Shugaban kasar Sin Xi Jinping da shugaban kasar Rasha Vladimir Putin sun halarci bikin kulla takardar hada kai da aka shirya a fadar Kremlin a jiya Alhamis. A shaidar shugabannin kasashen biyu, shugaban CMG Shen Haixiong ya wakilci hukumar fina-finai ta kasar Sin da ministar hukumar al’adu ta Rasha Olga Borisovna Lyubimova sun kulla hannu da yi musanyar takardar “Shirin samar da fina-finai bisa hadin gwiwar hukumar fina-finai ta kasar Sin da hukumar al’adu ta Rasha kafin shekarar 2030”.

 

Shirin ya taka rawar gani wajen gaggauta hadin gwiwar kasashen biyu ta fuksar samar da fina-finai tare, da shigowar fina-finan junansu da gabatar da bukukuwan fina-finai tsakaninsu, ta yadda za a kara tuntubar al’adu da koyi da juna a bangaren fina-finai don ciyar da huldar abota bisa manyan tsare-tsare a duk fannoni tsakaninsu a sabon zamani gaba. (Amina Xu)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Da Karamar Hukumar Dutse Za Su Shirya Taron Bita Ga Kansiloli

Shugaban Kwamatin kananan hukumomi na majalisar Dokokin jihar Jigawa, Alhaji Aminu Zakari, ya bayyana cewa gudanar da ayyukan raya kasa sosai a yankunan karkara zai kara daga martabar jihar a idon sauran jihohin kasar nan.

Ya yi wannan tsokaci ne yayin ziyarar aiki a sakatariyar karamar hukumar Dutse, inda ya ja hankalin shugaban karamar hukumar game da bukatar bada fifiko ga bangaren ayyukan raya kasa fiye da harkokin yau da kullum domin karfafa matakin cigaban karamar hukumar.

A cewar sa, kwamatin na rangadin kananan hukumomin jihar 27 ne domin bibiyar yadda ake aiwatar da tanade tanaden kasafin kudi domin tabbatar da kashe kudaden gwamnati ta hanyar da ta dace, Inda Kwamatin ke duba kundin bayanan sha’anin mulki da na harkokin Kudi da nufin cusa dabi’ar aiki da tanade tanaden aikin gwamnatin da ka’idojin kashe kudade.

Kazalika, Alhaji Aminu Zakari yace an kafa kananan kwamitoci guda 2 domin ziyarar gani da ido kan ayyukan raya kasa da karamar hukumar Dutse ta gudanar ga jama’ar yankin.

Karamin Kwamati na daya bisa jagorancin wakilin mazabar
Kanya Babba Alhaji Ibrahim Hashim Kanya, ya duba aikin ginin Masallacin khamsissalawati na garin Barangu da rumfunan kasuwa a garin ‘Yar Gaba da Masallacin khamsissalawati na Gidan Gawo da aikin ginin karamin asibitin garin Charka da aikin karamin asibitin Zangon Buji, da aikin gyaran Masallacin Juma’a na garuruwan Kacha da Barandau.

Shi kuwa karamin kwamati na 2 bisa jagorancin wakilin mazabar Buji, Alhaji Sale Baba Buji ya duba aikin hanyar Burji daga Bolari ta wuce Bakin Jeji zuwa Katangar lafiya, akan naira milyan 129 wadda wani kamfani ya yi, sai kuma rumfar kasuwa a garin Hammayayi da sanya fitilu masu amfani da hasken rana makaranta sikandire ta garin Madobi da Masallacin Juma’a na garin Baranda.

A jawabin sa na maraba, shugaban karamar hukumar Dutse Malam Sibu Abdullahi, ya bayyana ayyukan Kwamatin a matsayin ginshikin samun nasarar gudanar da mulkin kananan hukumomi.

Ya bayyana kudurin sa na karbar gyare-gyare da shawarwarin Kwamatin domin cigaban karamar hukumar sa.

Malam Sibu Abdullahi ya bayyana kudurinsa na hada Kai da majalisar Dokokin jihar Jigawa domin shiryawa kansiloli da Akawun majalisar kamsilolin bita game da tsare tsaren zaman majalisa kamar yadda mataimakin sakataren Kwamatin Malam Sadiq Muhammad ya kawo shawara.

 

Usman Mohammed Zaria

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Iran Ta Cilla Tauraron Dan’adam Mai Suna Nahid-2 A Yau
  • Gwamnan Jigawa Ya Rattaba Hannu Kan Kudirin Dokar Tabbatar Da Hisbah
  • Firaministan Sin Ya Jagoranci Taron Tattaunawa Tsakanin Shugabannin Sin Da EU Karo Na 25 Tare Da Shugaban Majalisar EU Da Shugabar Hukumar EU
  • Shugaban Sin Ya Aike Da Sakon Ta’aziyya Ga Takwaransa Na Rasha Sakamakon Hadarin Jirgin Saman Fasinja Da Ya Auku A Kasar
  • Majalisar Dokokin Jihar Jigawa Da Karamar Hukumar Dutse Za Su Shirya Taron Bita Ga Kansiloli
  • Ayatullahi Makarem Shirazi Ya Jinjinawa Al’ummar Iran Kan Hadin kai Da Suka Bayar Lokacin Yakin Kwanaki 12
  • Ministan Lafiya Na Kamaru: Hadin-Gwiwa Ta Fuskar Kiwon Lafiya Ta Shaida Zumunci Mai Karfi Tsakanin Kamaru Da Sin
  • Iran Tace Tawagar Kwararru Daga Hukumar IAEA Zata Ziyarci Kasar Nan Ba Da Dadewa Ba
  • NAFDAC ta gano dakin ajiye kayayyaki makare da sinadaran hada bam a Kano
  • Jami’an Kasashen Rasha, China, Iran Sun Gudanar Da Taron Hadin Gwiwa A Tehran