HausaTv:
2025-06-28@02:46:01 GMT

Amurka ta kulla yarjejeniyar sayen makamai ta dala biliyan 142 da Saudiyya

Published: 13th, May 2025 GMT

Amurka ta sanar da cimma wata yarjejeniya makamai mai tsoka ta Dala biliyan 142 da Saudiyya.

Wanan dai na zuwa ne a daidai lokacin da shugaban kasar Amurka Donald Trump, ke gudanar da ziyara a kasar Saudiyya irinta ta farko a ketare tun bayan sake hawansa karagar mulki.

Amurka ta bayyana yarjejeniyar a matsayin “mafi girma a tarihi.

” Wannan yarjejeniya, wacce wani bangare ne na babban kunshin alkawurran saka hannun jari – da darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 600, a cewar gwamnatin Amurka – za ta ba wa masarautar Saudiyya damar sayen “kayan aikin soja daga kamfanonin tsaron Amurka goma sha biyu,” musamman a fannin tsaron sararrin samaniya, makamai masu linzami, tsaron teku da tsarin sadarwa.

A wani labarin kuma shugaban kasar ta Amurka ya sanar da dage takunkumi kan kasar Siriya.

“Zan ba da umarnin dage takunkumin da aka kakaba wa Siriya domin ba su dama ta daukaka,” in ji shugaban na Amurka, wanda ke nuni da cewa ya cimma wannan matsaya ne bayan bukatar gaggawar da yarima mai jiran gadon Saudiyya Mohammed bin Salman ya yi masa.

Ana san kuma zai gana da shugaban rikon kwarya na Siriya Ahmed al-Charaa nan gaba a Saudiyyar.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Gombe, ta samu nasarar kama wasu ɓarayin daji da suka addabi garin Bajoga da ke Ƙaramar Hukumar Funakaye.

Wannan na daga cikin ƙoƙarin da rundunar ke yi wajen yaƙar masu aikata laifuka a faɗin jihar.

Ribas: Duk wani rikici tsakanina da Fubara ya ƙare – Wike NAJERIYA A YAU: Ko Wadanne Dalilai Ne Ke Hana Mata A Arewa Koyon Ilimin Kimiyya?

A wata sanarwa da Kakakin Rundunar, DSP Buhari Abdullahi, ya fitar, ya bayyana cewa an kama mutum huɗu da ake zargi da kai wa wani matashi mai suna Muhammed Ahmed hari, wanda ke zaune a Unguwar Matasa, Bajoga.

An ce ɓarayin sun kai masa hari da makami cikin dare, inda suka tsoratar da shi da adda da sanduna, suka kuma ƙwace masa kayayyaki.

Sanarwar ta ce laifin ya faru da sanyin safiyar ranar 26 ga watan Yuni, 2025, da misalin ƙarfe 1:30 na dare.

Sun shiga gidan Ahmed ɗauke da makamai, suka kuma yi masa barazana da cewa za su kashe shi idan bai biya musu buƙata ba.

Waɗanda ake zargi da aikata wannan laifi sun haɗa da Manu Muhammed da ake kira (Bappa Charger), Auwalu Muhammed da ake kira (Yellow) mai shekaru 30 daga Bajoga.

Sauran sun haɗa da Ubaida Sani mai shekaru 19 daga Unguwar Pantami a Gombe, da Hussaini Muhammed mai shekaru 19 daga Unguwar Madaki, Gombe.

DSP Buhari, ya ce yayin da ake gudanar da bincike, ’yan sanda sun ƙwato babur ƙirar Haojue UD wanda kuɗinsa ya Naira miliyan 1.6, wayoyi uku da kuɗinsu ya kai Naira 336,000, tsabar kuɗi Naira 74,150, da kuma wuƙa.

Ya ƙara da cewa waɗanda ake zargin suna hannun ’yan sanda yanzu, kuma bincike na ci gaba da gudana.

Ya ce da zarar an kammala bincike, za a gurfanar da su a gaban kotu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva
  • Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba
  • Xi Jinping Ya Gana Da Firaminitan Senegal Da Shugaban Ecuador
  • ’Yan sanda sun kama ɓarayi 5, sun ƙwato kuɗi da makamai a Gombe
  • An Yi Bikin Nune-Nunen Kayan Al’adu Na Murnar Cika Shekaru 55 Da Kulla Huldar Diflomasiyya Tsakanin Sin Da Italiya A Rome
  • Gwamnatin Kano ta ba da hutun sabuwar shekarar musulunci
  • Gwamnatin Gombe za ta biya ’yan fansho Naira biliyan 6.6 kuɗin ritaya
  • Arsenal za ta ɗauki ɗan ƙwallon Brentford Christian Norgaard
  • Za mu ci gaba da tattaunawa da Iran kan yarjejeniyar nukiliya — Trump
  • PDP ta mayar wa da na hannun damar Wike kujerarsa ta sakatarenta