Aminiya:
2025-06-24@22:18:13 GMT

Sauya sheƙa bayan cin moriyar jam’iyya butulci ne — Kwankwaso

Published: 10th, May 2025 GMT

Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya soki ’yan siyasar da ke sauya sheƙa daga jam’iyyar da a ƙarƙashinta suka samu nasarar lashe zaɓe zuwa wata.

Kwankwaso ya bayyana lamarin a matsayin cin moriyar ganga, yana mai cewa hakan babban kuskure ne a siyasance.

HOTUNA: An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa Saudiyya JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025

Sanata Kwankwaso ya bayyana hakan ne a gidansa da ke Miller Road a Kano yayin da yake karɓar wasu ’yan siyasar da suka sauya sheƙa zuwa NNPP daga Ƙaramar Hukumar Takai.

Kwankwaso ya ƙara jaddada irin juriya da haɗin kai da ke tafiyar Kwankwasiyya duk kuwa da cewa an ta ƙoƙarin ganin an kawar da hankalin mabiya.

“Duk mun ga abin da ya riƙa faruwa a tarihi, musamman a shekarar 2015 lokacin da wasu ’yan siyasa suka dawo cikinmu amma ashe mayaudara ne masu mugun nufi a zuciyarsu.

“Waɗannan ’yan siyasa sun yi ƙoƙarin kawo hargitsi a cikin jam’iyyarmu amma ba su yi nasara ba.

“Haka ma lokacin da zaɓen 2019 ya zo duk kowa ya san abin da ya faru. Amma abin da yake faruwa a bayan nan ya koya mana darasi sosai.

“Wannan tafiyar tamu ta Kwankwasiyya tana tare da talakawa a kodayaushe, saboda haka duk wani mai kwaɗayi ba zai iya zama a cikinta ba.

Furucin Kwankwaso na zuwa ne yayin da bayan nan wasu jiga-jigan siyasa a NNPP da tafiyar Kwankwasiyya suka sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC — ciki har da Sanata Kawu Sumaila da Kabiru Alhassan Rurum da sauransu.

Kodayake a baya-bayan nan shi ma dai Kwankwason ana raɗe-raɗin cewa zai koma jam’iyya mai mulki ta APC.

 

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Sanata Rabi u Musa Kwankwaso Sauya Sheƙa Kwankwaso ya

এছাড়াও পড়ুন:

Leeds ta ɗauki ɗan bayan Udinese Jaka Bijol

Leeds United ta kammala ɗaukar ɗan wasan bayan ƙungiyar Udinese na ƙasar Slovenia, Jaka Bijol mai shekaru 26 kan farashin fam miliyan 15.

Wannan dai shi ne sabon ɗan wasa na biyu da ƙungiyar ta ɗauka bayan zuwan ɗan wasan gaban Jamus, Lukas Nmecha, kyauta.

‘Harin da Iran ta kai wa sansanin sojin Amurka keta haddin Qatar ne’ Iran ta ƙaddamar da hare-hare kan sansanonin sojin Amurka

Cefanen Bijol da Leeds ta yi zai ƙara wa ƙungiyar tagomashi wajen tsaron bayanta a yayin da ake shirye-shiryen dawowa sabuwar kakar wasanni ta Firimiyar Ingila.

Bijol dai ya buga ƙasarsa Slovenia wasanni 63 ciki har da rawar gani da ya taka a gasar Euro 2024, inda suka yi canjaras da Ingila a wasannin cikin rukuni gabanin rashin nasara a hannun Portugal yayin bugun daga kai sai mai tsaron raga daf da tafiya matakin kwata-fainal.

Bijol ya shafe kaka uku a yana taka wa Udinese leda a gasar Serie A, inda ya haska a wasanni 95 bayan dawowarsa ƙungiyar ta Italliya daga CSKA Moscow, inda ya shafe shekaru hudu.

Leeds dai ta samu nasarar haurowa Firimiyar Ingila a watan Mayun da ya gabata, bayan ta karkare gasar Championship ta maki 100 daidai da Burnley wadda ta bai wa rata da kwallaye.

AFP

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato
  • Trump ya zargi Isra’ila da Iran da saɓa yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Manchester United Za Ta Biya Fam Miliyan 60 Don Ɗaukar Mbeumo Daga Brentford
  • Leeds ta ɗauki ɗan bayan Udinese Jaka Bijol
  • Akwai ƙasashen da ke shirin bai wa Iran makaman nukiliya — Rasha
  • Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
  • 2027: Wajibi Ne A Saka Sakamakon Zaɓe A Na’ura – Farfesa Jega
  • ’Yan bindiga sun sace babban alƙali a Bayelsa 
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da kisan ’yan ɗaurin aure a Filato
  • Matsalolin Rayuwa: Matasan Suleja Na Buƙatar Ƙarfafa Gwuiwa