IRGC Ya Kaddamar Da Sabon Sansanin Jiragen Yaki Na Karkashiun Kasa
Published: 10th, May 2025 GMT
Janar Hussain Salami babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci a nan Iran ya kaddamar da sabon sansanin jiragen yaki wadanda ake sarrafasu daga nesa na karkashin kasa.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Janar Salami yana cewa, wadannan jiragen yakin da ake sarrafasu daga nesa, suna iya daukar hotunan jiragen yakin Amurka wadanda suka kasance sansanin jiragen saman yaki na kasar wadanda suke cikin tekuna, don amfani da hotunan saboda kai wa sansanin hare hare.
Salami yace gabatar da wannan sansanin gargadi ne ga mjakiya, sannan duk wata kasa a yankin wacce ta bar Amurka ta yi amfani da dandanin sojojinta da ke kasar don kaiwa kasar Iran hare0hare kasar ma ta zama filin daga.
Wannan kaddamarwan ta na zuwa ne bayan da kasashen Amurka da HKI suka yi barazanar farwa kasar don wargaza cibiyoyin Nukliyar kasar ta Iran. Sai daga bayan shugaba Trump yace ya fi son a cimma yarjeniya da Iran maimakon yaki.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Iran Ta Yi Tsokaci Kan Jita-Jitar Da Ake Yadawa Cewa: Shugaban Kasar Iran Zai Gana Da Shugaban Amurka
Ma’aikatar harkokin wajen Iran ta yi tsokaci kan jita-jitar cewa: Shugaban kasar Iran zai gana da shugaban kasar Amurka
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran Isma’il Baqa’i ya yi watsi da jita-jitar da ake yadawa game da batun cewa shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian zai yi wata ganawa da shugaban Amurka Donald Trump a mako mai zuwa, da rashin gamsuwar bangaren Amurka da Iran da shiga tsakanin masarautar Oman, da kuma cewa Iran ta gabatar da shawarar gudanar da shawarwari kai tsaye da Amurka, da sauran da’awar karya a matsayin batutuwa na jita-jita maras asali da tushe.
Dangane da wata tambaya game da jerin jita-jita da ake yadawa a kafafen yada labarai game da matsayin tattaunawar da ake yi tsakanin Iran da Amurka, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Iran ya jaddada cewa duk wadanda batutuwa da suke fitowa daga majiyoyi marassa tushe da asali kuma mafi yawansu labarai ne na karya na bogi da ba su da wata madogara mai tushe. Baqa’i ya jaddada cewa: Ma’aikatar harkokin wajen kasar ita ce ke da alhakin ba da bayanai dangane da ayyukan jami’an diflomasiyya, ciki har da batun tattaunawar da ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, cikin gaskiya, kwarewa, da kuma lokacin da ya dace.