2025-08-04@15:59:40 GMT
إجمالي نتائج البحث: 4401

«ya haifar da»:

    Gwamnatin Kano ta bayyana shirin mayar da tsohon gidan yarin nan na Kurmawa, wanda aka gina fiye da shekara 100 da suka gabata, zuwa gidan adana abubuwan tarihi. Gidan yarin Kurmawa mai ɗaukar fursunoni 690 kacal, wanda aka gina a shekarar 1910 tun a zamanin Turawan mulkin mallaka a kusa da fadar mai martaba Sarkin Kano, yana da tarihin shekaru 115. An sace jariri sabuwar haihuwa a asibitin Ekiti Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet Mai ba Gwamnan Kano shawara kan harkokin yaɗa labarai, Ibrahim Adam, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Lahadi. Hadimin gwamnan ya ce an yanke shawarar sauya ma’anar wurin,...
    An nemi wani jariri sabuwar haihuwa an rasa a Cibiyar Lafiya ta Okeyinmi da ke Ado-Ekiti, babban birnin Jihar Ekiti, a ranar Litinin. Wani ganau ya ce an gano ɓatan jaririn ne lokacin da ma’aikatan jinyar da ke bakin aiki suka je su duba lafiyarsa da safiyar wannan Litinin ɗin. Za a samu ruwan sama kamar da bakin ƙwarya na kwanaki uku a faɗin Nijeriya — NiMet Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura Lamarin na ba-zato-ba-tsammani ya haifar da fargaba musamman yadda ɗimauta uwar jaririn da kuma wasu daga cikin mutanen da ke cikin harabar asibitin. Tuni dai an garzaya da ma’aikatan da ke kula da ɗakin haihuwa da uwar jaririn da mai gadi...
    Sakamakon wannan mummunan ta’annuti, Mataimakin Gwamnan ya jagoranci wata ƙaƙƙarfar tawaga, wacce ta haɗa manyan ma’aikatan gwamnati da jami’an tsaro zuwa Banga da sauran wurare uku da waɗannan hare-hare ya shafa, don a jajanta masu, tare da ba su tallafi na abinci da kuɗaɗe.   Mataimakin Gwamnan ya kuma tabbatar wa da waɗannan al’ummu cewa gwamnatin na nan tana duk abin da za ta iya yi don kawo dawwamammen zaman lafiya a yankin.   Lokacin da ya ke mayar da jawabi, shugaban Ƙaramar Hukumar Ƙauran Namoda, Manir Haidara ya yaba da ƙoƙarin gwamnatin jihar na ganin ta samar da tsaro a duk faɗin jihar Zamfara. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin...
    Hukumar Hasashen Yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta yi gargaɗin cewa za a yi ruwan sama kamar da bakin ƙwarya da tsawa na kwaki uku a faɗin ƙasar daga ranar Litinin. NiMet ta fitar da wannan hasashen ne ranar Lahadi a Abuja, lamarin da ke ƙara barazanar ambaliya a wasu jihohin ƙasar. Shirin kashe N712bn kan gyaran filin jirgin Legas ya tayar da ƙura Najeriya na hasashen samun N300bn a shekara daga noman dabino Hasashen na zuwa ne bayan ruwan sama ya lalata gidaje kimanin 50 da gonaki da wuraren ibada a Jihar Filato. Hukumar ta yi hasashen cewa za a yi tsawa da ruwan sama a jihohin arewacin ƙasar da suka haɗa da Adamawa da Taraba da Sakkwato da Kebbi...
    Shirin Makon Kiwon Lafiyar Uwa da Ɗa (MNCH) a Karamar Hukumar Gwarzo ta Jihar Kano ya samu gagarumar nasara, inda mata da yara da dama suka amfana da ayyukan kiwon lafiya kyauta iri-iri. Wannan kamfen na mako guda, wanda Gwamnatin Jihar Kano tare da haɗin gwiwar UNICEF da sauran abokan hulɗa suka tallafa masa, na da nufin inganta lafiyar mata da yara tare da rage mace-macen da za a iya kauce wa ta hanyar samar da dama ga ayyukan kiwon lafiya. Cibiyoyin lafiya a fadin karamar hukumar, ciki har da Asibitin Gwamnati na Gwarzo da Asibitin ‘Yar Kasuwa, sun bayar da rigakafi kyauta, shawarwari kan abinci mai gina jiki, kulawar haihuwa da sauran muhimman ayyuka na kiwon lafiya. Jami’in...
    Gwamnan jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni ya tuhumi sabon Sarkin Gudi, Alhaji Ismaila Ahmed Gadaka da ya jagoranci zaman lafiya, hadin kai, da ci gaban al’ummar masarautar sa, jiha da kasa baki daya. Gwamna Buni ya yi wannan kiran ne a ranar Litinin yayin gabatar da takardar nadin sarauta ga basaraken a hukumance a majalisar masarautar Gudi. Gina Tituna A Karkara Yana Bunkasa Tattalin Arziki – Gwamna Sule Wasu Kungiyoyi Sun Yi Kira Ga Dan Majalisa Aminu Sani Jaji Ya Fito Takarar Gwamnan Zamfara  Kwamishinan ilimi mai zurfi, kimiyya da fasaha na jihar, Farfesa Muhammad Bello Kawuwa ne ya mika takardar nadin ga sabon sarkin a madadin gwamnan. Da yake isar da sakon Gwamnan, Farfesa Kawuwa ya bayyana muhimmiyar...
    Shugaban kungiyar malaman addinin musulunci ko –Council Of Ulema-na Tafawa Balewa a jihar Bauchi na tarayyar Najeriya Sheikh Dan’azuki Musa tafawa balewa, yayi kira ga kasashen musulmi da kuma sauran kasashen duniya da su dauki darasi a jajircewar JMI da turjiyarta ga HKI, a kuma matsayin hanya tilo ta kawo karshen HKI. Kamfanin dillancin labaran Iran Press ko IP na kasar Sheikh Dan’azumi yana fadar haka a lokacinda yayi hira da shi a Bauchi. Sheikh Dan’azumi ya kara dacewa , gwamnatin Amurka ce bayan dukkan ayyukan ta’addancin da HKI take aikatwa a Gaza. Ya ce kafin yakin kwanaki 12 da HKI ta kallafawa JMI, musulmi sun debe kauna da samun mafita ga matsalar al-ummar Palasdinu wacce aka dade ana fama...
    Akalla mutane 11 ne aka kashe a harin da wasu ‘yan bindiga suka kai a unguwannin Kagara da San-Isa da ke karamar hukumar Kaura-Namoda a jihar Zamfara. Majiyoyi daga yankunan biyu sun shaida wa wakilinmu cewa an kai hare-haren ne a unguwannin Kagara da San-Isa tare da wasu kauyukan da ke kewaye. Waɗanne Ƙasashe Ne Suka Amince Da Kafa Ƙasar Falasɗinu? Sanata Shehu Buba Ya Ƙaddamar Da Rabon Taki Da Rigakafin Shanu A Bauchi Wata majiya daga dan garin Kagara wanda ya bayyana sunansa da Abubakar Sani ya shaidawa LEADERSHIP cewa ya rasa ‘yan uwansa guda biyu a harin wanda ya afku a ranar Asabar din da ta gabata. Ya ce, ‘yan fashin da suka yiwa kauyen su kawanya da...
    Tawagar ƴan wasan kwando na matan Najeriya ta lashe gasar ƙwallon kwando ta Afirka karo biyar a jere, lamarin da ya sa ta kafar tarihin wannan bajinta a Afirka. Tawagar D’Tigress ta samu nasara ne a wasan ƙarshe bayan doke Mali da ci 78-64 domin ɗaukar kofin gasar karo na bakwai a tarihi. Ƴan wasan Najeriyar sun kankane gasar ƙwallon kwandon Afirka, inda suka yi nasara sau 29 a jere a duka wasan da suka buga ba tare da rashin nasara ba tun 2015. Nasarar D’Tigress na zuwa ne kimanin mako guda bayan da tawagar Super Falcons ta ƴan wasan ƙwallon kafar matan Najeriya ta lashe gasar ƙwallon ƙafar matan Afirka, karo na 10 a tarihi.
    Majalisar zartaswar jihar Sokoto a karkashin jagorancin Gwamna Ahmed Aliyu ta amince da kashe kudade wajen ayyuka a sassa daban daban nufin tabbatar da amana da aka dora wa gwamnati.   Da yake karin haske ga manema labarai yayin taron da ya saba gudanarwa, kwamishinan yada labarai Alh. Sambo Bello Danchadi ya ce majalisar ta amince da bayar da kwangilar gina dakin kwanan dalibai mai hawa daya a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, da za a kasha naira miliyan dari hudu da tamanin da bakwai.   Alhaji Sambo Bello Danchadi ya ce majalisar ta kuma amince da gyaran sashen da aka kona na gidan talabijin ta Najeriya NTA Sokoto wanda kudinsa ya kai naira miliyan dari biyu da casa’in....
    Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Gusau/Tsafe ta tarayya Kabiru Amadu (wanda aka fi sani da Mai Palace) ya shirya taron addu’a na musamman ga jihar Zamfara da Najeriya baki daya, domin neman zaman lafiya da cigaba mai dorewa.   Taron addu’o’in wanda ya gudana a babban masallacin Juma’a na Tudun Wada da ke Gusau, ya hada malaman addinin Musulunci, da sarakunan gargajiya, da masu ruwa da tsaki a harkokin siyasa, da kuma daruruwan al’ummar jihar baki daya, duk sun ba da hadin kai wajen ganin an samar da zaman lafiya mai dorewa a jihar.   A nasa jawabin, Kabiru Mai Palace, ya bayyana taron a matsayin wani shiri na ruhi da nufin neman taimakon Allah wajen magance matsalar rashin...
    Amincewar Gwamnatin Tarayya da kashe Naira biliyan 712 biliyan don gyaran Filin Jirgin Sama na Murtala Muhammed da ke Legas ya haifar da ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya. Wannan gagarumin kashe kuɗi, da Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da shi a ranar Alhamis da ta gabata, ya sanya masana harkar jiragen sama, ’yan adawa, da kuma jama’ar ƙasa yin tambayoyi game da buƙatarsa, tsadarsa, da kuma inda za a samo kuɗin. Masu suka suna nuna yadda kuɗin ya yi yawa, har ya ninka kuɗin da aka ware wa Ma’aikatar Sufurin Jiragen Sama a kasafin kuɗin 2025 har sau goma. Hasali ma aikin ba ya cikin kasafin 2025. Wannan ya sa wasu ke kiran aikin a matsayin “almubazaranci,” musamman ganin halin...
    Gwamnatin Najeriya ta ce tana sa ran samun kimanin Naira biliyan 300 a duk shekara daga noman dabino a ƙasar. Ta ce tana fatan samun wannan kuɗaɗen shiga ne daga rabon irin dabino guda miliyan biyar da ta samar ga manoma a wannan shekara ta 2025. Darakta-Janar na Hukumar Yaƙi da Kwararowar Hamada (NAGGW), Alhaji Saleh Abubakar, ya ce, “Kowane iri ƙwaya ɗaya na iya samar da miliyan 100 na dabino, wanda kuɗinsa ya kai Naira miliyan ɗaya. Ga shi kuma sau biyu dabino ke yin ’ya’ya a shekara. “Muna hasashen manoma za su samar da Naira biliyan 300, wanda tabbas zai bunƙasa tattalin arzikin Najeriya,” in ji shi. Ya ƙara da cewa hukumar za ta raba irin dabino miliyan...
    Majalisar Dinkin Duniya ta fitar da wani kakkausar gargadi kan matsalar ruwan sha da ke kara kamari a zirin Gaza, inda ta bayyana cewa yunwa na ci gaba da rataya a kan al’ummar da ke kara hana samun tsaftataccen ruwan sha da tsaftar muhalli. A cikin wani sabon rahoto, MDD ta ce kashi 96% na iyalai a Gaza na fuskantar matsalar rashin ruwa, yayin da kashi 90% na al’ummar kasar ba su da tsaftataccen ruwan sha. Ya kara da cewa kashi 75 cikin 100 na mazauna garin suna kokawa wajen shiga bandaki, lamarin da ke kara tabarbarewar bala’in jin kai a cikin ci gaba da kawanya da kuma ta’addancin Isra’ila na tsawon watanni Tun da farko, ofishin kare hakkin bil...
    Gwamnatin Jihar Jigawa ta sake jaddada kudirin ta na kare al’umma daga ambaliyar ruwa kamar yadda hukumar hasashen yanayi ta kasa ta yi hasashen samu a wasu kananan hukumomin jihar a daminar bana. Mataimakin Shugaban kwamitin fasaha kan magance ambaliya, kuma mai bai wa Gwamna Umar Namadi shawara kan ambaliya da kuma sauyin yanayi, Alhaji Hamza Muhammad Hadejia ya bayyana haka yayin da yake duba aikin jingar ruwan kogi da ya ratsa garuruwan Auyo da Tsidir da Agin da Matsa da Sorakin da Jiyan da Tage da Turabu da kuma Tandanu. Alhaji Hamza Hadejia ya ce daga zuwan Gwamna Umar Namadi kan karagar mulkin Jihar, ya dauki kwararan matakai don kaucewa ambaliyar ruwa, domin kare rayuka da dukiyoyin al’umma. Ya...
    Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun bayyana cewa: Masu shirin halaka Gaza suna neman hadiye duniyar Musulunci  ne Dakarun kare juyin juya halin Musulunci nanIran sun yi gargadin cewa; Bangarorin da ke shirya kisan kiyashi a Gaza ba wai kawai halakar al’ummar Falastinu ba ne kawai, a’a suna neman mamaye yankuna masu arziki da muhimmanci na duniyar Musulunci ne a wani bangare na ci gaba da fadada ayyukan da suka shafi tsaro da albarkatun kasa. Dakarun kare juyin juya halin na Musuluncin sun bayyana a cikin wata sanarwa cewa: Tsayin daka da gwagwarmayar da al’ummar Falastinu suke yi a yau a zirin Gaza wajen fuskantar kisan kare dangi da laifukan yahudawan sahayoniyya, wata shaida ce da ke...
    A cewar sanarwar, AIHS za ta taimaka wajen haɓaka tambarin dangote da haɓaka dabarun haɗin gwiwa tare da masu ruwa da tsaki. Kodinetan shirin Barista Festus Adebayo ya shaida wa manema labarai cewa, za a iya cike giɓin gidaje a ƙasar ta hanyar haɗin gwiwar Haɗin kan Jama’a masu zaman kansu (PPP). Ya ce: “Kwarewa da haɗin gwiwa su ne manyan abubuwan da muka a gaba, idan aka yi la’akari da saurin ci gaban fasaha a cikin gine-ginen gidaje, samar da kudaɗe da kuma inganta tsarin.” Ya ce taken taron na wannan shekara, Maimaita Gidaje Ta Hanyar Sabuntawa, wanda daidai yake da ainihin darajar kamfanin. Barista Adebayo ya ce yana da ƙwarin gwiwar cewa haɗin gwiwa da kamfanin Simintin dangote...
    Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya ƙaddamar da babban shirin dashen bishiyoyi miliyan biyar a shekarar 2025. An fara dashen ne yankin Yanbawa da ke Ƙaramar Hukumar Makoda. Sake zaɓen Tinubu zai lalata makomar Najeriya — El-Rufai  Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi Gwamnan ya ce wannan shiri na nufin yaƙi da sauyin yanayi, farfaɗo da ƙasar da ta lalace, da kuma kare muhalli. Ya ce an fara dashen bishiyoyin a wannan fili tun shekarar 1972, amma aka bari ya lalace. Yanzu gwamnatinsa ta gyara shi don ya taimaka wajen shawo kan matsalolin fari da sauyin yanayi. Ya ƙara da cewa wannan shiri yana daga cikin ayyukan muhalli da gwamnatinsa ta aiwatar cikin shekara guda....
    Ma’aikatan agajin gaggawa a lardin Hebei na arewacin kasar Sin da ambaliya ta aukawa, sun karfafa kokarin gyara tituna da gadojin da suka lalace, domin tabbatar da isar da kayayyakin agaji da na aikin ceto ba tare da tangarda ba. Ruwan sama dake ci gaba da sauka a kwanakin baya-bayan nan ya haifar da ambaliya da zaftarewar kasa a fadin lardin, lamarin da ya rutsa da gundumomi da dama. Zuwa safiyar jiya Asabar, an dawo da zirga-zirga a sassan tituna 961 dake fadin lardin Hebei. (Fa’iza Mustapha) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki...
    Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, ya ce idan Shugaba Bola Ahmed Tinubu da jam’iyyar APC suka sake lashe zaɓe a 2027, hakan zai lalata makomar ’yan Najeriya. El-Rufai, ya faɗi haka ne a Jihar Sakkwato yayin wani gangamin wayar da kan jama’a da jam’iyyar adawa ta ADC, ta shirya. Gwamnan Yobe ya naɗa Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba Ya ce yana goyon bayan wannan haɗaka, kuma zai taimaka wajen ganin ’yan Najeriya sun sauke APC daga kan mulki. “Idan muka bar wannan gwamnati ta ci gaba da mulki zuwa karo na biyu, ragowar abin da ya rage na haɗin kai da amincewa tsakanin ‘yan Najeriya zai lalace. “Ƙasar...
    Gargaɗin ya yi daidai da irin wannan sanarwar da ofisoshin jakadancin Amurka a Jamaica da Uganda suka fitar kwanan nan, a wani ɓangare na yaƙi da dabi’ar karya ƙa’ida shige da fice.  A cikin watan Janairun 2025, hukumomin Amurka sun sake jaddada aniyarsu na ƙarfafa ikon kula da iyakoki kan yin amfani da damar zama dan ƙasa ta haihuwa. A farkon wannan shekara, shugaban ƙasar ɗonald Trump ya sake nanata matsayinsa na cewa yaran da aka haifa a Amurka ga baƙin haure ba su da takardun zama ƴan ƙasa kai tsaye. A bisa dokar da aka yi wa kwaskwarima na Amurka kan shaidar zama dan ƙasa, ta fayyace cewa duk wani jaririn da aka haifa sai an duba matakin damar...
    Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni, ya amince da naɗa Hon. Ismaila Ahmed Gadaka a matsayin sabon Sarkin Gudi, bayan rasuwar Alhaji Isa Bunuwa Madugu Ibn Kaji. Sabon Sarkin na Gudi, Ismaila Ahmed Gadaka, ya shahara da ƙwarewa a fannoni da dama. Sojoji sun ceto malamin Jami’a da aka sace a Taraba Ma’aikatan jinya sun dakatar da yajin aiki a faɗin Najeriya Ya taɓa zama ɗan majalisar wakilai mai wakiltar Fika/Fune daga 2011 zuwa 2019, kuma kafin nan ya yi aiki a matsayin Kwamishina a Jihar Yobe daga 2007 zuwa 2010. Gadaka, ƙwararren ma’aikacin banki ne, inda ya yi aiki da bankuna irin su UBA da Standard Trust Bank, inda ya kai matsayin Manajan Kasuwanci. Kafin naɗa shi Sarki, ya...
    Rundunar Sojin Najeriya tare da haɗin gwiwar jami’an Hukumar DSS sun ceto Injiniya Joshua Saleh, wani malami a Jami’ar Taraba, wanda ’yan bindiga suka sace. An sace malamin ne a ranar 31 ga watan Yuli, 2025, a hanyar Chinkai–Kente zuwa Wukari, da ke Ƙaramar Hukumar Wukari a Jihar Taraba. Sai an samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu za mu ajiye makamai — Hamas An ƙara hakimai 6 a Masarautar Katsina Bayan samun sahihan bayanai, sojoji da DSS suka fara bincike tare da ƙoƙarin ceto shi a wurare da dama, ciki har da Kente, Sondi 1 da 2, Yaku, da Warawa. A cewar Laftanar Umar Muhammed, mai magana da yawun rundunar, sojojin sun yi arangama da ’yan bindigar, inda suka yi musayar...
    Ministan harkokin wajen kasar Aran Abbas Aragchi ya bayyana cewa JMI da kuma kasar Japan suna iya jagorantar kasashen duniya zuwa ga rabata daga makaman kare dangi. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Ministan yana fadar haka a wani rubutu da yayi, wanda kuma aka buga a jaridar Asahi Shimbun ta kasar Japan. Ya kuma kara da cewa, kasashen biyu an yi amfani da makaman kare dangi a kansu. Y ace kamar yadda Amurka ta yi amfani da makaman nukliya kan kasar Japan a shekara ta 1945 a karshen yakin duniya na biyu, haka nan Sadam ya yi amfanin da makaman guba a kan iraniyawa a kallafeffen yakin da suka fafata na shekaru 8 a tsakaninsu. Arachi...
    Ƙungiyar Hamas ta sake jadadda matakinta na cewa ba za ta taɓa ajiye makami ba, har sai lokacin da duniya ta amince da samar da ’yantacciyar ƙasar Falasɗinu a yankin Gabas ta Tsakiya, wani abu da zai sake mayar da yarjejeniyar zaman lafiya da ake ƙoƙarin ƙullawa baya. A halin da ake ciki yanzu haka ana wata tattaunawa wadda ba ta kai tsaye ba tsakanin Isra’ila da Hamas don ƙulla yarjejeniyar tsagaita wuta ta kwanaki 60, da kuma sakin mutanen da ke riƙe a hannun ɓangarorin biyu. A Talatar da ta gabata ne ƙasahen Qatar da Masar suka sanar da matakin ƙasashen Saudi Arabiya da Faransa na goyon bayan samar da ƙasar Falasdinu, don tabbatar da dawamammen zaman lafiya a...
    Sojojin HKI sun kashe falasdinawa 62 daga safiyar jiya Asabar zuwa lokacin bada wannan labarin a yau Lahadi. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa mafi yawan wadanda aka kashen masu neman abainci ne, a cibiyoyin karban abincin wadanda HKI da Amurka suka kafa. Kafafen yada labarai daga asbitocin Gaza sun bayyana cewa a jiya Asabar yahudawan sun kashe mutane 38 masu neman abinci. Labarin ya kara da cewa, duk tare da sanarwar da gwamnatin HKI ta bayar na tsagaita wuta a wani bangar na zirin gaza, saboda bawa Falasdinawan dama samun agaji daga wasu wurare amma sojojin HK sun ci gaba da kashe Falasdinawan . Zuwa ranar jumma’an da ta gabata, sojojin yahudawan sun kashe Falasdinawa...
    Minista Idris ya bayyana damuwa da irin martanin da al’umma da masu ruwa da tsaki a harkar yaɗa labarai suka nuna dangane da lamarin. Amma ya jaddada cewa hukumar da ke da hurumin dakatar da lasisin gidajen rediyo da talabijin ita ce Hukumar Kula da Gidajen Radiyo da Talabijin ta Ƙasa (NBC), kamar yadda doka ta tanada.   Sanarwar da Gwamnatin Tarayya ta bayar kan lamarin ta ce: “Saboda haka, ministan yana maraba da matakin da Gwamnatin Jihar Neja ta ɗauka na kai koken da ta ke da shi kan zargin rashin ɗabi’a da Badeggi FM ta yi a hukumance zuwa ga NBC domin a warware batun.”   Idris ya roƙi dukkan ɓangarori da su kwantar da hankalin su, yana...
    Rundunar sojin Jamus ta fara gudanar da aikin jefa kayayyakin gaji da suka hada da abinci da magunguna ta sama a Zirin Gaza. Ma’aikatar Tsaron Jamus da ke Berlin, fadar gwamnatin kasar, ce ta tabbatar da hakan, inda ta ce jiragen rundunar sojin sama sun ajiye kunshin tallafi 34 dauki da tan 14 na abinci da kuma magunguna. Ambaliya: Mutum 165 sun mutu a Nijeriya a bana — NEMA Dadiyata: Buhari ya gaza nemo shi, Tinubu yana da lokaci — Amnesty Sai dai a cewar Ministan Tsaron Jamus, Moris Pistorius kai tallafi ta sama ba zai yi wani babban tasiri ba. A cewar Majalisar Dinkin Duniya, Zirin na bukatar tallafin tan dubu 62 na abinci a duk wata domin...
    “daidaita farashin ya kasance hanya daya tilo da za a iya amfani da ita wajen tafiyar da harkokin kasuwa da kuma tabbatar da gaskiya,” in ji shi. Edun ya nuna ƙalubale a tsarin biyan ciniki a Nijeriya, tare da lura da cewa har yanzu ana samun yawan hada-hadar kasuwanci ta hanyoyin da ba kamata ba. Ya bayyana cewa gwamnati na binciken gyare-gyare da nufin ƙara bayyana gaskiya, ciki har da yiwuwar gudanar da cinikin danyen mai daga ƙasashen waje da na naira. “Yawancin mu’amalar kasuwancinmu ana gudanar da su ne a waje da tashoshi na yau da kullun. Muna aiki kan gyare-gyaren da za su inganta tsarin,” in ji shi. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni...
    Ya danganta mutuwar ta ƙanana da matsakaitan sana’oi a ƙasar, kan rashin samun rancen kudaɗen da za su ci gaba da ka kasuwancin su da rashin kayan aiki, da rashin kasuwa da ba a samu sosai da kuma rashin gudanar da ingantaccen shiri, kafin su fara gudanar da kasuwancinsu. Ya sanar da cewa, ya zama wajibi, ƴan kasuwa musamman ƙanana da matsakaitan sana’oi a su sani cewa, bab wani batun yin wani holewa, na jin daɗi Ya bayyana cewa, sama da ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar nan, burin su ba shi ne, na ƙara yawan adadin alƙaluma ba, anna burin shi ne, na ƙarfafa zurewar kasuwancinsu. “Alƙaluma sun nuna cewa, akwai ƙanana da matsakaitan sana’oi 40 a ƙasar...
    Nijeriya, wadda take ta daya a jerin ƙasashen da suka fi iya ƙwallon mata a Afirka, ta zura ƙwallon da ta ba ta nasara ne a gab da tashi wasa a karawarta da Afirka ta Kudu a wasan kusa da na ƙarshe. A yanzu za a iya cewa Nijeriya ta cimma burinta na ‘Mission ɗ’, wato lashe kofin a karo na 10 a tarihi kuma ta ci gaba da jan zarenta na tawagar mata wadda babu kamarta a wannan nahiyar. Nijeriya ta ƙara kafa wani tarihin kasancewar ita ce ta farko da ta lashe sabon kofin na gasar bayan sauya shi da aka yi daga wanda aka saba amfani da shi a baya. A ƙarshen wasan Rasheedat Ajibade ta Nijeriya...
    Ƙungiyar kare haƙƙin ɗan Adam ta Amnesty International, ta ce Gwamnatin Tarayya ta yi sakaci game da ɓacewar ɗan gwagwarmaya Abubakar Idris, wanda aka fi sani da Dadiyata. A wata sanarwa da ta fitar, Amnesty, ta ce abin takaici ne ganin cewa shekara shida kenan da Dadiyata ya ɓace ba tare da wani sahihin bayani ba. Mutum ɗaya ya rasu, an jikkata wasu yayin arangama da ’yan sanda a Abuja Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja Dadiyata ya ɓace ne a ranar 2 ga watan Agustan 2019, bayan wasu mutane ɗauke da makamai sun shiga gidansa da ke unguwar Barnawa a Jihar Kaduna, suka tafi da shi. Tun daga wannan lokacin, iyalansa da abokansa ke jiran jin...
    “Kazalika sarkin ya bayyana cewa, mun kuma duba yanayinmu. Me muke da shi? Me za mu iya yi? Me ya kamata mu yi domin inganta rayuwar mutanenmu? Allah ya albarkaci ƙasarmu, ƙasa ce mai faɗi sosai, kuma ta dace da ayyukan noma. Mun kuma yi la’akari da fannin ilimi. Jihar Neja, an san tana gaba a fannin ilimi. To, kwatsam, sai wannan mataki ya samu tasgaro, yara ba su iya cin jarabawar WASC, zuwa makaranta ya yi ƙasa da ƙasa, ba a kula da malamai yadda ya kamata. Wasu makarantun ba su da malamai. Za ka ga makaranta mai yawan dalibai 300 tana da malami daya ko biyu, hakan ba abu ne mai yiwuwa ba,”in ji shi. Ya ci gaba...
    Wani fim mai suna “Dead to Rights”, wanda aka shirya game da kisan kiyashin da aka yi a birnin Nanjing, ya mamaye kasuwar fina-finai ta lokacin zafi ta kasar Sin, inda kudin shigar da aka samu da shi ya zarce yuan biliyan daya, kwatankwacin dalar Amurka miliyan 140 cikin kwanaki takwas kacal. Wanda aka yi amfani da ingantattun shaidun hotuna na ta’asar yakin da Japanawa suka aikata a lokacin kisan kiyashin Nanjing, Fim din na “Dead to Rights” ya ba da labari ne na wani rukunin fararen hula na kasar Sin da suka nemi mafaka a dakin daukar hoto a lokacin muguwar mamayar da azzaluman Japanawa suka yi a birnin Nanjing. A wani yunkuri na neman tsira da rayukansu hajaran-majaran,...
    A’isha ƴar shekara uku da suke zaune a ƙarƙashin inuwar bishiyar ɗogoyaro a wani ƙauye mai nisa a yankin Arewa maso Gabas (sansanin gudun hijira). Babu takalmi a ƙafarta, ta yi shiru, saboda radaɗi da take ji. ƙafafuwanta sirara sun yi rauni, cikinta ya dan kumbura saboda yunwa, idanunta sun fito tana cikin halin da bai kamata a ce mai shekaru irinta na ciki ba. Aisha Abdullahi ba ta iya yin kuka ba, domin babu ƙarfin halin yin hakan Mahaifiyarta, Maryam Abdullahi, tana girgiza ta a hankali a cinyarta, ta hada man gero mai ruwa da dakakken ganye a cikin wani ƙaramar roba. Abincin da suke ci a cikin kwana biyu. Ta shaida wa LEAɗERSHIP Weekend cewa, “wani lokaci ta...
    Fiye da shekaru goma da suka gabata, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya dora samun ci gaba marar gurbata muhalli a matsayin wata muhimmiyar manufar raya kasa. Ya taba fitar da manufar raya kasa ta hanyar bayar da muhimmnci ga “Muhalli”, wadda ta yi nuni da cewa ingantaccen yanayin muhalli abu ne mai matukar daraja don samun ci gaba. Tun daga wannan lokacin, kasar Sin ta ci gaba da yin sauye-sauye masu kiyaye muhalli, inda ta zama kasa mafi girma a duniya wajen kera batir na lithium da motocin masu amfani da lantarki. Game da hakan, a yayin da ake tattaunawa da Jorge Moreira da Silvas, babban darektan ofishin kula da ayyuka na MDD, a wani shiri mai suna “Leaders Talk” da...
    Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Suna fatan haɓakar musayar kasuwanci tsakanin Iran da Pakistan ta haura dala biliyan 10 Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya bar birnin Tehran a wannan ranar Asabar din zuwa Islamabad na Pakistan a wata ziyarar aiki a kasar bisa gayyatar da fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif ya yi masa. Shugaba Pezeshkian a cikin wata sanarwa da ya fitar kafin ya bar Tehran ya ce: “Zasu ziyarci Pakistan ne tare da tawaga bisa gayyatar da dan uwansu fira ministan Pakistan Shehbaz Sharif ya yi musu.” Ya kara da cewa: “Akwai kyakykyawar dangantaka, mai karfi da kuma zurfafa a tsakanin Iran da Pakistan. Wannan alakar ba ta shafi tattalin arziki, kimiyya, al’adu, masana’antu, da kan iyaka...
    Majalisar Dinkin Duniya ta yi gargadi game da barazanar kungiyoyin ta’addanci na ISIS da Al-Qaeda a nahiyar Afirka Wani sabon rahoto da kwararrun Majalisar Dinkin Duniya suka fitar ya yi gargadin karuwar barazanar da kungiyoyin ‘yan ta’adda ke da alaka da ISIS da Al-Qaeda suka yi kan kasashen nahiyar Afirka. Rahoton ya yi nuni da cewa: Nahiyar Afirka na fuskantar karuwar barazanar ayyukan ta’addanci da ba a taba ganin irinsa ba, yayin da wata gungun jama’a da take karkashin kungiyar al-Qaida ke ci gaba da fadada ikonta a arewacin Mali da Burkina Faso tare da samun ‘yancin kai, gami  da samun goyon bayan ayyukan ci gaba da suka hada da jiragen sama marasa matuka ciki da nau’o’in makamai na zamani....
    A yau Asabar, hukumar bayar da agajin gaggawa ta birnin Beijing ta sanar da cewa, an dawo da wutar lantarki da ayyukan sadarwa a dukkan kauyukan da ibtila’i ya shafa a fadin birnin na Beijing, biyo bayan mamakon ruwan sama da iska mai karfi da aka tafka, yayin da kuma ake ci gaba da aikin ceto wadanda suka bace. Ruwan sama da iska mai karfi da aka yi fama da shi daga ranar 23 zuwa 29 ga watan Yuli ya yi sanadin mutuwar mutane 44, yayin da mutane tara suka bace, a babban birnin kasar, kamar yadda aka sanar a wani taron manema labarai da aka gudanar a ranar Alhamis da ta gabata. Hukumar bayar da agajin gaggawa ta birnin...
    Ƙungiyar Ma’aikatan Jinya ta Najeriya (NANNM), ta dakatar da yajin aikin gargaɗi na kwanaki bakwai da ta fara a faɗin ƙasar nan. Ƙungiyar ta bayyana hakan ne cikin wata takarda da shugabanta ƙasa, Haruna Mamman, da sakatarenta, T.A. Shettima, suka sanya wa hannu. Rufe gidan rediyo ya haifar da cece-ku-ce a Neja Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa Sun fara yajin aikin ya fara ne a ranar Laraba tare da niyyar shafe kwanaki bakwai suna yin sa. Ma’aikatan jinyar sun shiga yajin aikin ne saboda ƙarancin albashi, ƙarancin ma’aikata, da kuma rashin ingantattun wuraren aiki. Wannan yajin aiki na zuwa ne a daidai lokacin da likitoci ke takun saƙa da gwamnati kan batutuwan suka shafi jin...
    Ce-ce-ku-ce ya ɓarke a Jihar Neja, bayan da Gwamna Mohammed Umaru Bago, ya bayar da umarnin rufe gidan rediyon Badeggi FM da ke Minna, Babban Birnin Jihar. Ya kuma umarci ’yan sanda da Kwamishinan Tsaron Cikin Gidan jihar su rufe tashar, tare da soke lasisinta. Jami’ar Umaru Yar’adua ta kori ɗalibai 57 kan satar jarabawa HOTUNA: Yadda aka yi Jana’izar Sarkin Gudi na Yobe bayan rasuwarsa a Abuja Ya kuma bayar da umarnin bincikar mai gidan rediyon, kan zarginsa da tayar da hankalin jama’a da kuma adawa da gwamnati. “Tashar na yaɗa kalaman tunzuri,” in ji mai magana da yawun gwamnan, Bologi Ibrahim. “Gwamna ya umarci jami’an tsaro su ɗauki mataki a kan gidan rediyon da kuma mamallakinsa.” Sai dai...
    Saboda haka, ƙarfin APC a zauren majalisar dattawa mai mambobi 109 ya kai 70, kujeru biyu kadai take buƙata ta cika 72 don samun rinjaye na kashi biyu cikin uku. PɗP yanzu haka tana da kujeru 28, yayin da jam’iyyar LP ke da biyar. Jam’iyyar SɗP na da kujeru biyu, yayin da jam’iyyar NNPP da APGA ke da kujeru guda daya kowannansu. A yanzu haka, akwai kujeru biyu na majalisar dattawa da babu kowa. Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa (INEC), har yanzu ba ta gudanar da zaɓen cire gurbin Sanata Ifeanyi Ubah, mai wakiltar Anambra ta kudu, wanda ya rasu a farkon wannan shekara, da Sanata Monday Okpebholo, mai wakiltar Edo ta tsakiyar, wanda ya bar kujerarsa bayan...
    “Saurayin nata ne ya kashe marigayiyar a ranar Talata kuma ya kulle ta a cikin dakinsa, maƙwabta ne suka ja hankalin daliban a lokacin da suka fahimci wani wari daga dakin. “Har yanzu ba mu san dalilin da ya sa saurayin ya kashe ta ba, dalibar tana sana’ar POS a yankin, amma tun ranar Talata, ta ɓace kuma babu wanda ya san inda take sai jiya, lokacin da maƙwabta suka ji wani wari daga dakin saurayinta. “Shi yaron, bayan sun kashe ta, ya tafi da cinikin da yi a wajen sana’ar ta ta POS. “Lokaci ya yi da gwamnatin jihar za ta yi wani abu game da kashe-kashen da ƴan asalin garin suke yi wa dalibanmu, idan ba a yi...
    Shugaban kasar Iran Masuod Pezeshkiya ya yi juyayin shahadar Isma’ila Haniyya marigayi shugaban kungiyar Hamasa a nan Tehran shekara guda kenen. Ya kuma jaddada cewa JMI ba za ta taba manta da shi ba. Tashar talabijin ta Presstv ta nakalto shugaban yana bayyana wannan juyayin a ranar da  Haniya yake cika shekara guda da shahada, sannan shahadarsa ya zo dai dai da ranar da Pezeshkiyan ya fara shugabancin kasar. Labarin ya kara da cewa shugaba Pezeshkiyan ya bayyana haka ne a shafinsa na X ya kuma kara da cewa a ranar da na fara aiki a matsayin shugaban kasa kenen, makiya HKI da kuma Amurka suka sanyamu cikin bakin ciki tare da kashe bakommu wanda ya zo ya taya mu...
    Masu zanga-zanga a duk fadin siriya sun bayyana rashin amincewarsu da ci gaba da kisan mabiya mazhabar Aalawiyya a bakin nruwan tekun medeteranin. Da kuma rikicn da ya kai ga zubar da jnin mutanen kasar a Sewaida saboda shishigin da HKI take yi a cikin al-amuran cikin gida na kasar. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kafafen yada labaran kasar suna fadar cewam dubban mutanene suka  fito suka kuma taru a babban dandalin da ke tsakaiyar suwaida inda suke kira ga gwamnatin rikon kwarya ta HTS ta janye yan ta’addan da ta tura zuwa yankin suwaida don kashe mutanen yankin. Masu zanga zangar suna dauke da alluna wadanda aka rubuta a kansa : a bude hanyoyi don...
    Kungiyar wasan Taekwondo ta JMI kuma guragu, sun zama zakara a wasan taekwondo gurago sun lashe gasar ta Asia karo na 10 a jere. Kanfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto cewa an gudanar da gasar ne a kasar Malasiya, kuma yan wasa 107 ne daga kasashe 18 suka sami damar halattar gasar a ranar Jumma’an da ta gabata. Alireza Bakht da Mamed Haqshenas da kuma Marzieh Nasrollah sun sami lambobin Zinari sannan  Saeed Sadeghianpour, Maryam Abdollahpour, da Amir mohammad Haghitshenas sune suka sami lambobin azurfa. A yayinda Aylar Jami, Leila Mirzaei, Mohammad Taha Hassanpour, Roza Ebrahimi, Leila Rahimi, da Mehdi Pourrahnama kuma suka sami lamabobin tagulla guda 6. Share 0 0 votes Article Rating Subscribe Login...
    An yi jana’izar Marigayi Sarkin Gudi da ke Jihar Yobe, Alhaji Isa Bunuwa Madugu Ibn Khaji, ranar Juma’a a Abuja, inda ya rasu a wani asibiti bayan fama da jinya. Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni ya ranar Juma’a ya jagoranci tawagar gwamnatin jihar wajen hakartar taron. Sanarwar da Mamman Mohammad daraktan yada labarai na gwamna Buni ya fitar ta ce, gwamnan da ke halartar wani taro a Abuja ya yanke ziyarar tasa domin halartar jana’izar marigayi Sarkin da kansa. Gwamna Buni ya samu rakiyar Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Yobe, Alhaji Chiroma Buba Mashio, Sanata Ibrahim  Mohammed Bomoi, Sanata Musa Mustapha, da ’yan Majalisar Wakilai. Sauran sun haɗa da sakataren gwamnatin jihar, Baba Malam Wali, ’yan majalisar dokokin jihar, da  kwamishinoni,...
    A bisa ƙiyasin da babban bankin Nijeriya (CBN) ya yi, ya ce; tumatirin da ake nomawa a   shekara a Nijeriya, ya kai kimanin tan miliyan 1.701, wanda kuma ake amfani da shi a shekara ya kai aƙalla tan 2.93, inda wannan adadin ya nuna cewa; a shekara, ana samun ƙarancinsa da ya kai na kimanin tan miiyan miliyan 1.2, inda kuma a duk shekara ake cike giɓin da ake da shi na wanda ake shigo da shi kimanin na ƙalla dala biliyan 2.5. Wani ƙiyasi da kamfanin ‘Reportlinker’ ya gudanar ya ce, buƙatar tumatir a shekara , za ta ƙaru zuwa tan miliyan 3.01 a 2028. Jerin Manyan ƙalubalen da Ke Shafar Farashin Tumatir A Nijeriya: 1- Noman Tumatir...
    Bincike a kan zargin da ake wa Hukumar Raya ƙasashe ta Amurka (USAID) da wasu ƙungiyoyi masu zaman kansu na cikin gida da na ƙasa da ƙasa game da tallafa wa ƙungiyoyin Boko Haram da ISWAP da sauran masu tayar da ƙayar baya a Nijeriya har yanzu bai kammala ba. Kawo yanzu babu wata ƙwaƙƙwarar hujja da aka gabatar da ke tabbatar da wannan zargi, wanda hakan ya sa binciken ya tsaya. Kimanin wata biyar ke nan da Majalisar Dattijai da Majalisar Wakilai na Nijeriya suka fara bincike kan zargin, amma har yanzu babu wani sakamako ko rahoto. Aminiya ta gano cewa tun sama da shekara goma da suka wuce, ake zargin wasu ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa da...
    Bankin Raya Ci-gaban Afirka (AfDB) ya amince da ba wa Gwamnatin Jihar Sakkwato bashin Naira biliyan 70.4 domin inganta fannin kiwon lafiya. Wannan shiri na da nufin bunƙasa fannin kiwon lafiya da ingancinsa, da kuma cike giɓin da ake da shi a ɓangaren a Jihar Sakkwato, a cewar AfDB ta bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a. Rahotanni na nuni da cewa, yaro ɗaya cikin kowane yara 20 ne akale yi wa allurar rigakafi cikakke a Jihar Sakkwato a, a yayin da adadin mutuwar jarirai ya kai 104 daga cikin 1,000 a Jihar. Ƙasa da kashi 14 cikin 100 na cibiyoyin lafiya a jihar ne suke da kayan aiki masu aiki, kuma likita ɗaya ne kawai ke kula da mutum...
    Bankin Raya Ci-gaban Afirka (AfDB) ya amince da ba wa Gwamnatin Jihar Sakkwato bashin Naira biliyan 70.4 domin inganta fannin kiwon lafiya. Wannan shiri na da nufin bunƙasa fannin kiwon lafiya da ingancinsa, da kuma cike giɓin da ake da shi a ɓangaren a Jihar Sakkwato, a cewar AfDB ta bayyana a cikin wata sanarwa ranar Juma’a. Rahotanni na nuni da cewa, yaro ɗaya cikin kowane yara 20 ne akale yi wa allurar rigakafi cikakke a Jihar Sakkwato a, a yayin da adadin mutuwar jarirai ya kai 104 daga cikin 1,000 a Jihar. Ƙasa da kashi 14 cikin 100 na cibiyoyin lafiya a jihar ne suke da kayan aiki masu aiki, kuma likita ɗaya ne kawai ke kula da mutum...
    Ministan harkokin wajen Iran Abbas Araghchi ya ce gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila na da burin kawo cikas ga harkokin tsaro a yankin, yana mai kira ga daukacin kasashen yankin da su yi taka tsantsan wajen tunkarar irin wannan makirci. Araghchi ya bayyana hakan ne a wata tattaunawa ta wayar tarho da mataimakin firaministan Hadaddiyar Daular Larabawa kuma ministan harkokin wajen kasar Sheikh Abdullah bin Zayed Al Nahyan a ranar Juma’a. Ministan na Iran ya ce gwamnatin Isra’ila ta saba da dabi’a ta  son kai da rashin bin doka da oda. Manyan jami’an diflomasiyyar Iran da na Hadaddiyar Daular Larabawa sun tattauna kan sabbin abubuwan da ke faruwa a yankin musamman halin da Falasdinu ke ciki. Har ila yau Araghchi da...
    A yanzu haka dai ratotannin sun tabbatar da cewa APC da ADC suna gogayya wajen neman samun goyon bayan mutanen arewa kafin babban zaɓen 2027 ya ƙariso. A ranar 1 ga Yuli, manyan ƴan adawa da suka hada da tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar da dan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP a 2023, Peter Obi da dan takarar shugaban ƙasa a APC a 2023, Rotimi Amaechi, da tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, sun gabatar da ADC a matsayin hadakar jam’iyyar adawa domin ƙalubalantar Tinubu a 2027. Shugabannin ADC sun ci gaba da yin ƙoƙari don samun goyon bayan mutanen arewacin Nijeriya da sauran yankuna tun bayan buɗe jam’iyyar. A taron, Mark ya buƙaci shugabannin arewacin Nijeriya da...
    Yau Jumma’a, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun ya gudanar da taron manema labarai na yau da kullum. Dangane da sanarwar da Amurka ta fitar ta kakaba takunkumi kan jami’an hukumar kare hakkin Falasdinawa da mambobin kungiyar ‘yantar da Falasdinu, Guo Jiakun ya bayyana cewa, Sin ta kadu da hakan, kuma tana nuna takaici da rashin fahimta cewa, Amurka ta yi watsi da kokarin da kasashen duniya ke yi na samar da zaman lafiya ga Falasdinu. Kuma kasar Sin ta dage wajen goyon bayan tsari mai adalci ta al’ummar Falasdinu don maido da halastaccen hakkin al’ummar, kuma za ta ci gaba da yin namijin kokari a wannan fanni tare da sauran kasashen duniya. Dangane da umarnin da shugaban...
    Shugaban jam’iyyar NNPP na Jihar Kano, Hashim Sulaiman Dungurawa, ya ce farin jinin jam’iyyar adawa ta PDP ya dusashe a jihar. Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake mayar da martanin da wasu jam’iyyun adawa suka yi, wajen zargin gwamnatin jihar da rashin bayyana yadda ta ke kashe kuɗaɗen da aka ware wa ilimi, lafiya, da gine-gine. Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya   Dungurawa, ya ce waɗannan zarge-zargen siyasa ce kawai, ba su da tushe ko makama. Ya ce waɗanda ke sukar gwamnati su ne suka gaza lokacin da suka yi mulki a Kano. “Da farko, muna gode musu da...
    Asusun kula da Ƙananan Yara na Majalisar Ɗinkin Duniya, UNICEF, ya ce Najeriya ce ƙasa ta biyu da aka fi samun ɓullar cutar kwalara a yammacin Afirka da tsakiyar Afirka. Darektan Hukumar UNICEF mai kula da yammacin Afirka da Afirka ta tsakiya, Gilles Fagninou  ne ya bayyana hakan tare da cewar annobar kwalara ta zama tamfar alaƙaƙai a Najeriya. Haɗarin tirela ya yi sanadin asarar awaki sama da 100 a Zariya Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya   “A cewarsa cutar Kwalara na ci gaba da yaɗuwa a Najeriya, inda ƙasar ke fama da ɓarkewar cutar a ‘yan shekarun nan.” “Ya zuwa ƙarshen watan Yuni, Najeriya ta samu adadin mutane 3,109 da ake zargin...
    A daren Juma’a ne dab da wayewar gari wata motar tirela ɗauke da awaki da kaji wadda ta taso daga Gwauron Dutse a Jihar Kano ta yi haɗari. Motar tirelar wadda take ɗauke da dakon awaki da kuma kwandunan kaji mai yawa a samanta baya ga mutane da ta ɗauko ta yi haɗarin a kusa da kasuwar Ɗan Magaji saman gadar da ke kan hanyar  Zariya zuwa Kaduna. Martani: Har yanzu muna ci gaba da yajin aiki — Ma’aikatan jinya   An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi Awaki kusan sama da 100  suka mutu da kuma kaji kusan ɗari 500 ne aka ƙeyasta sun mutu. Sai dai ba a sami asarar rai ko ɗaya...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran ya bayyana cewa: Matukar dai Trump ya bukaci dakatar da inganta sinadarin Uranium gaba daya a Iran, to ba za a cimma wata yarjejeniya ba Ministan harkokin wajen Iran Sayyid Abbas Araqchi ya jaddada a wata hira da jaridar Financial Times cewa: Iran na neman a biya ta diyya kan irin hasarar da ta yi a harin wuce gona da irin kwanaki 12 na ta’addanci kan kasarta. Araqchi ya yi nuni da bukatar Amurka ta bayyana dalilin da ya sa ta kai farmaki kan Iran a tsakiyar shawarwari tare da bayar da tabbacin cewa ba za a sake daukar irin wannan mataki ba. Araqchi ya kara da cewa, warware rikicin makamashin nukiliya na bukatar nemo...
    Kungiyar Ma’aikatan jinya da Ungozoma ta Ƙasa (NANNM) ta mayar wa da gwamnati martanin cewa har yanzu tana ci gaba da gudanar da yajin aikin da take yi. Ministan Lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Ali Pate, ne dai ya bayyana cewa ƙungiyar ta janye yajin aikin gargaɗin. An ceto mutum uku da aka yi garkuwa da su a Kebbi Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi Da yake magana da manema labarai bayan wani taron sirri da aka yi a Abuja ranar Juma’a, Pate ya ce matakin ya biyo bayan yarjejeniyoyin da gwamnati da shugabannin Ƙungiyar NANNM suka cimma ne. Amma da aka tuntuɓi shugaban Ƙungiyar na ƙasa, Morakinyo Rilwan ya ce ba gaskiya ba ne cewa an...
    Kasar Spain ta bayyana abin da ke faruwa a Gaza a matsayin abin kunya ga bil’adama Ministan harkokin wajen kasar Spain José Manuel Albares ya yi kira ga mahukuntan Isra’ila a ranar Alhamis da su bude mashigar ruwa na dindindin domin ba da damar kai agajin jin kai zuwa zirin Gaza, yana mai gargadin cewa; Bala’in jin kai a yankin da aka killace zai iya ta’azzara. A nasa jawabin Albares ya jaddada cewa: Gaza na fuskantar yunwa sakamakon killacewar da haramtacciyar  kasar Isra’ila ta mata, kuma abin da ke faruwa a wurin abin kunya ne ga bil’adama. Ya kara da cewa yunwa na ci gaba da lakume rayukan fararen hula a yankin a kowace rana. Ministan na Spain ya jaddada...
    Rundunar ’yan sandan Jihar Kebbi ta ce ta ceto wasu mutane uku da aka yi garkuwa da su, bayan sun yi artabu da wasu da ake zargin sun yi garkuwa da su a wani mummunan musayar wuta da aka yi a tsaunin Shanga. Waɗanda aka yi garkuwan da su sun haɗa da: Muhammad Nasamu Namata mai shekara 25, da Gide Namata mai shekara 20 da Hamidu Alhaji Namani mai shekara 35. INEC za ta fara rajistar ƙuri’a a ranar 18 ga Agusta Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansaninta a Kebbi An  yin garkuwa da su ne a safiyar ranar 27 ga watan Yuli, 2025, lokacin da masu garkuwa da mutane ɗauke da makamai suka mamaye ƙauyen Sangara da ke...
    Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta a Ƙaramar Hukumar Yauri ta Jihar Kebbi a wani mataki don bunƙasa harkokin tsaron iyakokin ruwa. Hakan na zuwa ne bayan da wata tawagar manyan jami’an sojojin ruwan suka kai ziyara gidan gwamnatin Jihar Kebbi. Ɗaliban da aka sace a Binuwai sun kuɓuta  ’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa Sojojin sun kai ziayarar ne ƙarƙashin jagorancin Rear Admiral Patrick Nwatu – wanda ya wakilci babban hafsan sojin ruwan ƙasar. Rundunar ta ziyarci Kebbi ne domin duba yadda za ta samar da sansaninta a jihar. Patrick Nwatu ya yi tir da harin ta’addanci a kogin Neja, yana mai cewa yankin ya zama maɓoyar masu safarar makamai da sauran masu aikata...
    Jami’an tsaro sun tabbatar da kuɓutar wasu ɗalibai shida na Makarantar Horon Ilimin Shari’a ta Najeriya da aka sace. Rundunar ’yan sandan Jihar Binuwai ce ta bayyana hakan a ranar Juma’a. ’Yan Najeriya miliyan 34 na cikin barazanar yunwa Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN Kakakin ’yan sandan, Udeme Edet, ya ce ɗaliban sun taso ne daga Jihar Anambra, yayin da suke kan hanyarsu ta zuwa makarantar horon ilimin shari’a da ke Yola, a Jihar Adamawa. ’Yan bindiga ne suka tare su a iyakar Binuwai da Taraba. “An ceto ɗalibai shida da aka sace a ranar 26 ga watan Yuli, 2025, yayin da suke kan hanyarsu daga Anambra zuwa Adamawa. “An...
    “Kiyasin ƴan Nijeriya miliyan 20 ke rayuwa da cutar hanta, kuma mutum miliyan 18.2 sun kamu ne da cutar rukunin B, sannan wasu mutum miliyan 2.5 sun kamu da cutar rukunin C. Abin takaici, ƴan Nijeriya 4,252 ne ke mutuwa a duk shekara sakamakon ciwon hanta da aka kasa maganceta ke haifarwa,” ya shaida.  A jawabinsa na fatan alkairi, mai riƙon muƙamin wakilin hukumar kula da lafiya ta duniya (WHO) a Nijeriya, dakta Aleɗ Gasasira, ya yi kira ne ga gwamnatin tarayya da ta tashi tsaye wajen yin na mijin ƙoƙari kan cutar hanta, yana mai cewa cutar tana shafar miliyoyin jama’a a ƙasar nan.  Gasasira, wanda ya samu wakilcin dakta Mya Ngon, a faɗin ofishin WHO da ke Nahiyar...
    Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayyana naɗin Saidu Yahya a matsayin sabon Shugaban Hukumar Karɓar Ƙorafe-ƙorafen Jama’a da yaƙi da cin hanci da rashawa (PCACC), bayan ƙarewar wa’adin tsohon shugaban, Barrister Muhuyi Magaji Rimin Gado, a watan Yuni. Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ta tabbatar da naɗin Sa’idu Yahya, mai shekaru 47, jami’i a fannin bincike kan cin hanci, inda ya shafe fiye da shekaru 18 yana aiki a Hukumar ICPC. Za A Kammala Aikin Titin Jirgin Ƙasan Kaduna-Kano A 2026 – Gwamnatin Tarayya Gwamnatin Kano Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Belin Dillalin Kwaya An bayyana cewa Yahya na da digiri a fannin tattalin arziki daga Jami’ar Bayero Kano,...
    A cewar Adelabu, har yanzu dai wutar lantarki ne ƙashin bayan kamfanoni a Nijeriya da kuma tattalin arziki, ya nemi haɗin kan dukkanin wadanda lamarin ya shafa domin sake farfaɗo da sashin wutar lantarki yadda ya kamata. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Akalla ’yan gudun hijira miliyan daya da dubu 400 da ke Arewa maso gabashin Najeriya ne suke fuskantar barazanar yunwa bayan yanje tallafin da Majalisar Dinkin Duniya (MDD) ke bayarwa. Wani rahoton majalisar a kan abinci da tsaro wanda gwamnatin Najeriya, Shirin Kula da Abinci na Majalisar (FAO) da sauran masu ruwa da tsaki a baya dai sun yi hasashen ’yan Najeriya miliyan 33.1 za su iya fuskantar matsanancin karancin abinci daga tsakanin watan Yuni zuwa Agustan 2025. Mun ci ribar Naira biliyan 414 a cikin wata 6 a Najeriya – Kamfanin MTN Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul Hakan dai na nufin a yanzu yan kasar miliyan 34.7 ne ke nan suke...
    Ya nuna rashin jin daɗinsa da rabon ayyukan tituna kamar yadda aka samu a cikin wata sanarwa da ma’aikatar ayyuka ta fitar a watan Mayun 2025, wanda a cewarsa, an ware Naira tiriliyan 1.394 wa yankin Kudu-maso-Yamma, yayin da ɗaukacin yankin Arewa-maso-gabas suka samu Naira biliyan 30, sai kuma yankin Arewa-maso-Yamma Naira 105 biliyan. “Rashin tsaro ya zama babban abin damuwa, ƴan fashi, tada ƙayar baya, da kuma garkuwa da mutane na ci gaba da wanzuwa a sassan Arewa da dama, inda jihohi kaɗan ne kamar Kaduna da Bauchi suka samu kwanciyar hankali,” in ji shi. Ya yi kira ga gwamnatin tarayya da ta fito da manufofin siyasa don kawo ƙarshen rikicin. ɗalhatu ya kuma soki manufofin gwamnatin tarayya kan...
    Tauraron dan wasan gaba na Super Eagles, Victor Osimhen, ya kammala komawarsa ƙungiyar Galatasaray ta ƙasar Turkiyya daga Napoli, a wata yarjejeniya ta dindindin da ta kai Yuro miliyan 75. Ƙungiyar Galatasaray ta sanar da kammala ɗaukar Osimhen a shafinta na yanar gizo a ranar Alhamis, inda ta bayyana cewa yarjejeniyar ta fara aiki daga nan take. Ɗan wasan mai shekaru 26 ya rattaba hannu kan yarjejeniyar shekaru huɗu tare da zakarun na ƙasar Turkiyya, kuma za a biya shi Yuro miliyan 15 a kowace kakar wasa. Hakazalika, zai karɓi ƙarin Yuro miliyan 5 a matsayin hakkinsa na mallakar hoto, yayin da Napoli za ta sami kashi 10 cikin 100 na duk wani kudi da za a sayar da shi...
    Sai dai girma, kima da ɗaukakar da matasa ke da ita ga al’umma ta ja baya ƙasa sosai a bisa ga yadda rayuwarsu ke iyo da ninƙaya a kogin  zubar da mutunci ta hanyar aiwatar da abubuwan da ke da alamar ayar tambaya. Matasa da dama a yau ba su ganin kowa da gashi, ba su girmama kowa, ba su ganin mutuncin kowa, ba su daraja kowa ballantana har a tsawata masu ko a ba su shawara da ɗora su kan hanyar yadda za su daidaita rayuwar su daga gurɓatacciyar hanya zuwa madaidaiciyar hanya. Abin takaici ne da matuƙar damuwa yadda matasa suka gurɓata rayuwarsu mamakon amfani da lokaci da damar da suke da ita amma sai suka zaɓi biyewa...
    A Alhamis din nan ne dai kasar ta Habasha ta fito da Shirin shuka bishiyoyi har miliyan 700 a rana daya, ta hanar shigar da miliyoyin mutanen kasar. Fira ministan kasar ta Habasha Abi Ahmad yana son a rika tunawa da shi anan gaba ta hanyar shuka bishiyoyin da za su kai biliyan 50, daga nan zuwa shekara ta 2026. Tun da safiyar jiya Alhamis ne dai miliyoyin mutanen kasar ta Habasha su ka fito zuwa wuraren yin shukar, inda su ka rika haka ramukan da za su yi dashen bishiyoyin. Kakakin gwamnatin kasar ta Habasha, Tesfahun Gobezay ya bayyana cewa, da jijjifin Safiya, gabanin cikar karfe; 6;a.m, mutane miliyan 14.9 sun dasa bishiyoyin da sun kai miliyan 355.  Shi...
    Kamfanin sadarwa na MTN ya sanar da cin ribar Naira biliyan 414 a watanni shida na farkon shekarar 2025 a Najeriya. Kamfanin ya bayyana hakan ne a rahotonsa na karshen wata shidan da ya gabatar a gaban Hukumar da ke Kula da Kasuwar Hannun Jari ta Najeriya a ranar Alhamis. Za a kashe biliyan 712.26 don yi wa filin jirgin saman Legas garanbawul NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi? A cewar rahoton, kamfanin ya kuma tafka asarar da ta kai ta Naira biliyan 90 saboda musayar kudaden kasashen waje. Rahoton ya kuma ce jimillar abin da kamfanin ya samu a tsawon lokacin kafin a cire riba ya kai Naira...
    Majalisar Zartarwa ta Kasa ta amince da kashe Naira biliyan 712.26 don yi wa wani sashe na filin jirgin saman a Murtala Muhammad da ke Legas garambawul. Hakan dai ya biyo bayan zaman majalisar wanda Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranta a Abuja ranar Laraba. NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi? Za a fara yi wa ɗaliban jami’o’i gwajin ƙwaya — Gwamnatin Nijeriya Aikin dai wani bangare ne na Naira biliyan 900 da aka ware domin inganta harkokin sufurin jiragen sama a fadin Najeriya. Ministan Harkokin Sufurin Jiragen Sama, Festus Keyamo ne ya bayyana hakan jim kadan da kammala taron majalisar, inda ya ce tuni har an ba...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya yi wa Kwanturola Janar na Hukumar Hana Fasa Kwauri ta Kasa, Bashir Adewale Adeniyi na ta shan suka daga mutane daban-daban. Yayin da wasu ke ganin abin da shugaban ya yi da cewa ya dace, wasu kuwa na ganin hakan ya yi hannun riga ga tanade-tanaden kundin tsarin mulkin kasa. Shin ko me dokar kasa ta ce game da wannan karin wa’adi da shugaban kasan ya yi? NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure Wannan shine batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci...
    Gwamnatin Nijeriya ta bayanna cewa za ta soma yi wa ɗaliban jami’o’in ƙasar nan gwajin miyagun ƙwayoyi a wani mataki na daƙile yaɗuwar ta’ammali da ƙwayoyin. Kamfanin Dillancin Labarai na Nijeriya NAN ya ruwaito cewa, Ma’aikatar Ilimi ta Tarayya tare da haɗin gwiwar Hukumar Yaƙi da Fataucin Miyagun Kwayoyi NDLEA ne za su jagoranci aikin. Sarkin Gudi na Jihar Yobe, Isa Bunuwo Ibn Khaji ya rasu Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani Hakan na zuwa ne bayan ganawar Shugaban Hukumar NDLEA, Birgediya Janar Buba Marwa mai ritaya da kuma ministan ilimin ƙasar, Olatunji Alausa a jiya Laraba. Ɓangarorin biyu sun kuma amince da ɓullo da daftarin koyar da darasin ilimin ta’ammali da ƙwayoyi a makarantun sakandiren...
    Yayin da yajin aikin gargadi na kasa baki daya da kungiyar ma’aikatan jinya da ungozoma ta kasa (NANNM) ta kira ya shiga rana ta biyu, iyalai sun fara kwashe ‘yan uwansu daga asibitocin gwamnati zuwa masu zaman kansu a jihar Filato. A Asibitin Kwararru na Jihar Filato, dogon layin masu amsar katin asibiti don neman kulawa da lafiyarsu ya yi batan dabo a lokacin da wakilinmu ya ziyarci asibitin. Gwamna Zulum Ya Sauke Kwamishinoni Biyu Tare Da Maye Gurbinsu Da Wasu Uganda Ta Jinjinawa Gudummawar Sin Ga Manufofin Wanzar Da Zaman Lafiya A Yankin Kahon Afirka Wata mata mai suna Misis Mary David, wacce ta yi rajista a asibitin duba lafiyar mata masu juna biyu, ta shaida wa wakilinmu cewa...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Allah Ya yi wa Mai Martaba, Sarkin Gudi Alhaji Isa Bunuwo Ibn Khaji rasuwa a asibitin Nizameye da ke Abuja ranar Alhamis. Mai martaba Sarkin wanda ke garin Gadaka a Ƙaramar hukumar Fika cikin Jihar Yobe ya rasu ne bayan ya yi fama da jinya. Gwamnatin Jigawa ta horas da malamai 20,000 fasahar sadarwar zamani Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana Sakataren masarautar Gudi da ke Gadaka ne ya tabbatar da rasuwar Sarkin, ya kuma ce an shirya gudanar da Sallar Jana’izar marigayi Sarkin a ranar Juma’a da ƙarfe 2:00 na rana a fadar Sarkin da ke Gadaka. Labarin rasuwar Sarkin dai ya tayar da hankalin a ɗaukacin al’ummar masarautar da ma Jihar Yobe...
    Gwamnatin Jihar Jigawa ta horas da Malaman makarantun sakandare kimanin dubu 20 ilimin fasahar sadarwar zamani (digital). Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi ne ya bayyana hakan a lokacin da ya karɓi baƙuncin tawaga daga Hukumar Bunƙasa Fasahar Sadarwa ta ƙasa (NITDA) da Cibiyar Zaman Lafiya ƙarƙashin jagorancin Farfesa Hauwa Ibrahim da take Amurka, a ziyarar ban girma da suka kai a gidan gwamnati da ke Dutse. Peter Obi zai lashe jihohin Arewa idan ya koma PDP – Jerry Gana Mun yi asarar shanu 340 a hannun ɓarayi a Yuli — Miyetti Allah Ya ce: “Mun gabatar da cibiya ta dijital don malamai, don sadarwa da kuma kula da ilmantarwa a matakin farko, mun sanya hannu kan haɗin gwiwa na...
    A nasa tsokaci game da batun, wakilin musamman na kasar Sin a yankin kahon Afirka Xue Bing, ya ce Sin ta dade tana goyon bayan matakan wanzar da zaman lafiya da ci gaba a yankin. Ya kuma jaddada muhimmancin hadin gwiwa tsakanin kasashe masu tasowa ta fuskar shawo kan tarin kalubale dake addabar duniya. (Saminu Alhassan)   Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Ministan harkokin waje na kasar siriya ya isa birnin Mosco a yau Alhamis don bude sabon shafi da kasar Rasha bayan kifar da gwamnatin Bashar Al-asad a shekarar da ta gabata. Shafin yanar gizo na larabai Arabnews na kasar Saudiya ya bayyana cewa Asaad Hassan al-Shaibani tuna ya gana da ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov sannan ya fada masa cewa, kasar Siriya tana son ta kara tabbatar da wasu yarjeniyoyi dake tsakanin Rasha da Siriya a can baya, sannan a samar da sabbin wuraren wadanda sabuwar gwamnatin rikon kasar Siriya take son ta kulla da Rasha, a cikin yanayin mutunta juna. A nashi bangaren Sergey Lavrov ya bayyana cewa kasar Rasha a shirye take ta taimakawa sabuwar gwamnatin...
    Tawagar kananan yan wasan damben gargajiya na kasar Iran sun zama zakara a wasannin da aka gudanar a na wannan shekara ta 2025 tare da Zinari guda, azurfa guda da kuma Tagullah 4. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jami’an gasar wasan na damben gargajiya na kasar Iaran suna fadar haka a birnin Athen na kasar Girka. Sun kuma kara da cewa tawagar yan wasan zun zama zakara a wannan gasar ne duk da cewa mutum guda daga cikinsu bai shaga wasan ba. Labarin ya kara da cewa matasan kasar Iran sun kware a wammam wasan gargajiya, wanda ake kiransa damben Roma. Tawagar ta sami, zinari 1, azurfa 1 da Tagulla 4 , ta kuma sami maki...
    Ganawar da shugaba Trump ya yi a baya-bayan nan da shugabannin wasu kasashe biyar dake nahiyar Afirka, ita ma ta janyo hankalin al’ummun duniya. Inda shugaba Trump ya yabawa shugaban kasar Laberiya Joseph Boakai kan yadda ya iya Turancin Ingilishi sosai, lamarin da ya bayyana rashin fahimtarsa kan alakar tarihi tsakanin kasar Laberiya da Amurka. Bugu da kari, Trump ya katse maganar shugaban kasar Mauritaniya Mohammed Ghazouani, inda ya nemi ya yi magana da sauri. A hakika, rashin mutuntawa da shugaba Trump ya nuna a fili, ta bayyana ainihin dalilin da ya sa aka gayyaci shugabannin Afirka biyar zuwa wajen ganawar—ba domin neman karfafa dangantaka ba ne, sai dai don tabbatar wa Amurka din damar samun ma’adanan da take bukata,...
    Fadar Shugaban ƙasa ta bayyana cewa shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya amince da ƙarin wa’adin shekara guda ga shugaban hukumar Kwastan ta Nijeriya, Bashir Adewale Adeniyi. Kafin wannan ƙarin wa’adin, aikin Adeniyi zai kare ne a ranar 31 ga Agusta, 2025. Sai dai sanarwar da mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ya fitar a ranar Alhamis ta ce wannan mataki na Tinubu zai ba Adeniyi damar kammala muhimman gyare-gyare da ayyuka da gwamnatin ke aiwatarwa a hukumar. Matsalar Tsaro: Tinubu Ya Ziyarci Jama’a, Ya Daina Sauraron Gwamnoni — ADC Tinubu Ya Karrama Mata ‘Yan Ƙwallon Nijeriya Da Lambar Girmamawa (OON), Dala Dubu 100 Da Gidaje A cikin manyan ayyukan da ake son a kammala akwai shigar da...
    Tsohon ɗan wasan tsakiyar Barcelona, Carles Perez, yana kwance a asibiti a ƙasar Girka bayan da wani kare ya cije shi a al’aurarsa yayin da yake yawo da nasa karen a Thermi, a wata unguwa a Thessaloniki, ranar Talata. Perez, mai shekaru 27, yana ƙoƙarin raba karensa da wani da suke fada lokacin da ya ji ciwo mai tsanani a wajen. An garzaya da shi zuwa wani asibiti mai zaman kansa a Panorama inda aka ɗinke masa raunin da ƙwayoyin da suka kai guda shida. Rashford Na Dab Da Komawa Barcelona A Matsayin Aro Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Aris FC, wacce ta karɓi Perez aro daga Celta Vigo, ta tabbatar...
    Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa Bashir Adeniyi, Shugaban Hukumar Kwastam ta Ƙasa, karin shekara ɗaya a kan wa’adin da ya kamata ya yi na shugabancin hukumar. Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Alhamis. Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani A cewarsa, wa’adin Mista Adeniyi zai ƙare ne a ranar 31 ga watan Agusta, 2025. Amma yanzu Shugaba Tinubu ya amince da ƙara masa shekara ɗaya, wanda hakan ke nufin zai ci gaba da zama a kan kujerarsa har zuwa watan Agustan 2026. Sanarwar ta bayyana cewa ƙarin wa’adin zai ba shi damar kammala wasu...
    Shugaba Bola Tinubu ya ƙara wa Bashir Adeniyi, Shugaban Hukumar Kwastam ta Ƙasa, karin shekara ɗaya a kan wa’adin da ya kamata ya yi na shugabancin hukumar. Mai magana da yawun shugaban ƙasa, Bayo Onanuga, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa a ranar Alhamis. Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa NNPCL ya sake haƙa sabbin rijiyoyin man fetur 4 a Kolmani A cewarsa, wa’adin Mista Adeniyi zai ƙare ne a ranar 31 ga watan Agusta, 2025. Amma yanzu Shugaba Tinubu ya amince da ƙara masa shekara ɗaya, wanda hakan ke nufin zai ci gaba da zama a kan kujerarsa har zuwa watan Agustan 2026. Sanarwar ta bayyana cewa ƙarin wa’adin zai ba shi damar kammala wasu...
    Abdullahi ya ce tun kafin a kafa haɗakar, wasu sun riga sun fara yaɗa cewa an shirya ta ne domin Atiku. Ya ƙara da cewa: “Ni ina da shekara 56, wa ya ce ba zan iya tsayawa takarar shugaban ƙasa ba?” Da aka tambaye shi game da Peter Obi, tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar LP, Abdullahi ya ce Obi na cikin haɗakar har yanzu. Amma ya ce bai zama cikakken ɗan jam’iyyar ADC ba har yanzu. Ya bayyana cewa jam’iyyar ADC ta bai wa Obi da kuma tsohon gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai, dama su fice daga jam’iyyunsu na yanzu wato LP da SDP. Ya kuma ce Obi ba zai koma jam’iyyar PDP ba, duk da cewa jam’iyyar...
    Babban Sakatare Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres,ya bayyana cewa, samar da makamashi mai tsabta da zai daidaita tsarin rayuwar dan Adam daga sarrafa wuta, ta hanyar yin amfani da tururi, zuwa rarrabuwar ma’adinan, shi ne ginshikin bunkasar al’umma. Mista Gutterres ya bayyana hakan ne a taron inganta samar da makamshi da aka gudanar a harabar ofishin Majalisar Dinkin Duniya. Ya ce “a yau, muna son tabbatar da yadda za a farka bisa tsarin sabon zamani. Rana tana fitowa don samar da makamashi mai tsabta ga al’umma. A bara, kusan dukkanin sabbin qarfin wutar lantarki sun fito ne daga abubuwan da ake sabuntawa. Zuba jari a harkar samar da makamashi mai tsafta darajarsa ta haura zuwa Dala tiriliyan 2...
    Manchester United ta soma tattaunawa da Paris St-Germain kan golan Italiya Gianluigi Donnarumma, mai shekara 26, amma Chelsea da Manchester City na cikin masu sha’awar golan. (Telegraph – subscription required, external) Yayin da ɗanwasan gaba na Sweden Alexander Isak, mai shekara 25, ya amince ya koma Liverpool, Newcastle ta saka ɗanwasan Brazil Rodrigo Muniz, mai shekara 24 cikin lissafinta. (Mail – subscription required, external) Crystal Palace ta sanar da Arsenal cewa sai ta fara biya aƙalla fam miliyan 35 kafin ta ɗauko Eberechi Eze, daga baya ta cike sauran kuɗin. (Guardian, external) Palace a shirye take ta biya fam miliyan 27.6 domin ɗauko ɗanwasan baya na Jamus Yann Bisseck, mai shekara 24 daga Inter Milan domin maye gurbin Marc Guehi, da ake alaƙantawa da Liverpool. (Gazzetta dello Sport – in Italian, external) Chelsea na ci gaba da matsi kan Alejandro...
    Rundunar ‘yan sandan jihar Neja ta saki tare da hada wadanda aka yi garkuwa da su talatin da biyar tare da iyalansu.   Sun kunshi mata goma sha shida da yara goma sha tara daga Kagara, Tegina da Agwara, bayan sun shafe makonni a hannun ‘yan sanda da ke tsare da kuma kawar da hankalinsu daga barayin da ke Minna.   Kwamishinan ‘yan sanda mai kula da jihar Neja Adamu Abdullahi Elleman ya bayyana haka a lokacin wani takaitaccen bayani da ya mikawa shugaban karamar hukumar gidan rediyon Ayuba Usman Katako a Minna.   Kwamishinan ‘yan sandan wanda mataimakin kwamishinan ‘yan sanda Ibrahim Adamu ya wakilta, ya bayyana cewa za’a sake haduwa da wadanda abin ya shafa da iyalansu domin...
    Sama da mutum 5,000 ne suka tsere daga gidajensu a Jihar Katsina, sakamakon sabbin hare-haren da ’yan bindiga suka kai a Ƙananan Hukumomin Bakori da Faskari. Mutane daga ƙauyuka sama da 10 sun nemi mafaka a garin Bakori, inda da dama ke zaune wajen ’yan uwansu, yayin da wasu ke kwana a waje ba tare da masauki ko abinci ba. Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga Tallafin matar Tinubu na N1bn ga ’yan gudun hijirar Binuwai ya bar baya da kura Wasu daga cikin waɗanda abin ya shafa sun bayyana cewa, maharan sukan shiga ƙauyuka da yawa, inda suka dinga harbi, ƙone gidaje, sannan suka sace mutane ciki har da mata da ƙananan yara....
    Tawagar Iran ta fice daga taron majalisun dokokin kasashen duniya kafin fara jawabin jami’in gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila a zaman taron A wata gagarumar nuna rashin amincewa da tushen zaluncin da ya addabi duniya, tawagogin kasashen Iran, Yemen, da Falasdinu sun fice daga zaman taron Majalisar Dinkin Duniya a Geneva, bayan da shugaban majalisar dokokin Isra’ila “Knesset” zai fara gabatar da jawabinsa mai kunshe da bayanai neman tunzura jama’a, wanda kuma bayanai suka haifar da cece-kuce a tsakanin wadanda suka zauna suka saurara. A cikin jawabin shugaban majalisar dokokin Isra’ila “Knesset” ya bayyana cewa; Akwai yiwuwar samar da ‘yantacciyar kasar Falasdinu a wajen yankunan Falasdinu, musamman a biranen London da Paris na kasashen Birtaniya da Faransa. Wannan matakin na nuna...
    Bayo Onanuga, Mai Bai Wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin yaɗa labarai, ya ce wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu ne kawai saboda ya fito daga Kudancin Najeriya. Yayin wata hira da Trust Radio, Onanuga ya ce maganar cewa ana yi wa Arewacin Najeriya wariya ba gaskiya ba ce, face tsantsar siyasa kawai. Tinubu ya karɓi baƙuncin Abdulmumin Jibrin Kofa Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya Ya ce ƙorafin da Ƙungiyar Tuntuɓa ta Arewa (ACF), ta yi na cewa an yi watsi da Arewa wajen naɗe-naɗen muƙaman gwamnati da ayyukan ci gaba, wata dabara ce kawai don rage ƙimar shugabancin wanda ya fito daga Kudu. Ya shawarci ’yan siyasar Arewa...
    Da alama tallafin da matar Shugaban Kasa, Sanata Remi Tinubu ta ba wadanda hare-haren jihar Binuwai ya raba da muhallansu na Naira biliyan daya ya bar baya da kura. Kwana daya da bayar da tallafin, ’yan gudun hijirar sun fito suna zanga-zangar yunwa, amma kakakin hukumar bayar da agaji ta jihar (SEMA), Terna Ager, ya ce musu kudin ba na sayen abinci ba ne. Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya Aminiya ta rawaito yadda Sanata Remi a ranar Talata ta ziyarci jihar inda ta mika wa Gwamnan Jihar, Hyacinth Alia tallafin kudin, a madadin ’yan gudun hijirar....
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Kungiyar Tuntuba ta Arewa (ACF) ta zargi Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu da kin yin adalci wurin ayyuka da raba mukamai tsakanin Arewa da Kudancin Kasar nan. Wadannan zarge-zarge suka sa fadar Shugaban Kasa ta hannun mai taimaka masa na musamman kan kafofin yada labarai Bayo Onanuga mayar da martani ga kungiyar ta ACF. Ko wadanne irin martani fadar shugaban kasar ta mayar ga kungiyar? NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba a kai. Domin sauke shirin, latsa nan
    Gwamna Umar Namadi ya kaddamar da shirin tallafi guda biyu da suka kai fiye da naira miliyan 392, ga membobin kungiyar direbobi ta NURTW da kuma ƴan kungiyar mahauta a jihar Jigawa. Wannan tallafi wani ɓangare ne na ƙoƙarin gwamnatinsa na inganta rayuwar masu sana’o’in  da ke taka muhimmiyar rawa a rayuwar yau da kullum. A wajen kaddamar da shirin a filin wasa na Dutse, Gwamna Namadi ya bayyana cewa shirin yana da manufa ta musamman domin tallafa wa jama’a kai tsaye. Ya ce ƙungiyoyin NURTW da mahauta suna da matuƙar tasiri, ba kawai ga membobinsu ba, har ma da al’umma gaba ɗaya, shi ya sa gwamnatinsa ta ga dacewar tallafa musu. Gwamnan ya kara da cewa taimakon...
      A shekara ta 2009, hukumar Kwallon Kafa ta Nijeriya ta dauki Yusuf aiki a matsayin mataimakin koci ga Samson Siasia  wanda ke rike da mukamin babban kocin tawagar kwallon kafa ta Nijeriya, Yusuf har yanzu yana aiki da Siasia, ya taimakawa Pillars samun gurbin shiga gasar cin kofin CAF, a shekarar 2012 ya koma Enyimba inda ya maye gurbin Austin Eguavoen a matsayin koci kuma ya taimaka masu wajen lashe kofin gasar Federation Cup na shekarar 2013. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Bayanin da ofishin siyasa na kwamitin kolin JKS ya yi a baya-bayan nan game da hasashe kan tattalin arzikin kasar Sin cikin shekaru biyar masu zuwa ya jawo hankalin duniya sosai. Kuma sakamkon binciken jin ra’ayoyin jama’a da CGTN na babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG ya yi a tsakanin masu bayyana ra’ayoyi 47,000 a kasashe 46 daga shekarar 2023 zuwa 2025, ya nuna jama’ar sun nuna yakini game da karfi da juriyar tattalin arzikin kasar Sin. Binciken ya nuna cewa, yawancin masu bayyana ra’ayoyin daga sassan duniya suna da kyakkyawan fata ga tattalin arzikin kasar Sin wajen samun bunkasa mai kyau a dogon lokaci, inda amincewarsu ta kai kashi 74.7 bisa dari, da 81.3 bisa...
    Wadannan ’yan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi sun sake nuna bajintar da kasar Sin ke nunawa a fagen kere-keren mutum-mutumi masu siffar dan’adam da kuma yadda masana’antar bangarensu ke samun ci gaba cikin hanzari a kasar. A watan Agusta mai kamawa ne kasar Sin za ta karbi bakuncin gasar wasannin motsa jiki na mutum-mutumi masu siffar dan’adam. Kuma wannan wasan kwallon kafa na mutum-mutumi da aka gwabza fafatawar karshe a dandalin wasannin motsa jiki na fasahar zamani da ke birnin Beijing, wata kyakkyawar shaida ce a kan yadda kasar ta shirya wa karbar bakuncin wannan gasa. (Abdulrazaq Yahuza Jere)   Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura...