Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne — Kwankwaso
Published: 10th, May 2025 GMT
Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya soki ’yan siyasar da ke sauya sheƙa daga jam’iyyar da a ƙarƙashinta suka samu nasarar lashe zaɓe zuwa wata.
Kwankwaso ya bayyana lamarin a matsayin cin moriyar ganga, yana mai cewa hakan babban kuskure ne a siyasance.
HOTUNA: An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa Saudiyya JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a gidansa da ke Miller Road a Kano yayin da yake karɓar wasu ’yan siyasar da suka sauya sheƙa zuwa NNPP daga Ƙaramar Hukumar Takai.
Kwankwaso ya ƙara jaddada irin juriya da haɗin kai da ke tafiyar Kwankwasiyya duk kuwa da cewa an ta ƙoƙarin ganin an kawar da hankalin mabiya.
“Duk mun ga abin da ya riƙa faruwa a tarihi, musamman a shekarar 2015 lokacin da wasu ’yan siyasa suka dawo cikinmu amma ashe mayaudara ne masu mugun nufi a zuciyarsu.
“Waɗannan ’yan siyasa sun yi ƙoƙarin kawo hargitsi a cikin jam’iyyarmu amma ba su yi nasara ba.
“Haka ma lokacin da zaɓen 2019 ya zo duk kowa ya san abin da ya faru. Amma abin da yake faruwa a bayan nan ya koya mana darasi sosai.
“Wannan tafiyar tamu ta Kwankwasiyya tana tare da talakawa a kodayaushe, saboda haka duk wani mai kwaɗayi ba zai iya zama a cikinta ba.
Furucin Kwankwaso na zuwa ne yayin da bayan nan wasu jiga-jigan siyasa a NNPP da tafiyar Kwankwasiyya suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC — ciki har da Sanata Kawu Sumaila da Kabiru Alhassan Rurum da sauransu.
Kodayake a baya-bayan nan shi ma dai Kwankwason ana raɗe-raɗin cewa zai koma jam’iyya mai mulki ta APC.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sanata Rabi u Musa Kwankwaso Sauya Sheƙa Kwankwaso ya
এছাড়াও পড়ুন:
Tarayyar Turai: Ana Fuskantar Matsananciyar Wahalar Isar Da Kayan Agaji Zuwa Al-Fashar Na Sudan
Tarayyar turai ta bayyana cewa ma’aikatan Agaji ba za su iya isha cikin garin Al-fahar ba,kuma birnin ya zama tamkar makabarta.
Tarayyar turai din ta bakin mai Magana da yawunta Eva Herneserova ta kuma ce; Sudan ta zama daya daga cikin kasashen da gudanar da ayyukan agaji ya tsananta a duniya,kuma har yanzu da akwai fararen hula da aka killace su adaidai lokacin da ake ci gaba da kai wa asibitoci hare-hare.
Eva Herneserova ta kuma ce; Babu sauki ko kadan a kokarin shiga cikin birnin domin isar da kayan agaji.
Ma Magana da yawun kungiyar tarayyar turai din ta kuma yi gagradi akan cewa bai kamata a rika amfani da yunwa da kuma kisan kiyashi a matsayin makamin yaki ba,domin hakan yana a matsayin take dokokin kasa da kasa ne na ayyukan agaji.
Haka nan kuma ta yi kira ga dukkanin bangarorin da suke fada da juna da koma kan teburin tattaunawa da kuma tsagaita wutar yaki.
Rundunar kai daukin gaggawa ta RSF kwace iko da birnin Al-fasha, bayan da killace shi na tsawon watanni 18. A yayin da mayana rundunar ta RSF su ka shiga cikin birnin sun aikata laifukan yaki da ya hada da yi wa fararen hula kisan kiyashi.
Bugu da kari, suna hana mutane ficewa daga cikin garin domin zuwa inda za su sami aminci.
Gwamnatin Sudan tana zargin kasar UAE da taimakawa mayakan na RSF da makamai da kuma kawo ‘yan ina da yaki daga kasashen Columbia, Sudan Ta Kudu da Afirka Ta Tsakiya.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Wuce Gona Da Iri Kan Kasar Lebanon November 7, 2025 Iran Ta Yi Kira Da A Kafa Kwamitin Kasa Da Kasa Don Binciko Falasdiawan Da Suka Bace A Gaza November 7, 2025 Falasdinawa Miliyan 1.5 Ne Ke Cikin Mawuyacin Hali November 7, 2025 Kwamitin Tsaro Ya Dage Takunkumi Kan Manyan Jami’an Gwamnatin Kasar Siriya November 7, 2025 Karuwar Matsalar Jin Kai Mafi Girma A Duniya A Sudan Saboda Ci Gaba Da Masifar Yaki A Kasar November 7, 2025 An Rantsar Da Paul Biya A Matsayin Shugaban Kamaru Karo Na Takwas November 7, 2025 Dakarun Sojin Kasar Sudan Sun yi Watsi Da Batun Dakatar Da Bude Wuta Da Amurka Ta Gabatar November 7, 2025 Zanga zanga Ta Barke A Birmingham Ta Nuna Kin Jinin Isra’ila . November 7, 2025 Pezeshkiyan: Masu Kawo Rarraba Tsakanin Musulmi Suna yi wa Yan Sahayuniya Aiki Ne November 7, 2025 Shugaban Najeriya Bola Tinubu Ya yi Alwashin Kawo Karshen Ta’addanci A Kasar November 7, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci