Wani babban hafsan sojin Yemen ya bayyana dabarun Yemen da suka tilastawa Amurka dakatar da kai hare-hare kan kasar Yemen

Kwararren kan harkar sojin kasar Yemen kuma kwararre kan harkar yaki Birgediya Janar Aziz Rashid ya jaddada bunkasar karfin sojan kasar Yemen, yana mai nuni da dalilan da suka sanya aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Yemen.

A wata hira ta musamman da ya yi da tashar talabijin ta Al-Alam, kwararren sojan kasar Yemen kuma kwararre kan harkar dabarun yaki birgediya Janar Aziz Rashid ya tabbatar da cewa: Kasar Yemen ta samu wani matsayi mai inganci a arangamar da take yi da haramtacciyar kasar Isra’ila, inda ta yi nasarar sauya ma’aunin karfin iko da kuma karuwar matakan soji da sabbin ka’idojin arangama kan makiya.

Birgediya Janar Rashid ya yi nuni da cewa dakarun kasar Yemen sun tilastawa Amurka gaggauta kawo karshen ta’asarta ta hanyar tuntubar mai shiga tsakani na kasa da kasa na kasar Oman. An dai cimma matsaya kan kauracewa luguden wuta kan kasar Yemen, domin kauracewa kai hari kan jiragen ruwan Amurka, muddin Amurka ta kuduri aniyar kawo karshen kai hari kan Yemen.

Ya bayyana cewa yarjejeniyar tsagaita wutar ta zo ne bayan faduwar jiragen saman Amurka guda uku samfurin F-18. Sun danganta faduwar jirgin na farko da harbin abokan Amurka, na biyu kuma da juyowar da jirgin dakon jiragen saman Amurka ya yi da kuma yin artabu da sojojin Yemen daga baya. Dangane da na uku kuma, sun kasa yin karya game da musabbabin faduwar jirgin, lamarin da ya sa Trump ya tuntubi mai shiga tsakani na Amurka don gaggauta tsagaita bude wutar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji

Bugu da kari, a baya bayan nan ma jaridar Financial Times, ta bayyana yadda a yanzu haka adadin hajojin da ake shigarwa Amurka daga sassan duniya daban daban suka ragu zuwa kaso 13 bisa dari, sabanin kaso kusan 20 bisa dari da kasar ke shigowa da su a tsawon shekaru 20 da suka gabata.

Kamar dai yadda kimar Amurka ke raguwa sakamakon matsin lamba da take yiwa sauran sassan duniya abokan cinikayyarta, haka ma wadannan manufofi na kakaba haraji ke fuskantar turjiya, da kyama har daga abokan kasar makusanta. (Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Venezuela: An dakile yunkurin kai wasu munanan hare-hare a cikin kasar
  • Iran: ‘Yan Sahayoniyya Na Shari Share Falasdinawa Daga Kn Doron Kasa
  • Iran: Amurka Ta Sha Kaye Daga ‘Yan Gwagwarmayar Kasar Yemen
  • Jamus ta dakatar da ba wa Isra’ila kayayyakin aikin soji saboda shirinta na mamaye Gaza
  • Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?
  • Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan hare-haren ’yan bindiga
  • Amurka Ta Fara Girbar Sakamakon Kare-Karen Haraji
  • Hare-Haren Sojojin Mamayar Isra’ila Kan Gaza Sun Janyo Shahadan Falasdinawa Masu Yawa
  • Human Rights Watch Ta Ce: Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Rusa Makarantu Fiye Da 500 A Gaza
  • Gaza: Fararen hula 22 sun yi shahada a hare-haren Isra’ila a daren jiya