Dakarun Yeman sun sanar da sake kai hari kan filin jirgin saman Isra’ila na Ben Gurion da ke kusa da birnin Tel Aviv da makami mai linzami mai linzami.

Bayanai sun ce ko wannan karo tsarin garkuwa daga hare haren sama na Amurka samfarin THAAD ya gaza kakkabo harin.

Sanarwar da rundunar ta fitar ta hannun mai magana da yawunta Birgediya Janar Yahya Saree ta bayyana cewa, an kai harin ne yau Juma’a.

Kakakin rundunar ‘yan Houthi Yahya Saree ya ce, sun yi amfani da makami mai linzami mai gudun tsiya,”

Isra’ila dai ta sha alwashin mayar da martani mai karfi kan harin.

Kasar Yemen dai na mai kai hari kan kaddarorin Isra’ila domin nuna goyan baya ga al’ummar Gaza da ke fuskantar hare-hare daga Isra’ila.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

HOTUNA: An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa Saudiyya

An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa ƙasar Saudiyya domin gudanar da Aikin Hajjin 2025.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima ne ya ƙaddamar da tashin maniyattan a filin jirgin Sam Mbakwe da ke birnin Owerri na Jihar Imo.

’Yan kungiyar asiri sun kashe masu shirin tafiya NYSC a Bayelsa JAMB ta saki sakamakon jarrabawar 2025

Sahun farko na maniyyata 315 waɗanda suka kama hanyar ƙasa mai tsarki sun fito ne daga jihohin Imo da Abia da Bayelsa inda jirgin Air Peace ne ya kwashe su.

Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodinma da Shugaban Hukumar Alhazan Nijeriya, Farfesa Abdullahi Usman da Sarkin Musulmi, Alhaji Muhammadu Sa’adu Abubakar III da sauran manyan jami’an gwamnatin Nijeriya ne suka tarbi Kashim Shettima domin ƙaddamar da tashin maniyyatan.

Aƙalla mutum 43,000 ne waɗanda suka yi rajistar gudanar da aikin hajji daga jihohi 36 da birnin tarayyar ƙasar za su tafi ƙasa mai tsarki domin sauke farali.

Hukumar alhazan ta ce jirgin Air Peace zai kwashi maniyyata 5,128 daga Jihohin Abia da Akwa Ibom da Anambra da Bayelsa da Benue da Cross River da Delta da Ebonyi da Edo da Ondo da Ribas da Taraba.

Sai kuma jirgin FlyNas zai ɗauki maniyyata 12,506 daga Abuja babban birnin Nijeriya da Kebbi da Legas da Ogun da Osun da Sokoto da Zamfara.

Sannan kuma jirgin Max Air zai ɗauki fasinjoji 15,2043 daga Jihohin Gombe da Jigawa da Kano da Katsina da Kwara da Oyo da Filato.

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • HOTUNA: An ƙaddamar da tashin sahun farko na maniyyatan Nijeriya zuwa Saudiyya
  • Isra’ila Ta Yi Barazanar Kai Hare-Hare Kan Iran Kamar Hamas Da Hezbollah
  • Yemen Ta Jaddada Cewa: Idan Amurka Ta Kai Mata Hari, Tabbas Yarjejeniyar Kawo Karshen Bude Wuta Tsakaninsu Zata Ruguje  
  • Falasdinawa Sun Yi Shahada A Hare-Haren Da Sojojin Isra’il Suka Kai Gidan Cin Abinci Da Kasuwa A Gaza
  •  Waji Jirgin Amurka Samfurin F-18 Na 3 Ya Fadi A Tekun “Red-Sea”
  •  Hare-haren Hizbullah Sun Jazawa HKI A Fagen Gona Asarar Dala Miliyan 108
  • Ansarullah: Yarjejeniya da Amurka ba za ta dakatar da hare-haren da Yemen ke kaiwa Isra’ila ba
  • Yaƙi ya ɓarke tsakanin Indiya da Pakistan
  • Kasar Indiya Ta Yi Luguden Makamai Masu Linzami Kan Kasar Pakistan