Na yi wannan wannan ziyara ne saboda shaukin da nike da shi a kan abin da ya shafi kishin kasata Nijeriya, da kuma neman hadin kan kasashen Afirika ta yamma mu zama tsintsiya madaurinki daya,da son zaman lafiya da ci gaban Dimokaradiyya.

Kazalika, na yi wannan rangadi ne domin murnar cikar kungiyar ECOWAS shekara 50 da kafuwa.

Kasan an kafa kungiyar ne ranar 28 ga watan Mayu,1975 bana kungiyar za ta cika shekaru 50. To kasancewa shekaru 50 sun wuce wasa na ga cewa, kungiyar ta cancanci a yaba mata, kuma a kara matakaimi da azama. Kuma za ka yarda da ni idan na ce ma cikin wadannan shekaru 50, Kungiyar ta taka muhimmiyyar rawa ta a zo a gani wajen bunkasa tattalin arzikin kasashen Afirika da hadin kai tare da kulla zumunci a tsakanin wadannan kasashe. Kadan daga cikin rawar da Kungiyar ta taka sun hada da cire bisa ga matafiya mazauna yankin, hakan ya karfafa shige da fice don kasuwanci, neman ilimi da yawon bude .

Wani kuma ci gaba da Kungiyar ta kawo shi ne samar da zaman lafiya. Mun ga rawar da Kungiyar ta taka a lokacin yakin basasa a kasashen Saliyo da Laberiya.

Haka kuma, Kungiyar tana assasa mulkin Dimokaradiyya, kamar yadda ta yi a kasashen Nijar, Gambia da Cote D’Iboire a lokutta daban-daban. To wadannan sune dalillaina na nuna goyan baya ga Kungiyar.

Ya al’ummar Kasashen suka karbi   gangamin da ka kai musu na bunkasar dimokradiyya

Alhamdulillah, mutane sun ji dadi kuma sun ba da hadin Kai. Na hadu da mutane daban-daban, Kuma abin da na fahimta shi ne mutanen Afirika mutane ne masu son zaman lafiya da kwanciyar hankali. Kuma mutane suna goyon bayan mulkin Dimokaradiyya.

Ta yaya Nijeriya za ta amfana da wannan ziyarar?

Nijeriya ta dade tana taka rawa wajen taimaka wa kasashen Afirika. A tsarin manufofin kasashen ketare na Nijeriya, Najeriya tana fifita muradan kasashen Afirika.

Idan aka samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a Afirika, Nijeriya za ta amfana. Ni Kuma dama manufar tattakina shi ne a zauna lafiya.

Sannan kada ka manta ko bayan cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu,shi ne shugaban kungiyar ECOWAS, Nijeriya ce ke ba da kaso mai tsoka na kudaden da ake tafiyar da ECOWAS. Saboda haka, nuna goyan baya ga ECOWAS daidai yake da nuna goyan baya ga kasata Nijeriya.Wanda ba ya san ECOWAS, ba ya son Nijeriya, nima ba na son shi kowaye.

Wanne tallafi ka samu daga gwamnati a wannan gaggarumin aiki da ka yi?

Ina dai fatan yanzu gwamnati za ta tallafa mani in samu in buga littafina Mai sunan : ECOWAS: Labarin Ziyarata kasashen Afirika ta yamma. Wannan littafin ya kunshi duk abubuwan da suka shafi ziyarata wadannan kasashe goma wadanda na ziyarata ta mota. Kuma zan so in kaddamar da littafin nan ba da dadewa ba.

Ko akwai wani bayani da kake son al’umma su sani da ban tambaye ka ba?

Al’umma su daina bari ‘yan siyasa na yaudarar su. Ya kamata mutane su nemi sahihan bayanai game da mulki da tsarin mulki.

Mu daina kira wa kanmu ruwa, kamar masu da’awar mulkin soja. Mulkin soja bala’i ne ba alheri ba ne. Duk kasashen nan na AES da ake mulkin soja,suna cikin fitina. Amma sai a boye gaskiya azo ana yada farfaganda da karya. Mu son kasarmu,mu nuna kishinta, kada mu dinga aibata ta domin ba mu da wata kasar sai ita.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ECOWAS zaman lafiya kungiyar ta Kungiyar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, ya zabi dan wasan tsakiya Bernardo Silba a matsayin sabon kyaftin din kungiyar, jaridar Daily Mail ta rawaito Guardiola ya yanke hukuncin da kan sa inda ya ki ya nemi shawarar sauran yan wasan kungiyar, Silba ya maye gurbin Kebin De Bruyne bayan dan kasar Belgium din ya bar Etihad a karshen kwantiraginsa.

Guardiola ya kuma nada mataimakan kyaftin guda uku kafin fara gasar kakar wasa ta gaba da suka Ruben Dias, Rodri da Erling Haaland, Silba wanda kwantiraginsa zai kare a bazara mai zuwa, ka iya daura kambun kyaftin na Manchester City na kakar wasa daya kawai idan bai samu karin kwantiragi a kungiyar ba.

Jakadan Sin Dake Amurka Ya Yi Jawabi A Gun Liyafar Da Kwamitin Kasa Mai Lura Da Kasuwancin Amurka Da Sin Ya Shirya Atiku Da Wasu Sun Kafa Sabuwar Jam’iyya, Sun Nemi INEC Ta Musu Rajista

Duk da cewa har yanzu bai rattaba hannu kan wata sabuwar yarjejeniya da City ba, Silba ya ki amincewa da tayin da dama na barin kungiyar a kasuwar musayar yan wasa na baya-bayan nan, kungiyoyin Saudiyya da dama na zawarcin dan wasan na Portugal, sai kuma tsohuwar kungiyarsa ta Benfica da itama ke fatan dawowarsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa
  • Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba
  • Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu
  • Iran ta kama ’yan leƙen asirin Isra’ila 6
  • Majalisar Dattawa Na Nazarin Shawarwari 31, Da Ƴancin Ƙananan Hukumomi
  • Bio ya maye gurbin Tinubu a matsayin sabon shugaban ECOWAS
  • Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi
  • Bernado Silba Ya Zama Sabon Kyaftin Din Manchester City 
  • Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa
  • Kiran Gwamnatin Tarayya Ga ‘Yan Jarida: Ku Zama Jigo Wajen Gina Dimokuraɗiyyar Nijeriya