HausaTv:
2025-06-14@14:44:34 GMT

Amurka ta kulla yarjejeniyar sayen makamai ta dala biliyan 142 da Saudiyya

Published: 13th, May 2025 GMT

Amurka ta sanar da cimma wata yarjejeniya makamai mai tsoka ta Dala biliyan 142 da Saudiyya.

Wanan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar Amurka Donald Trump, ke gudanar da ziyara a kasar Saudiyya irinta ta farko a ketare tun bayan sake hawansa karagar mulki.

Amurka ta bayyana yarjejeniyar a matsayin “mafi girma a tarihi.

” Wannan yarjejeniya, wacce wani bangare ne na babban kunshin alkawurran saka hannun jari – da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 600, a cewar gwamnatin Amurka – za ta ba wa masarautar Saudiyya damar sayen “kayan aikin soja daga kamfanonin tsaron Amurka goma sha biyu,” musamman a fannin tsaron sararrin samaniya, makamai masu linzami, tsaron teku da tsarin sadarwa.

A wani labarin kuma shugaban kasar ta Amurka ya sanar da dage takunkumi kan kasar Siriya.

“Zan ba da umarnin dage takunkumin da aka kakaba wa Siriya domin ba su dama ta daukaka,” in ji shugaban na Amurka, wanda ke nuni da cewa ya cimma wannan matsaya ne bayan bukatar gaggawar da yarima mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ya yi masa.

Ana san kuma zai gana da shugaban rikon kwarya na Siriya Ahmed al-Charaa nan gaba a Saudiyyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar

Ministan man fetur na kasar Iran Mohsen Paknejad ya bayyana cewa kasarsa zata ci gaba da saida danyen man fetur ga masu sayensa a kasashen waje duk tare da kokarin gwamnatin kasar Amurka na kara kuntatawa kasar a bangaren saida makamashin kasar ga kasashen waje.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto ministan yana fadar haka a jiya laraba bayan taron majalisar ministocin kasar a nan Tehran.

Ministan ta kara da cewa shirin Amurka na hana Iran saida danyen manta ga kasashen waje zai rugurguje kamar yadda ya rugurguje a baya. Y ace don mun rika mun gano kan zaren lalata duk wani shiri na hana mu saida danyin man ga masu sayan man kasar.

Ministan ya bayyana cewa labara ya zo masa kan cewa gwamnatin Amurka na kokarin kakabawa kasar takunkuman tattalin arziki kan sinadarin Methanol na kasar, shi ma suna aiki a kansa.

Gwamnatin Amurka ta Donal Trump tun watan Fabray run wannan shekarar ta fara wani sabin shiri na takurawa Iran, daga ciki har da maida sayar da danyen man fetur na kasar zuwa sifili.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran, ta yi wa Isra’ila ruwan makamai masu linzami
  • Bin Hanya Daya Da Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Muhimmin Mataki Ne Na Ba Da Tabbaci Ga Huldar Ciniki Da Tattalin Arzikin Sin Da Amurka
  • Masana Ilimin Nukiliyar Iran Sun Yi Shahada
  • Matsin Rayuwa: ‘Yan Nijeriya Sun Rage Zuwa Kasashen Waje
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
  • Ministan man Fetur na Kasar Iran Yace Amurka Ta Kasa Hana Iran Saida Danyen Man Fetur Na Kasar
  • Ana shirin mayar da rantsar da Shugaban Nijeriya zauren majalisa
  • Amurka da China sun cimma sabuwar yarjejeniyar kasuwanci
  • He Lifeng Ya Bukaci Amurka Da Ta Warware Takaddamar Cinikayya Da Sin Ta Hanyar Tattaunawa Da Hadin Gwiwa