Ma’aikatar Kasuwanci: Sanarwar Da Sin Da Amurka Suka Fitar Muhimmin Mataki Ne Na Warware Sabaninsu
Published: 12th, May 2025 GMT
A yau Litinin, mai magana da yawun ma’aikatar kasuwancin kasar Sin ya bayyana cewa, Sin da Amurka sun cimma matsaya tare da fitar da sanarwar hadin gwiwa bayan taron kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin kasashen biyu, inda ya kara da cewa, hakan wani muhimmin mataki ne da bangarorin biyu suka dauka na warware sabaninsu ta hanyar yin shawarwari da tuntuba bisa daidaito, tare da aza tubali da samar da yanayi na kara dinke baraka da zurfafa hadin gwiwa.
Daga bangarenta kuwa, Darakta-Janar ta Hukumar Kasuwanci ta Duniya (WTO) Ngozi Okonjo-Iweala, a jiya Lahadi ta bayyana cewa, ta yi farin cikin ganin an samu sakamako mai kyau yayin taron kolin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka.
A cikin wata sanarwa da ta fitar, Okonjo-Iweala ta ce tattaunawar ta nuna wani muhimmin mataki na ci gaba, inda ta kara da cewa bisa halin da ake ciki a duniya, irin wannan ci gaba da aka samu na da matukar muhimmanci ba ga kasashen biyu kadai ba, har ma da sauran kasashen duniya, ciki har da kasashe masu fama da matsalar tattalin arziki. (Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Direba ɗaya ya tsira a hatsarin tankokin dakon iskar gas a Zariya
A safiyar wannan Litinin ɗin ce aka wayi gari da wani mummunan hatsarin tankoki biyu na dakon iskar gas a Zariya, inda direba ɗaya kacal ya tsira da rai, yayin da wasu da dama suka ƙone ƙurmus.
Shaidun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe tara na safe, a kusa da shatale-talen Jirgin Sama Mota da ke titin Kaduna zuwa Zariya, daura da sabuwar Kasuwar Ɗan Magaji.
An kama mutumin da ake zargi da kashe jami’in sibil difens a Jigawa Ya ba wa alaramma kyautar motarsa saboda daɗin karatun Alkur’aniRahotanni sun nuna cewa motocin biyu sun gogi juna ne yayin da ɗaya ke ƙoƙarin wuce ɗaya, lamarin da ya haddasa kamawar wuta nan take.
An ji wata ƙara mai ƙarfi da ta tashi a lokacin haɗarin, lamarin da ya tayar da hankalin mazauna yankin.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, mutane da dama sun yi ta tserewa daga gidajensu domin guje wa abin da ka iya zuwa ya komo, yayin da kuma hayaƙi mai yawa ya mamaye hanyar da ya daƙile zirga-zirgar ababen hawa.
Jami’an tsaro da na kashe gobara sun kai ɗauki wurin domin ceto mutane, amma ƙarfin wutar ya hana su samun damar kaiwa kan motocin.
Shugaban Sashen Kula da Hatsari na Ƙasa (FRSC) reshen Zariya, Nasir Abdullahi Falgore, ya bayyana cewa hatsarin ya faru ne sakamakon goguwar motocin dakon gas ɗin biyu, saɓanin raɗe-raɗin cewa tsautsayin ya rutsa da wasu ƙananan motoci ƙirar Golf.
“Direban ɗaya daga cikin motocin ya tsira, kuma mun kai shi asibiti domin samun kulawa. Shi kaɗai ne zai iya ba da cikakken bayani idan ya samu sauƙi,” inji Falgore.
Shugaban Ƙungiyar Direbobi a Zariya, Malam Sa’idu Haruna, ya bayyana cewa ana yawan samun hatsari a wurin saboda yanayin kwana da titin yake da shi.
“Kusan duk wata biyu zuwa uku sai an sami hatsari a nan. Muna kira ga hukumomi su kawo ɗauki,” inji shi.
Haka kuma, shugaban bayar da agajin gaggawa na ƙaramar hukumar Sabon Gari, Abdul Malik Aminu, tare da na Zariya, Abdul’muminu Adamu, sun tabbatar da cewa ba a gama tantance adadin mutanen da suka rasu ba saboda akwai fasinjoji a motocin da ba a gano su ba tukuna.
DPO na ofishin Ɗan Magaji, CSP Auwalu A. Sani, ya ce aikinsu shi ne sanya ido don kare rayukan masu wucewa, amma bai bayar da ƙarin bayani kan hatsarin ba.