Wani babban hafsan sojin Yemen ya bayyana dabarun Yemen da suka tilastawa Amurka dakatar da kai hare-hare kan kasar Yemen

Kwararren kan harkar sojin kasar Yemen kuma kwararre kan harkar yaki Birgediya Janar Aziz Rashid ya jaddada bunkasar karfin sojan kasar Yemen, yana mai nuni da dalilan da suka sanya aka cimma yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin Amurka da Yemen.

A wata hira ta musamman da ya yi da tashar talabijin ta Al-Alam, kwararren sojan kasar Yemen kuma kwararre kan harkar dabarun yaki birgediya Janar Aziz Rashid ya tabbatar da cewa: Kasar Yemen ta samu wani matsayi mai inganci a arangamar da take yi da haramtacciyar kasar Isra’ila, inda ta yi nasarar sauya ma’aunin karfin iko da kuma karuwar matakan soji da sabbin ka’idojin arangama kan makiya.

Birgediya Janar Rashid ya yi nuni da cewa dakarun kasar Yemen sun tilastawa Amurka gaggauta kawo karshen ta’asarta ta hanyar tuntubar mai shiga tsakani na kasa da kasa na kasar Oman. An dai cimma matsaya kan kauracewa luguden wuta kan kasar Yemen, domin kauracewa kai hari kan jiragen ruwan Amurka, muddin Amurka ta kuduri aniyar kawo karshen kai hari kan Yemen.

Ya bayyana cewa yarjejeniyar tsagaita wutar ta zo ne bayan faduwar jiragen saman Amurka guda uku samfurin F-18. Sun danganta faduwar jirgin na farko da harbin abokan Amurka, na biyu kuma da juyowar da jirgin dakon jiragen saman Amurka ya yi da kuma yin artabu da sojojin Yemen daga baya. Dangane da na uku kuma, sun kasa yin karya game da musabbabin faduwar jirgin, lamarin da ya sa Trump ya tuntubi mai shiga tsakani na Amurka don gaggauta tsagaita bude wutar.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: kasar Yemen

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamna Buni ya tallafawa iyalan sojojin da suka mutu 

Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni a ranar Alhamis ya ziyarci sojojin Hedikwatar Task Force Brigade ta 27 Buni Gari, domin jajantawa waɗanda aka kashe kan harin da ’yan tada ƙayar baya suka kai. 

A cikin jawabinsa Gwamna Buni ya bayyana cewa, abin takaici ne ga sake ɓarkewar tashe-tashen hankula da kuma hare-haren da ake kaiwa jami’an tsaro.

’Yan sanda sun ƙaddamar da ƙwararrun Jami’an tsaro saboda makarantu a Bauchi An gurfanar da mutum 10 kan yi wa nakasasshiya fyaɗe a Kaduna

Gwamnan ya jajanta wa sojoji da iyalan ma’aikatan da suka mutu, yana mai cewa, “Jami’an ba su mutu a banza ba, sun mutu suna ƙoƙarin kare ƙasarsu sosai”.

Ya bayar da tallafin Naira miliyan 2m ga kowane iyalan jaruman da suka mutu, sannan kuma Naira miliyan 1m ga jami’an da suka samu raunuka.

Buni ya ce, gwamnati za ta kuma bayar da tallafin ilimi kyauta ga yaran sojojin da suka mutu.

Hakazalika, Gwamnan ya sanar da bayar da gudunmuwar Naira miliyan 50 da za a raba wa dakarun rundunar ta 27 Brigade Buni Gari, baya ga kayan abinci, katifa, barguna da sauran kayayyaki da gwamnatin jihar ta bayar.

Ya kuma ba da tabbacin goyon bayan gwamnati da al’ummar jihar ga sojoji da sauran jami’an tsaro domin yaƙar waɗannan ’yan ta’addan yadda ya kamata tare da fatattakarsu.

Gwamna Buni ya ba da umarnin ƙarfafa tsaro a kewayen rundunar, inda ya ba da tabbacin goyon bayan gwamnati ga jami’an tsaro, “Za mu ci gaba da ƙara ƙaimi wajen inganta tsaro a kewayen.

Kwamandan rundunar Birgediya Janar Usman Ahmed, wanda ya jagoranci Gwamnan wajen duba wannan runduna, ya yabawa Gwamna Buni kan yadda ya ke nuna damuwa da kulawa ga sojojin a kowane lokaci.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Pakisatan Ta Maida Martanin Farmakin Sindoor Na Indiya Kan Rumbun Makamai Masu Linzami Na Indiya
  • Yemen Tana Bukukuwan Samun Nasara Kan Amurka Kuma Zata Ta Ci Gaba Da Goyon Bayan Gaza
  • Jami’ar Colombiya Ta Birnin New York A Amurka Ta Dakatar Da Karatun Daliban Jami’ar Fiye Da 65
  • Yemen ta sake kai hari kan filin jirgin saman Isra’ila da makami mai linzami
  • Masana Sun Bayyana Ingancin TELA Maize Ga Rayuwar Al’umma
  • An Dakatar Da Ayyukan Jam’iyyun Siyasa A Kasar Mali
  • Gwamna Buni ya tallafawa iyalan sojojin da suka mutu 
  • Yemen Ta Jaddada Cewa: Idan Amurka Ta Kai Mata Hari, Tabbas Yarjejeniyar Kawo Karshen Bude Wuta Tsakaninsu Zata Ruguje  
  • Falasdinawa Sun Yi Shahada A Hare-Haren Da Sojojin Isra’il Suka Kai Gidan Cin Abinci Da Kasuwa A Gaza