Tsohon Shugaban Google: Deepseek Ya Kawo Muhimmin Sauyi A Bangaren AI
Published: 30th, January 2025 GMT
Tsohon shugaban kamfanin Google Eric Schmidt, ya bayyana bullar kamfanin DeepSeek na Sin a matsayin wadda ta kawo muhimmin sauyi ga takara a fagen kirkirarriyar basira ta AI a duniya.
Wannan na kunshe ne cikin wani sharhi da jaridar Washington ta wallafa ranar Talata, inda Eric Schmidt ya jaddada cewa, karfin Sin na yin takara da manyan kamfanonin fasaha ba tare da amfani da albarkatu mai yawa ba, ya nuna bukatar da Amurka ke da ita ta karfafa karfinta a bangaren.
DeepSeek kamfanin Sin ne dake mayar da hankali kan kirkirarriyar basira ta AI, wanda aka kafa a shekarar 2023. A cikin wannan watan na Junairun, kamfanin ya fitar da sabon samfurin AI mai suna DeepSeek-R1, wanda ya ja hankali sosai saboda kaifin basirarta. Aikin wannan sabon samfurin AI ya kai matsayin takara da tsare-tsaren AI kamar su ChatGPT na OpenAI, kuma an samar da shi ne kan farashi mai rahusa da bai kai na abokan takararsa ba.
Kaddamar da DeepSeek-R1 ya girgiza masa’antar fasahar zamani, lamarin da ya haifar da saukar farashin hannayen jari manyan kamfanonin fasaha kamar Microsoft da Meta da Nvidia. (Mai fassara: Fa’iza Mustapha
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamna Lawal Ya Naɗa Sabon Sarkin Gusau
Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya amince da naɗa Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello a matsayin sabon Sarkin Gusau kuma Sarkin Katsina na Masarautar Gusau.
Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Malam Abubakar Mohammad Nakwada ne ya sanar da hakan, inda ya bayyana cewa an yi naɗin ne bisa ga shawarwarin da masu zaɓen sarakuna na masarautar Gusau suka bayar, tare da bin al’ada da dokokin da suka dace.
A wata sanarwa da mai taimakawa na musamman kan harkokin yaɗa labarai a ofishin Sakataren Gwamnatin Jihar Zamfara, Sulaiman Ahmad Tudu, ya fitar, ya ce sabon Sarkin, Alhaji Abdulkadir Ibrahim Bello, shi ne ɗa na farko ga marigayi Sarki, kuma kafin naɗin nasa yana riƙe da mukamin Bunun Gusau.
Alhaji Abdulkadir ya hau karagar mulki a matsayin Sarkin Gusau na 16, bayan rasuwar mahaifinsa, Mai Martaba Dokta Ibrahim Bello, wanda ya rasu a ranar 25 ga Yulin 2025, bayan shafe shekara goma yana mulki.
Yayin da yake taya sabon sarkin murna, Gwamna Lawal ya bukace shi da ya ci gaba da rike kyakkyawar jagoranci da mutumtaka da aka san kakanninsa da shi, musamman kasancewarsa tsatson Malam Sambo Dan Ashafa.
Gwamnan ya kuma bukaci sabon Sarkin da ya kasance jajirtacce wajen kawo haɗin kai, zaman lafiya da cigaba, tare da ƙarfafa hadin kai a ciki da wajen masarautar Gusau.
Daga Aminu Dalhatu