A yau Litinin, mai magana da yawun ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ya bayyana cewa, Sin da Amurka sun cimma matsaya tare da fitar da sanarwar hadin gwiwa bayan taron kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu, inda ya kara da cewa, hakan wani muhimmin mataki ne da bangarorin biyu suka dauka na warware sabaninsu ta hanyar yin shawarwari da tuntuba bisa daidaito, tare da aza tubali da samar da yanayi na kara dinke baraka da zurfafa hadin gwiwa.

Daga bangarenta kuwa, Darakta-Janar ta Hukumar Kasuwanci ta Duniya (WTO) Ngozi Okonjo-Iweala, a jiya Lahadi ta bayyana cewa, ta yi farin cikin ganin an samu sakamako mai kyau yayin taron kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka.

A cikin wata sanarwa da ta fitar, Okonjo-Iweala ta ce tattaunawar ta nuna wani muhimmin mataki na ci gaba, inda ta kara da cewa bisa halin da ake ciki a duniya, irin wannan ci gaba da aka samu na da matukar muhimmanci ba ga kasashen biyu kadai ba, har ma da sauran kasashen duniya, ciki har da kasashe masu fama da matsalar tattalin arziki. (Abdulrazaq Yahuza Jere)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno

Sojoji sun kashe ’yan ta’addan Boko Haram 9 tare da kwato kudi fansa kimanin Naira miliyan 5 a  yankunan Magumeri da Gajiram a jihar Borno.

Kakakin rundunar Operation Hadin Kai (OPHK), Laftanar Kanar Sani Uba , ya ce sojojin da suke sintiri a yankunan ne suka hallakan mayakan bayan sahihan bayanan sirri kan zirga-zirgar ’yan ta’addan a kusa da Goni Dunari a Karamar Hukumar Magumeri.

Sanarwa da ya fitar a ranar Asabar, 11 ga Oktoba, 2025 ta ce, “Dakarun mu sun yi gaggawar daukar matakin dakile barazanar bayan da suka ga yadda ’yan ta’addan suka kona gidaje tare da tsoratar da mutanen yankin.”

Ya bayyana cewa sojoji sun yi artabu da ’yan ta’addan ne bayan sun shafe sa’o’i hudu suna bibiyar su, inda suka kashe mayaka biyar tare da tilasta wa sauran tserewa.

Soja ya harbe matarsa, ya kashe kansa a Jihar Neja Yaƙin Gaza: Hamas da Isra’ila sun fara sakin fursunoni

Kayayyakin da aka kwato sun haxa da bindiga kirar AK-47, alburusai, wuqa, da wayar hannu.

Uba ya qara da cewa “Babu asarar rayuka ko asarar kayan aiki da sojojin mu suka yi.”

A wani samamen kuma a hanyar Gajiram Bolori – Mile 40 – Gajiganna, sojoji sun yi arangama da mayakan Boko Haram a kusa da kauyen Zundur, inda suka kashe ’yan ta’adda hudu tare da kubutar da wasu mutane biyu da aka yi garkuwa da su daga Guzamala.

Kayayyakin da aka kwato sun hada da wata mota, sabbin wayoyin hannu guda biyu, man fetur lita 30, da tsabar kudi da suka kai Naira miliyan 4.35.

Binciken farko ya nuna cewa ’yan ta’addan sun bukaci naira miliyan 2 da wayoyi biyu a matsayin kudin fansa ga dan uwan ​​wadanda suka kama kafin sojojin su kai dauki.

Laftanar Kanar Uba ya tabbatar da cewa ana ci gaba da gudanar da ayyuka matsin lamba kan ’yan ta’addan tare da hana su sakat.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Labarin Xinjiang A Zane: Aikin Yawon Shakatawa Na Kara Samar Da Arziki Ga Al’ummar Xinjiang
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 9, sun kwato kudin fansa a Borno
  • Kasar Sin Ta Kare Matakinta Na Takaita Fitar Da Ma’adanan Farin Karfe Na Rare Earth
  • Mutane A Fadin Duniya Sun Soki Ayyukan Neman ‘Yancin Kan Taiwan
  • Zuwa Kofin Duniya: Za A Yi Ta Ta Kare A Nahiyar Afirka
  • Rashin Amincewa Da Kasashen Yamma Yana Haifar Da Sabon Tunani Kan Huldar Kasa Da Kasa
  • Masana Sun Bayyana Yadda Za A Magance Ficewar Kamfanoni Da Masana’antu Daga Nijeriya
  • Kungiyoyin Falasdinawa Sun Fitar Da Sanarwar Hadin Gwiwa Kan Tsagaita Bude Wuta A Gaza
  • Birnin Tarayya Zai Taimaka Da Tara Kudin Shiga Daga Fannin Da Bai Shafi Mai Ba — Dantsoho
  • Putin: Natanyahu Yan Son Warware Matsaloli Da Iran Cikin Lumana Ba Tare Da Yaki Ba