a yayin da ake jiran sakamako
  • Yaƙi Da Boko Haram: An Kashe Sojoji 2,700 A Shekara 12 – Janar Irabor
  • Daga Karshe Tawagar Super Eagles Ta Sauka A Uyo Bayan Saukar Gaggawa A Angola
  • Shugaban Kasar Najeriya Ya Yi  Afuwa Ga Wasu Mutanen Da Kotuna Su Ka Hukunta
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • ’Yan ta’adda sun kashe sojoji 4 a wani sabon hari a Borno
  • Sojoji Da ‘Yansanda Sun Ceto Mutum Shida Da Aka Yi Garkuwa Da Su A Taraba
  • Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
  • Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida