Na yi wannan wannan ziyara ne saboda shaukin da nike da shi a kan abin da ya shafi kishin kasata Nijeriya, da kuma neman hadin kan kasashen Afirika ta yamma mu zama tsintsiya madaurinki daya,da son zaman lafiya da ci gaban Dimokaradiyya.

Kazalika, na yi wannan rangadi ne domin murnar cikar kungiyar ECOWAS shekara 50 da kafuwa.

Kasan an kafa kungiyar ne ranar 28 ga watan Mayu,1975 bana kungiyar za ta cika shekaru 50. To kasancewa shekaru 50 sun wuce wasa na ga cewa, kungiyar ta cancanci a yaba mata, kuma a kara matakaimi da azama. Kuma za ka yarda da ni idan na ce ma cikin wadannan shekaru 50, Kungiyar ta taka muhimmiyyar rawa ta a zo a gani wajen bunkasa tattalin arzikin kasashen Afirika da hadin kai tare da kulla zumunci a tsakanin wadannan kasashe. Kadan daga cikin rawar da Kungiyar ta taka sun hada da cire bisa ga matafiya mazauna yankin, hakan ya karfafa shige da fice don kasuwanci, neman ilimi da yawon bude .

Wani kuma ci gaba da Kungiyar ta kawo shi ne samar da zaman lafiya. Mun ga rawar da Kungiyar ta taka a lokacin yakin basasa a kasashen Saliyo da Laberiya.

Haka kuma, Kungiyar tana assasa mulkin Dimokaradiyya, kamar yadda ta yi a kasashen Nijar, Gambia da Cote D’Iboire a lokutta daban-daban. To wadannan sune dalillaina na nuna goyan baya ga Kungiyar.

Ya al’ummar Kasashen suka karbi   gangamin da ka kai musu na bunkasar dimokradiyya

Alhamdulillah, mutane sun ji dadi kuma sun ba da hadin Kai. Na hadu da mutane daban-daban, Kuma abin da na fahimta shi ne mutanen Afirika mutane ne masu son zaman lafiya da kwanciyar hankali. Kuma mutane suna goyon bayan mulkin Dimokaradiyya.

Ta yaya Nijeriya za ta amfana da wannan ziyarar?

Nijeriya ta dade tana taka rawa wajen taimaka wa kasashen Afirika. A tsarin manufofin kasashen ketare na Nijeriya, Najeriya tana fifita muradan kasashen Afirika.

Idan aka samu zaman lafiya da kwanciyar hankali a Afirika, Nijeriya za ta amfana. Ni Kuma dama manufar tattakina shi ne a zauna lafiya.

Sannan kada ka manta ko bayan cewa shugaba Bola Ahmed Tinubu,shi ne shugaban kungiyar ECOWAS, Nijeriya ce ke ba da kaso mai tsoka na kudaden da ake tafiyar da ECOWAS. Saboda haka, nuna goyan baya ga ECOWAS daidai yake da nuna goyan baya ga kasata Nijeriya.Wanda ba ya san ECOWAS, ba ya son Nijeriya, nima ba na son shi kowaye.

Wanne tallafi ka samu daga gwamnati a wannan gaggarumin aiki da ka yi?

Ina dai fatan yanzu gwamnati za ta tallafa mani in samu in buga littafina Mai sunan : ECOWAS: Labarin Ziyarata kasashen Afirika ta yamma. Wannan littafin ya kunshi duk abubuwan da suka shafi ziyarata wadannan kasashe goma wadanda na ziyarata ta mota. Kuma zan so in kaddamar da littafin nan ba da dadewa ba.

Ko akwai wani bayani da kake son al’umma su sani da ban tambaye ka ba?

Al’umma su daina bari ‘yan siyasa na yaudarar su. Ya kamata mutane su nemi sahihan bayanai game da mulki da tsarin mulki.

Mu daina kira wa kanmu ruwa, kamar masu da’awar mulkin soja. Mulkin soja bala’i ne ba alheri ba ne. Duk kasashen nan na AES da ake mulkin soja,suna cikin fitina. Amma sai a boye gaskiya azo ana yada farfaganda da karya. Mu son kasarmu,mu nuna kishinta, kada mu dinga aibata ta domin ba mu da wata kasar sai ita.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: ECOWAS zaman lafiya kungiyar ta Kungiyar ta

এছাড়াও পড়ুন:

Babban Bankin Nijeriya Ya Rage Kuɗin Ruwan Da Bankuna Ke Caja

 

Wannan ne dai karo na farko da adadin gejin kuɗin ruwa ya yi ƙasa, wato mafi ƙaranci a cikin shekaru biyar.

 

Gwamnan na CBN ya ce an yanke shawarar rage kuɗin ruwan ne domin ci gaba da bunkasuwar tattalin arzikin cikin gida (GDP), da karyewar hauhawar farashi, wanda tsawon watanni biyar kenan ana samu a jere.

 

Tuni, dama masana suka yi hasashen cewa malejin tsadar rayuwa zai ƙara yin ƙasa sosai a sauran watannin ƙarshen 2025.

 

Haka kuma wani dalilin rage kuɗin ruwan shi ne domin a ci gaba da ƙarfafa tattalin arziki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Babban Bankin Nijeriya Ya Rage Kuɗin Ruwan Da Bankuna Ke Caja
  • Hindi: Amurka Da Kasashen Yamma Ba Sa Son A Dakatar Da Bude Wuta A Gaza.
  • Tattalin Arzikin Najeriya Ya HaBaka A Rubu’i Na Biyu Na 2025
  • He Lifeng: Ya Kamata Sin Da Amurka Su Karfafa Dangantakar Tattalin Arziki Da Cinikayya Mai Dorewa Cikin Lumana
  • Tattalin arzikin Najeriya ya ƙara haɓaka — NBS
  • Da Ɗumi-ɗumi: Tattalin Arzikin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 4.32 A 2025
  • Kashim Shettima Ya Isa New York Halartar Taron UNGA Na 80
  • APC Da PDP Na Zargin Juna Kan Amfani Da Addini Wajen Neman Nasara A 2027
  • Iran Da Pakistan Sun Sake Tsara Dangantakarsu Ta Tattalin Arziki
  • Ranar Zaman Lafiya ta Duniya: Kungiyar Arewa Ta Nemi Ƙarfafa Sirrin Tsaro Don Kare ‘Yan Najeriya