Aminiya:
2025-08-11@08:27:48 GMT

Za a kwaso ’yan Nijeriya 15,000 da ke gudun hijira a ƙetare

Published: 11th, May 2025 GMT

Gwamnatin Nijeriya ta ce tattaunawa ta yi nisa domin kwaso ’yan ƙasar guda 15,000 da suke gudun hijira a ƙasashen Kamaru da Nijar da Chadi da wasu ƙasashen cikin mutunci.

Kwamishinan hukumar kula da ’yan gudun hijira ta Nijeriya, Alhaji Tijjani Ahmed ne ya bayyana haka a zantawarsa da manema labarai a Abuja.

Matakan da gwamnonin Arewa suke so a ɗauka kan matsalar tsaron yankin An kama matashi da kawunan mutanen a Legas

Ya ce akwai aƙalla ’yan Nijeriya miliyan shida da ke zaman gudun hijira a cikin ƙasar, sannan akwai wasu dubbai da suke zaune a wasu ƙasashen na duniya.

“Akwai ’yan Nijeriya 15,000 da suke so su dawo da kansu; haka kuma muna da ’yan ƙasashen waje aƙalla 100,000 da suke zaman gudun hijira a ƙasar nan.

“Dukkan mutanen nan suna da alhaki a hukumarmu na ba su kulawar da ta dace,” in ji shi.

Ahmed ya yi godiya ga Shugaban Bola Tinubu bisa gudunmuwar da yake ba ma’aikatar jinƙai, sannan ya nanata ƙudurinsu na tabbatar da kwaso ’yan ƙasar da ke zaune a wasu ƙasashen.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: gudun hijira Kamaru Nijar gudun hijira a

এছাড়াও পড়ুন:

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

Rinsola Babajide, Ajibola Abiodun.

 

Yan Wasan Tsakiya

Ibrahim Ayinde, Asisat Oshoala, Chinwendu Ihezuo, Christy Ucheibe, Onyi Echegini,

Yan Wasan Gaba

Chioma Okafor, Toni Payne, Rasheedat Ajibade, Florence Ijamilusi, Esther Okoronkwo

Ifeoma Onumonu,

Hakazalika a wani taron liyafa da shugaba Tinubu ya karɓa, wanda mataimakin shugaban ƙasa, Kashim Shettima ya wakilta, ya bayar da lambar yabo ta ƙasa ga kowace ‘yar wasa ta tawagar ƙwallon kwando a tawagar, tare da ba su kyautar gida a Abuja, a lokacin da yake jawabi ga tawagar, Shettima ya ce nasarar da suka samu alama ce ta ƙarfin haɗin kai.

“Wannan nasara ta nuna abin da ke faruwa iɗan muka yi aiki tare, matan Nijeriya ba su tama bamu kunya a ɓangaren wasanni ba, kuma D’Tigress ta sake sanya mu alfahari,” in ji shi.

D’Tigress kamar yadda ake kiran tawagar ta ƙwallon kwando, ‘yanzu sun tabbatar da samuwar kofinsu na biyar a jere, ta samu nasarar lashe kofin a shekarun 2017, 2019, 2021, 2023, da 2025, wani abin da ba a taɓa ganin irinsa ba a tarihin ƙwallon kwando na matan Afirka.

Jerin ‘yan wasan ƙwallon kwando da suka rabauta da kyautar Dala 100,000

Amy Okonkwo, Pallas Kunaiyi-Akpanah, Elizabeth Balogun, Sarah Ogoke, Ifunanya Okoro, Promise Amukamara, Ɓera Ojenuwa, Murjanatu Musa, Blessin Ejiofor, Ezinne Kalu, Ɓictoria Macaulay, Nicole Enabosi.

Masu Horarwa 

Rena Wakama, Wani Muganguzi, Prince Oyoyo, Ezeala

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji sun kama wasu kan zargin kitsa juyin mulki a Mali
  • INEC Ta Gargaɗi Ƴan Siyasa Kan Azarɓaɓin Yaƙin Neman Zaɓen 2027
  • Harin Ƴan Bindiga Ya Yi Sanadin Kashe Ɗansanda Da Wasu Mutane 4 A Kwara
  • Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya
  • Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya
  • Fashewar gurneti ya kashe yara uku a Borno 
  • Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka
  • ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya
  • Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
  • Nijeriya Na Asarar Tiriliyan 3.2 Sanadiyyar Watsi Da Noma A Gandun Daji