Dakarun Yeman sun sanar da sake kai hari kan filin jirgin saman Isra’ila na Ben Gurion da ke kusa da birnin Tel Aviv da makami mai linzami mai linzami.

Bayanai sun ce ko wannan karo tsarin garkuwa daga hare haren sama na Amurka samfarin THAAD ya gaza kakkabo harin.

Sanarwar da rundunar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta Birgediya Janar Yahya Saree ta bayyana cewa, an kai harin ne yau Juma’a.

Kakakin rundunar ‘yan Houthi Yahya Saree ya ce, sun yi amfani da makami mai linzami mai gudun tsiya,”

Isra’ila dai ta sha alwashin mayar da martani mai karfi kan harin.

Kasar Yemen dai na mai kai hari kan kaddarorin Isra’ila domin nuna goyan baya ga al’ummar Gaza da ke fuskantar hare-hare daga Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah

Wani sabon kudiri da ke gaban Majalisar Dokokin Amurka ya nemi a hana ’yan kungiyar Fulani makiyaya ta Miyetti Allah da Miyetti Allah Kautal Hore bizar shiga Amurka.

Kudurin, wanda dan majalisa Christopher Smith ya gabatar a ranar Talata, ya kuma bukaci kwace kadarorin mambobin kungiyar.

An kashe babban limami a Kwara saboda zargin maita Gwamnatin Tarayya ta fara shirin sayar da matatun manta ga ’yan kasuwa

Wannan na daga cikin matakan da gwamnatin Amurka ke ɗauka don dakile abin da ta kira take hakkin ’yancin addini ga Kiristocin Najeriya.

Kudirin dai na neman hukunta mutane da ƙungiyoyi da ke da hannu ko goyon baya wajen take hakkin ’yancin addini mai, a ƙarƙashin dokar kasa da kasa ta IRFA.

Christopher ya yaba wa Shugaba Trump bisa sake ayyana Najeriya a matsayin Ƙasa Mai Ƙalubale Na Musamman, yana mai ambato rahotannin ci gaba da hare-hare kan al’ummomin Kirista a sassan ƙasar.

Kudirin ya kuma ambaci ’yan ta’adda Fulani da ke kai hare-hare a jihohin Binuwai da Filato a cikin kungiyoyin da ake sa’ido a kansu, wani matsayi da Amurka ke warewa ga ’yan ƙungiyoyin da ba na gwamnati ba da ake zargi da take hakkin addini.

Sauran irin wadannan kungiyoyin da aka ayyana a baya a ƙarƙashin dokar sun haɗa da Boko Haram, ISWAP, ISIS-Sahel, Taliban da kuma Houthi.

Idan aka amince da kudirin, zai bai wa hukumomin Amurka damar hana biza da kuma kulle kadarorin mutanen da ke da alaƙa da waɗannan ƙungiyoyi.

An gabatar da kudirin ne bayan watanni na kiraye-kirayen yin hakan daga ’yan majalisar dokokin Amurka da ƙungiyoyin Kiristoci masu tsattsauran ra’ayin.

Shugaban Amurka Donald Trump dai ya yi zargin ana yi wa Kiristoci a Najeriya kisan kiya, amma gwamnatin kasar ta yi fatali da zarge-zargen inda ta kira shi a matsayin na karya.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  •  Jirgin Kasan Dakon Kaya Na Farko Daga Rasha Ya Iso Kasar Iran A Yau Asabar
  •  Lebanon: Mutane 2 Sun Jikkata Sanadiyyar Harin “Isra’ila” A Garin Bint-Jubail
  • Sin Ta Kadammar Da Babban Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Yaki Na CNS Fujian a Rundunar Sojan Ruwanta
  • Barazanar Amurka Na Kawo Wa Nijeriya Hari 
  • Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu
  • Majalisar Dokokin Amurka na neman a hukunta ’yan kungiyar Miyetti-Allah
  • Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
  • Sojin Amurka sun gabatar da shirin ƙaddamar da hari a Najeriya
  • Najeriya: Ta Sake Jaddada Yin Watsi Da Zargin Take Hakkin Kiristoci A Kasar
  • Jirgin ƙasa ya murƙushe babur mai ƙafa uku a Jos