NAJERIYA A YAU: Gaskiyar Tasirin Amfani Da Irin Noma Na GMO
Published: 12th, May 2025 GMT
Alamu na nuna cewa galibin manoma a Najeriya suna da shakku a kan amfani da irin da aka sauya ƙwayoyin halittarsa.
Hakan dai na faruwa ne duk da bayanan da wasu masana suka yi game da alfanun wannan iri wanda ake kira GMO ko Genetically Modified Organism a turance.
Tuni dai wasu masanan, waɗanda suka shirya wani taron bita ga manema labarai, suka yi gargaɗi game da illolin irin.
Ko mece ce gaskiya game da amfani da wannan iri na GMO?
NAJERIYA A YAU: Abin ya sa aka kasa kawo ƙarshen Tamowa a Arewa Maso Gabas DAGA LARABA: Ɓoyayyun Dalilan Da ke Sa Faɗuwa Jarabawa A NajeriyaWannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannann rana zai yi duba.
Domin sauke shirin, latsa nan
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: ƙwayoyin halitta
এছাড়াও পড়ুন:
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Ce Kafa Hujja Da ‘Yan Tawaye Kan Iran Yankewar Kauna ce Ga Makiyanta
Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Amfanin da fira ministan gwamnatin mamaya ya yi da ƙungiyar ta’addanci babbar alama ce ta cikakkiyar yanke ƙauna
Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Matakin da fira ministan gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu ya dauka na yi amfani da wata karkatacciyar kungiyar ta’addanci ta “MKO” wato kungiyar Munafukai wajen yada labaran karya game da shirin makamashin nukiliyar Iran, don tsoratar da al’ummar duniya kan Iran, wata babbar alama ce ta yanke kauna.
A sakon da ya wallafa shafinsa na X ministan harkokin wajen Iran Abbas Araqchi ya bayyana cewa: Yayin da ake ci gaba da zaman tattaunawa ba na kai tsaye ba tsakanin Iran da Amurka, ana ci gaba da fitar da karin “hotunan tauraron dan adam don yada tsoro da fargaba kan Shirin makamashin nukiliyar Iran na zaman lafiya, inda ake murguda gaskiya zuwa karya.
Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: Fira ministan haramtacciyar kasar Isra’ila Benjamin Netanyahu, a matsayinsa na mai neman kawo cikas da zagon kasa, ya yi amfani da dukkan tsoffi da sabbin ma’aikatan da ya dauka a matsayin wani bangare na manufofinsa na “kayyade ayyuka ga Trump.”
Araghchi ya ce: A wannan karon, Netanyahu ya koma yin amfani da bayin Saddam Hussain ‘yan kungiyar ta’addanci ta “MKO” da suka kasance kaskantattu su na shirya masa karairayi kan Shirin nukiliyar Iran, inda dogaro da rahotonnin kungiyar “MKO” babbar alama ce ta yanke ƙauna.