HKI Ta Kai Hare Hare Kan Wani Sansanin Yan Gudun Hijira A Yamma Da Kogin Jordan
Published: 12th, May 2025 GMT
Sojojin HKI sun ci gaba da kai hare hare kan birane da garuruwan yankin yamma da kogin Jordan.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, hare-haren jiya sum sun fi maida hankali ne a garin Tulkaram da kuma sansanin yan gudun hijirar yankin
A wannan karomma sojojin HKI sun bada umurni ga ma zauna garin Tullaram mata da maza da yara da tsoffi duk su fice daga gidajensu.
Kwanaki 105 da suka gabata ne gwamnatin HKI ta fara wannan shirin na korar falasdinwa da kuma rusa gidajensu da nufin korarsu kwatakwata daga yankin. MDD ta bayyana a baya ya zuwa yanzu sun kori falasdinawa kimani 40,000 daga gidajensu, inda suka rusa su suka kuma .
A wani labarin kuma a jiya Lahadi sojojin yahudawan sun kai farmaki kan wata makaranta a Halhum da ke kusa da birnin Khalil inda suka jefa hayaki mai sa hawaye kan daliban da suke karatu a cikin makarantar ta kuma sa wasu da dama shaker iskar da kuma shekewa wuya. Na wani lokaci.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a Zamfara
Daya daga cikin manyan ’yan bindigar da suka addabi Najeriya, Bello Turji ya kashe ’yan sa-kai sama da 40 a wani harin kwanton bauna da ya kai a jihar Zamfara ranar Lahadi.
Bayanai sun nuna daga cikin wadanda aka kashe din har da wasu jami’an hukumar tsaro ta DSS su hudu da kuma wani tubabben dan bindiga da yanzu yake aikin bayar da bayanai ga jami’an tsaro, Bashar Maniya.
Majiyoyi daga yankin sun tabbatar da cewa an kai harin ne a kusa da Rugar Chida, wani kauyen da mahaifin Bello Turjin ke rike da sarautar gargajiya.
Barau ya nesanta kansa daga masu nema masa kujerar mataimakin Tinubu a 2027 An tura ’yan China 6 kurkuku kan laifin ta’addanci a NijeriyaAn dai yi wa jami’an da ke tafiya a cikin motoci biyu da babura kwanton baunar ne a yankin wanda ya shafe mako biyu babu sabis din waya saboda aikin da sojoji suke a ciki.
Wata majiya a yankin ta tabbatar wa Aminiya cewa harin ya daga musu hankali matuka kuma an shirya shi yadda ya kamata.
Majiyar ta ce, “An mamaye su. Bello Turji da yaransa sun kashe mutum 40 daga cikinsu sannan suka kwace ababen hawan da suke kai.
“Turji ya ji dadin harin sosai musamman saboda Bashar Maniya na cikin wadanda aka kashe, wanda tun a baya dama babban abokin hamayyarsa ne kafin ya tuba daga ta’addancin,” in ji majiyar.
A cikin wani bidiyo da ya karade shafukan sada zumunta, an ga Bello Turji yana murna tare da nuna gawarwakin mutanen, ciki har da ta Bashar Maniya, yana rera wakokin cin nasara.
“Wannan ce gawar Kwamandan da ya jagoranci harin,” kamar yadda aka jiyo Turjin yana bayyanawa a cikin bidiyon.
Daga bisani dai an kwaso gawarwakin mutanen tare da gudunmawar sojojin sama, yayin da wadanda suka jikkata kuma aka garzaya da su asibiti.
Wani jami’in tsaro da bai amince a bayyana sunansa ba, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya bayyana shi da abin takaici da za a iya kauce masa matukar ana aiki tare tsakanin jami’an tsaro da mutanen gari.
Bayanai dai sun nuna gabanin kisan mayakan, an kashe ’yan bindiga yaran Bello Turji sama da 30 a wata ba-ta-kashi da aka yi tsakanin yaran Turjin da na Maniya.