Nijeriya ta soke ba da tallafin karatu a ƙetare
Published: 9th, May 2025 GMT
Gwamnatin Nijeriya ta sanar da dakatar da tsarin bai wa ɗalibai tallafi domin samun damar zuwa ƙetare ƙarin ilimi.
Ministan Ilimi, Tunji Alausa, shi ne ya sanar da wannan mataki, da ke nufin cewa za a kawo ƙarshen wannan tsari da aka share tsawon shekaru ana aiwatarwa.
Yadda yara 5 suka mutu a cikin motar da aka yi watsi da ita Yadda rashin wutar lantarki ke ajalin rayuka a manyan asibitociMista Alausa ya bayyana cewa wannan matakai ya samu ne sakamako nazari da aka yi wajen sanya ƙaƙƙarfan jari a manyan makarantun ƙasar.
Ministan ya ce daga yanzu babu batun bai wa ’yan ƙasar kuɗaɗen ƙaro ilimi daga ƙetare, saboda yanayi da ake ciki da ma kyawun tsari da ake da shi a cikin ƙasar.
A cewarsa, dukkannin kwasa-kwasan da ’yan Nijeriyar ke zuwa wasu ƙasashen domin nazarin su, akwai su a cikin jami’o’i da ma kwalejojin fasaha masu nagarta da ake da su.
Ministan ya ce kuɗaɗen da ake kashewa wajen daukar nauyin karatun ɗaliban a ƙetare, zai fi dacewa a sanya su wajen inganta jami’o’in da kwalejojin da ake da su.
Sanarwar na zuwa ne a yayin da Hukumar Bunƙasa Arewa maso Yamma NWDC ta soke bayar da tallafin karatu ga ɗaliban da suka fito daga yankin.
Makonni kaɗan da suka gabata ne Hukumar ta NWDC ta fitar da sanarwar cewa tana neman haziƙan ɗalibai da suka fito daga yankin domin ɗaukar nauyin karatunsu a wasu ƙasashe ƙetare.
Sai dai wata sanarwa da hukumar ta fitar safiyar wannan Juma’ar, ta ce an soke tsarin, inda za ta mayar da hankali kan wasu ababen domin bunƙasa yankin.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Gwamnatin tarayya Hukumar Bunƙasa Arewa maso Yamma karatu
এছাড়াও পড়ুন:
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB
Eze na cikin jerin da rundunar tsaro ke nema ruwa a jallo saboda hannu da yake da shi wajen kai hare-hare da garkuwa da mutane a yankin Kudu maso Gabas.
Manjo Janar Kangye, ya ƙara da cewa, a watan Afrilu, sojojin sun ceto mutane 173 da aka yi garkuwa da su, sannan sama da ‘yan ta’adda 204 da iyalansu sun miƙa wuya.
Haka kuma, sun kama mutane 430 da ake zargi da satar mai da wasu laifuka daban-daban.
A ƙarƙashin Operation DELTA SAFE, an daƙile satar mai da darajarsa ta haura Naira biliyan 1.9 a cikin mako guda.
Sun ƙwato sama da lita miliyan ɗaya ta ɗanyen mai da kuma dubban litoci na man fetur da wasu nau’inkan haramtattun mai.
Sojojin sun lalata wuraren tace ɗanyen mai da jiragen ruwa da kayan aiki daban-daban.
Har ila yau, sun gano manyan makamai da harsasai da abubuwan fashewa.
Wannan aikin na daga cikin ƙoƙarin gwamnati na yaƙar aikata laifuka da kare rayuka da dukiyoyin ‘yan Nijeriya.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp